سوره: Suratul Balad

آيه : 1

لَآ أُقۡسِمُ بِهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ

Na rantse da wannan gari (na Makka)



سوره: Suratul Balad

آيه : 2

وَأَنتَ حِلُّۢ بِهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ

Alhali kuwa kai an halatta maka wannan gari[1]


1- Watau an halatta masa kashe wanda ya cancanci kisa a garin Makka. Ko kuma ana nufin Allah ya yi rantsuwa da Makka musamman lokacin da Annabi () yake zaune a cikinta.


سوره: Suratul Balad

آيه : 3

وَوَالِدٖ وَمَا وَلَدَ

(Na rantse) da mahaifi da abin da ya haifa[1]


1- Watau Annabi Adamu () da zurriyarsa. Ko kuma duk wani mahaifi da duk wani wanda aka haifa.


سوره: Suratul Balad

آيه : 4

لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِي كَبَدٍ

Haqiqa Mun halicci mutum cikin wahala



سوره: Suratul Balad

آيه : 5

أَيَحۡسَبُ أَن لَّن يَقۡدِرَ عَلَيۡهِ أَحَدٞ

Yanzu mutum yana tsammanin cewa wani ba zai sami iko a kansa ba?



سوره: Suratul Balad

آيه : 6

يَقُولُ أَهۡلَكۡتُ مَالٗا لُّبَدًا

Yana cewa: “Na vatar da dukiya mai ximbin yawa.”



سوره: Suratul Balad

آيه : 7

أَيَحۡسَبُ أَن لَّمۡ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ

Shin yana tsammanin cewa ba wanda ya gan shi?



سوره: Suratul Balad

آيه : 8

أَلَمۡ نَجۡعَل لَّهُۥ عَيۡنَيۡنِ

Shin ba Mu sanya masa idanuwa biyu ba ne?



سوره: Suratul Balad

آيه : 9

وَلِسَانٗا وَشَفَتَيۡنِ

Da harshe da kuma lavva biyu?



سوره: Suratul Balad

آيه : 10

وَهَدَيۡنَٰهُ ٱلنَّجۡدَيۡنِ

Muka kuma bayyana masa hanyoyi biyu[1]?


1- Watau hanyar alheri da hanyar sharri.


سوره: Suratul Balad

آيه : 11

فَلَا ٱقۡتَحَمَ ٱلۡعَقَبَةَ

Sai bai qetare hanya mai wahala[1] ba?


1- Watau hanyar da ta raba tsakaninsa da gidan Aljanna.


سوره: Suratul Balad

آيه : 12

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡعَقَبَةُ

Me kuma ya sanar da kai mece ce hanya mai wahala?



سوره: Suratul Balad

آيه : 13

فَكُّ رَقَبَةٍ

(Watau) ‘yanta wuyaye (bawa ko baiwa)



سوره: Suratul Balad

آيه : 14

أَوۡ إِطۡعَٰمٞ فِي يَوۡمٖ ذِي مَسۡغَبَةٖ

Ko kuma ciyarwa a wata rana ta yunwa



سوره: Suratul Balad

آيه : 15

يَتِيمٗا ذَا مَقۡرَبَةٍ

Ga maraya ma’abocin kusanci



سوره: Suratul Balad

آيه : 16

أَوۡ مِسۡكِينٗا ذَا مَتۡرَبَةٖ

Ko miskini ma’abocin talauci



سوره: Suratul Balad

آيه : 17

ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡمَرۡحَمَةِ

Sannan kuma ya zama daga waxanda suka yi imani, suka yi wa junansu wasiyya da yin haquri kuma suka yi wa juna wasiyya da tausayawa



سوره: Suratul Balad

آيه : 18

أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ

Waxannan su ne ma’abota dama[1]


1- Watau ‘yan Aljanna.


سوره: Suratul Balad

آيه : 19

وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِنَا هُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ

Waxanda kuwa suka kafirce wa ayoyinmu, su ne ma’abota hagu[1]


1- Watau ‘yan wuta.


سوره: Suratul Balad

آيه : 20

عَلَيۡهِمۡ نَارٞ مُّؤۡصَدَةُۢ

A kansu akwai wuta abar kullewa