Surah: Suratur Rahman

Ayah : 15

وَخَلَقَ ٱلۡجَآنَّ مِن مَّارِجٖ مِّن نَّارٖ

Ya kuma halicci aljani daga harshen wuta



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 16

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 17

رَبُّ ٱلۡمَشۡرِقَيۡنِ وَرَبُّ ٱلۡمَغۡرِبَيۡنِ

Ubangijin mahudar rana biyu da mafaxarta biyu[1]


1- Watau a lokacin sanyi da kuma lokacin zafi.


Surah: Suratur Rahman

Ayah : 18

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 19

مَرَجَ ٱلۡبَحۡرَيۡنِ يَلۡتَقِيَانِ

Ya gudanar da koguna guda biyu suna haxuwa (da juna)



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 20

بَيۡنَهُمَا بَرۡزَخٞ لَّا يَبۡغِيَانِ

A tsakaninsu (kuma) akwai wani shamaki da ya hana su shiga juna



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 21

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 22

يَخۡرُجُ مِنۡهُمَا ٱللُّؤۡلُؤُ وَٱلۡمَرۡجَانُ

Lu’ulu’u da murjani suna fita daga cikinsu



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 23

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 24

وَلَهُ ٱلۡجَوَارِ ٱلۡمُنشَـَٔاتُ فِي ٱلۡبَحۡرِ كَٱلۡأَعۡلَٰمِ

Jiragen ruwa kuma da aka yi su suna gudu a cikin kogi kamar manya-manyan duwatsu nasa ne



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 25

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 26

كُلُّ مَنۡ عَلَيۡهَا فَانٖ

Dukkan wanda yake kanta (qasar) qararre ne



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 27

وَيَبۡقَىٰ وَجۡهُ رَبِّكَ ذُو ٱلۡجَلَٰلِ وَٱلۡإِكۡرَامِ

Fuskar Ubangijinka kuwa Ma’abocin girma da karamci ne kawai take wanzuwa



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 28

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 29

يَسۡـَٔلُهُۥ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ كُلَّ يَوۡمٍ هُوَ فِي شَأۡنٖ

Duk wanda yake cikin sammai da qasa yana roqon Sa. Kowane lokacin Shi a cikin wani sha’ani yake



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 30

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 31

سَنَفۡرُغُ لَكُمۡ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ

Ba da daxewa ba za Mu dawo kanku ya ku mutane da aljannu



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 32

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 33

يَٰمَعۡشَرَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِ إِنِ ٱسۡتَطَعۡتُمۡ أَن تَنفُذُواْ مِنۡ أَقۡطَارِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ فَٱنفُذُواْۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلۡطَٰنٖ

Ya ku jama’ar aljannu da mutane, idan kun sami ikon ficewa daga cikin sassan sammai da qasa to ku fice. Ba za ku fice ba sai da samun wani qarfi[1]


1- Watau ba za su kuvuce wa Allah ba sai idan suna da wata hujja ko wani qarfi, wanda kuma su ma sun tabbata ba su da shi.


Surah: Suratur Rahman

Ayah : 34

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 35

يُرۡسَلُ عَلَيۡكُمَا شُوَاظٞ مِّن نَّارٖ وَنُحَاسٞ فَلَا تَنتَصِرَانِ

Za a aiko muku (ku mutane da aljannu) da balbalin wuta da kuma hayaqi, saboda haka ba za ku iya kare kanku (daga gare shi) ba



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 36

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 37

فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتۡ وَرۡدَةٗ كَٱلدِّهَانِ

Sannan idan sama ta kekkece ta zama jajir kamar jar fata[1]


1- Watau saboda an gusar da hasken taurarin cikinta gaba xaya.


Surah: Suratur Rahman

Ayah : 38

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 39

فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُسۡـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٞ وَلَا جَآنّٞ

Sannan a wannan rana ba a tambayar mutum ko aljan laifinsa



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 40

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 41

يُعۡرَفُ ٱلۡمُجۡرِمُونَ بِسِيمَٰهُمۡ فَيُؤۡخَذُ بِٱلنَّوَٰصِي وَٱلۡأَقۡدَامِ

Ana gane manyan masu laifi da alamominsu[1], sai a kama su ta makwarkwaxa da dugadugai


1- Saboda fuskokinsu za su yi baqi qirin, idanuwansu kuma za su yi jawur.


Surah: Suratur Rahman

Ayah : 42

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 43

هَٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِي يُكَذِّبُ بِهَا ٱلۡمُجۡرِمُونَ

(Za a ce da su): Wannan ita ce Jahannamar da manyan masu laifi suke qaryatawa



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 44

يَطُوفُونَ بَيۡنَهَا وَبَيۡنَ حَمِيمٍ ءَانٖ

Za su riqa kai-kawo tsakaninta da tafasasshen ruwa mai tsananin zafi