وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ
Haqiqa kuma Mun sauqaqe Alqur’ani don tunatarwa, to ko akwai mai wa’azantuwa?
Share :
وَلَقَدۡ جَآءَ ءَالَ فِرۡعَوۡنَ ٱلنُّذُرُ
Kuma haqiqa gargaxi ya zo wa mutanen Fir’auna
كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذۡنَٰهُمۡ أَخۡذَ عَزِيزٖ مُّقۡتَدِرٍ
Suka qaryata ayoyinmu dukkaninsu, sai Muka kama su irin kamu na Mabuwayi, Mai iko
أَكُفَّارُكُمۡ خَيۡرٞ مِّنۡ أُوْلَـٰٓئِكُمۡ أَمۡ لَكُم بَرَآءَةٞ فِي ٱلزُّبُرِ
Yanzu kafiranku (ku mutanen Makka) su ne suka fi waxancan alheri, ko kuwa kuna da wata hanya ta kuvuta ne a cikin littattafan da aka saukar?
أَمۡ يَقُولُونَ نَحۡنُ جَمِيعٞ مُّنتَصِرٞ
A’a, suna dai cewa ne: “Mu jama’a ce wadda za ta ci nasara.”
سَيُهۡزَمُ ٱلۡجَمۡعُ وَيُوَلُّونَ ٱلدُّبُرَ
To ba da daxewa ba za a karya jama’ar tasu[1], su kuma su ba da baya
1- Haka kuwa ya faru a yaqin Badar lokacin da aka karya lagon kafiran Makka, aka kashe manyansu da dama.
بَلِ ٱلسَّاعَةُ مَوۡعِدُهُمۡ وَٱلسَّاعَةُ أَدۡهَىٰ وَأَمَرُّ
A’a, alqiyama ita ce lokacin yi musu azaba, alqiyama kuwa ita ta fi bala’i, ta kuma fi xaci
إِنَّ ٱلۡمُجۡرِمِينَ فِي ضَلَٰلٖ وَسُعُرٖ
Lalle masu manyan laifuka suna cikin vata da azabar wuta
يَوۡمَ يُسۡحَبُونَ فِي ٱلنَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمۡ ذُوقُواْ مَسَّ سَقَرَ
Ranar da za a ja su cikin wuta a kan fuskokinsu (a ce da su): “Ku xanxani azabar wutar Saqara.”
إِنَّا كُلَّ شَيۡءٍ خَلَقۡنَٰهُ بِقَدَرٖ
Lalle Mu, kowane abu Mun halitta shi da qaddara
وَمَآ أَمۡرُنَآ إِلَّا وَٰحِدَةٞ كَلَمۡحِۭ بِٱلۡبَصَرِ
Kuma al’amarinmu bai zamanto ba face kalma xaya kamar qiftawar ido
وَلَقَدۡ أَهۡلَكۡنَآ أَشۡيَاعَكُمۡ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ
Haqiqa kuma Mun hallakar da ire-irenku[1], to ko akwai mai wa’azantuwa?
1- Watau kafirai irinsu masu taurin kai.
وَكُلُّ شَيۡءٖ فَعَلُوهُ فِي ٱلزُّبُرِ
Kuma kowane abu da suka aikata yana cikin littattafai
وَكُلُّ صَغِيرٖ وَكَبِيرٖ مُّسۡتَطَرٌ
Kowane qaramin abu da babba kuma suna nan a rubuce
إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَنَهَرٖ
Lalle masu taqawa suna cikin gidajen Aljanna da qoramu
فِي مَقۡعَدِ صِدۡقٍ عِندَ مَلِيكٖ مُّقۡتَدِرِۭ
A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko
ٱلرَّحۡمَٰنُ
(Allah) Mai rahama
عَلَّمَ ٱلۡقُرۡءَانَ
Shi Ya koyar da Alqur’ani
خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ
Ya halicci mutum
عَلَّمَهُ ٱلۡبَيَانَ
Ya koyar da shi bayani
ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ بِحُسۡبَانٖ
Rana da wata (suna tafiya) a tsare
وَٱلنَّجۡمُ وَٱلشَّجَرُ يَسۡجُدَانِ
Tsirrai da bishiyoyi suna yin sujjada[1]
1- Watau tsirrai waxanda ba sa tashi tsaye da bishiyoyi masu tsayawa a kan sandunansu.
وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلۡمِيزَانَ
Sama kuma Ya xaga ta, Ya kuma kafa adalci
أَلَّا تَطۡغَوۡاْ فِي ٱلۡمِيزَانِ
Don kada ku yi zalunci a abin awo
وَأَقِيمُواْ ٱلۡوَزۡنَ بِٱلۡقِسۡطِ وَلَا تُخۡسِرُواْ ٱلۡمِيزَانَ
Kuma ku tabbatar da awo da adalci kada kuma ku tauye abin awo
وَٱلۡأَرۡضَ وَضَعَهَا لِلۡأَنَامِ
Qasa kuma Ya yi ta saboda talikai
فِيهَا فَٰكِهَةٞ وَٱلنَّخۡلُ ذَاتُ ٱلۡأَكۡمَامِ
A cikinta akwai abin marmari da dabinai ma’abota kwasfa
وَٱلۡحَبُّ ذُو ٱلۡعَصۡفِ وَٱلرَّيۡحَانُ
Da qwayoyi ma’abota qaiqayi da kuma ganyaye masu qanshi
فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ
To da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?
خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِن صَلۡصَٰلٖ كَٱلۡفَخَّارِ
Ya halicci mutum daga busasshen tavo kamar kasko