فَكُبۡكِبُواْ فِيهَا هُمۡ وَٱلۡغَاوُۥنَ
Sai aka kikkifa su cikinta (wutar) su da vatattu
Share :
وَجُنُودُ إِبۡلِيسَ أَجۡمَعُونَ
Da kuma rundunar Iblis gaba xaya
قَالُواْ وَهُمۡ فِيهَا يَخۡتَصِمُونَ
Sai suka ce, alhali suna jayayya da juna a cikinta:
تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٍ
“Mun rantse da Allah tabbas mun kasance (a duniya) cikin vata bayyananne
إِذۡ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
“Lokacin da muke daidaita ku da Ubangijin talikai[1]
1- Watau wajen soyayya da bauta.
وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلۡمُجۡرِمُونَ
“Ba kuwa waxanda suka vatar da mu sai manyan masu laifuka
فَمَا لَنَا مِن شَٰفِعِينَ
“To a (yau) ba mu da wasu masu ceto
وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٖ
“Ba kuma wani aboki na qut-da-qut
فَلَوۡ أَنَّ لَنَا كَرَّةٗ فَنَكُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
“To ina ma da za mu samu damar komawa, sai mu zamanto daga muminai!”
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu, ba su zamanto muminai ba
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi Mai jin qai
كَذَّبَتۡ قَوۡمُ نُوحٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Mutanen Nuhu sun qaryata mazanni[1]
1- Domin qaryata Annabi Nuhu () daidai yake da qaryata dukkan manzannin Allah, domin saqo iri xaya suke xauke da shi.
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Lokacin da xan’uwansu Nuhu ya ce da su: “Yanzu ba za ku kiyaye dokokin Allah ba?
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
“Lalle ni Manzo ne amintacce a gare ku
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
“Ba na kuma tambayar ku wani lada a game da shi (isar da manzancin). Ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai
“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni.”
۞قَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلۡأَرۡذَلُونَ
Suka ce: “Yanzu ma yi imani da kai alhali qasqantattu ne mabiyanka?”
قَالَ وَمَا عِلۡمِي بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ
Ya ce: “Ba ni da sani game da abin da suka zamanto suna aikatawa
إِنۡ حِسَابُهُمۡ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّيۖ لَوۡ تَشۡعُرُونَ
“Hisabinsu kawai yana wajen Ubangijina ne; da za ku gane
وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
“Ni kuma ba mai korar muminai ba ne
إِنۡ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٞ مُّبِينٞ
“Ni kawai mai gargaxi ne mai bayyanawa.”
قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمَرۡجُومِينَ
Suka ce: “Ya Nuhu, mun rantse idan ba ka daina (faxar abin da kake faxa) ba, tabbas za ka zamanto daga cikin jefaffu!”
قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوۡمِي كَذَّبُونِ
Ya ce: “Ya Ubangijina, lalle mutanena sun qaryata ni
فَٱفۡتَحۡ بَيۡنِي وَبَيۡنَهُمۡ فَتۡحٗا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِيَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
“Ka yi hukunci tsakanina da su, kuma Ka tserar da ni tare da muminan da suke tare da ni.”
فَأَنجَيۡنَٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِي ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ
Sai Muka tserar da shi da waxanda suke tare da shi a cikin jirgin ruwan da ke maqare (da mutane da dabbobi)
ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا بَعۡدُ ٱلۡبَاقِينَ
Sannan bayan haka Muka nutsar da sauran
Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba
Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai
كَذَّبَتۡ عَادٌ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Adawa (ma) sun qaryata manzanni[1]
1- Domin qaryata Annabi Hudu () daidai yake da qaryata duk manzannin Allah, saboda saqo iri xaya suke xauke da shi.