Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 13

تِلۡكَ حُدُودُ ٱللَّهِۚ وَمَن يُطِعِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ يُدۡخِلۡهُ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ وَذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

Waxannan iyakoki ne na Allah. Wanda duk yake bin Allah da Manzonsa, to zai shigar da shi gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, suna masu dawwama a cikinsu. Kuma wannan shi ne rabo mai girma



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 14

وَمَن يَعۡصِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ وَيَتَعَدَّ حُدُودَهُۥ يُدۡخِلۡهُ نَارًا خَٰلِدٗا فِيهَا وَلَهُۥ عَذَابٞ مُّهِينٞ

Wanda kuma yake sava wa Allah da Manzonsa, yake kuma qetare iyakokinsa, to zai shigar da shi wuta, yana mai dawwama a cikinta, kuma yana da wata azaba mai wulaqantarwa



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 15

وَٱلَّـٰتِي يَأۡتِينَ ٱلۡفَٰحِشَةَ مِن نِّسَآئِكُمۡ فَٱسۡتَشۡهِدُواْ عَلَيۡهِنَّ أَرۡبَعَةٗ مِّنكُمۡۖ فَإِن شَهِدُواْ فَأَمۡسِكُوهُنَّ فِي ٱلۡبُيُوتِ حَتَّىٰ يَتَوَفَّىٰهُنَّ ٱلۡمَوۡتُ أَوۡ يَجۡعَلَ ٱللَّهُ لَهُنَّ سَبِيلٗا

Kuma waxannan da suke aikata zina daga cikin matanku, to ku kafa musu shaidu guda huxu daga cikinku, sannan idan sun bayar da shaida, to sai ku tsare su a cikin gidaje har sai mutuwa ta xauke su ko kuma Allah Ya sanya musu wata mafita[1]


1- Wannan hukuncin ya kasance ne gabanin a saukar da hukuncin bulala xari ga mazinatan da ba su tava yin aure ba ko jefewa ga waxanda suka tava yin aure.


Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 16

وَٱلَّذَانِ يَأۡتِيَٰنِهَا مِنكُمۡ فَـَٔاذُوهُمَاۖ فَإِن تَابَا وَأَصۡلَحَا فَأَعۡرِضُواْ عَنۡهُمَآۗ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ تَوَّابٗا رَّحِيمًا

Kuma maza biyu daga cikinku da za su yi zina, to ku muzguna musu; amma idan sun tuba kuma suka gyara ayyukansu, to ku kawar da kai daga gare su. Lalle Allah Ya kasance Mai yawan karvar tuba ne, Mai jin qai



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 17

إِنَّمَا ٱلتَّوۡبَةُ عَلَى ٱللَّهِ لِلَّذِينَ يَعۡمَلُونَ ٱلسُّوٓءَ بِجَهَٰلَةٖ ثُمَّ يَتُوبُونَ مِن قَرِيبٖ فَأُوْلَـٰٓئِكَ يَتُوبُ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمۡۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Tuban da Allah Yake karva kawai (ita ce) na waxanda suke aikata mummunan aiki da jahilci, sannan su gaggauta tuba, to waxannan Allah zai karvi tubansu. Allah kuma Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai hikima



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 18

وَلَيۡسَتِ ٱلتَّوۡبَةُ لِلَّذِينَ يَعۡمَلُونَ ٱلسَّيِّـَٔاتِ حَتَّىٰٓ إِذَا حَضَرَ أَحَدَهُمُ ٱلۡمَوۡتُ قَالَ إِنِّي تُبۡتُ ٱلۡـَٰٔنَ وَلَا ٱلَّذِينَ يَمُوتُونَ وَهُمۡ كُفَّارٌۚ أُوْلَـٰٓئِكَ أَعۡتَدۡنَا لَهُمۡ عَذَابًا أَلِيمٗا

Kuma ba a karvar tuba daga waxanda suke aikata munanan ayyuka har sai lokacin da mutuwa ta zo wa xayansu, sai ya ce: “Ni kam na tuba yanzu;” kuma ba a karvar tuban waxanda suke mutuwa alhalin suna kafirai. Waxannan Mun yi musu tanadin azaba mai raxaxi



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 19

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا يَحِلُّ لَكُمۡ أَن تَرِثُواْ ٱلنِّسَآءَ كَرۡهٗاۖ وَلَا تَعۡضُلُوهُنَّ لِتَذۡهَبُواْ بِبَعۡضِ مَآ ءَاتَيۡتُمُوهُنَّ إِلَّآ أَن يَأۡتِينَ بِفَٰحِشَةٖ مُّبَيِّنَةٖۚ وَعَاشِرُوهُنَّ بِٱلۡمَعۡرُوفِۚ فَإِن كَرِهۡتُمُوهُنَّ فَعَسَىٰٓ أَن تَكۡرَهُواْ شَيۡـٔٗا وَيَجۡعَلَ ٱللَّهُ فِيهِ خَيۡرٗا كَثِيرٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, bai halatta gare ku ku gaji mata a bisa ga tilas ba; kuma kada ku hana su aure don ku qwace wani sashi na abin da kuka ba su, sai fa in sun zo da wata alfasha ta sarari. Kuma ku yi musu kyakkyawar mu’amala. Amma idan har kun qi su, to mai yiwuwa ne ku qi wani abu, Allah kuma Ya sanya alheri mai yawa a cikinsa



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 20

وَإِنۡ أَرَدتُّمُ ٱسۡتِبۡدَالَ زَوۡجٖ مَّكَانَ زَوۡجٖ وَءَاتَيۡتُمۡ إِحۡدَىٰهُنَّ قِنطَارٗا فَلَا تَأۡخُذُواْ مِنۡهُ شَيۡـًٔاۚ أَتَأۡخُذُونَهُۥ بُهۡتَٰنٗا وَإِثۡمٗا مُّبِينٗا

Kuma idan kun yi nufin musanya wata mace a gurbin wata macen, kuma kun riga kun ba wa xayarsu dukiya mai yawa (ta sadaki), to kar ku karvi komai daga cikinsa. Shin za ku karve shi ne a kan zalunci da laifi qarara?



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 21

وَكَيۡفَ تَأۡخُذُونَهُۥ وَقَدۡ أَفۡضَىٰ بَعۡضُكُمۡ إِلَىٰ بَعۡضٖ وَأَخَذۡنَ مِنكُم مِّيثَٰقًا غَلِيظٗا

Kuma ta yaya za ku karve shi alhali kuma kun riga kun sadu da juna, kuma sun riqi wani alqawari mai qarfi daga wajenku?



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 22

وَلَا تَنكِحُواْ مَا نَكَحَ ءَابَآؤُكُم مِّنَ ٱلنِّسَآءِ إِلَّا مَا قَدۡ سَلَفَۚ إِنَّهُۥ كَانَ فَٰحِشَةٗ وَمَقۡتٗا وَسَآءَ سَبِيلًا

Kuma kada ku auri wadda iyayenku maza suka aure ta cikin mata, sai fa abin da ya riga ya shuxe. Lalle yin hakan ya kasance alfasha ce kuma abu ne da zai jawo fushin Allah, kuma tafarki ne wanda ya yi muni



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 23

حُرِّمَتۡ عَلَيۡكُمۡ أُمَّهَٰتُكُمۡ وَبَنَاتُكُمۡ وَأَخَوَٰتُكُمۡ وَعَمَّـٰتُكُمۡ وَخَٰلَٰتُكُمۡ وَبَنَاتُ ٱلۡأَخِ وَبَنَاتُ ٱلۡأُخۡتِ وَأُمَّهَٰتُكُمُ ٱلَّـٰتِيٓ أَرۡضَعۡنَكُمۡ وَأَخَوَٰتُكُم مِّنَ ٱلرَّضَٰعَةِ وَأُمَّهَٰتُ نِسَآئِكُمۡ وَرَبَـٰٓئِبُكُمُ ٱلَّـٰتِي فِي حُجُورِكُم مِّن نِّسَآئِكُمُ ٱلَّـٰتِي دَخَلۡتُم بِهِنَّ فَإِن لَّمۡ تَكُونُواْ دَخَلۡتُم بِهِنَّ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ وَحَلَـٰٓئِلُ أَبۡنَآئِكُمُ ٱلَّذِينَ مِنۡ أَصۡلَٰبِكُمۡ وَأَن تَجۡمَعُواْ بَيۡنَ ٱلۡأُخۡتَيۡنِ إِلَّا مَا قَدۡ سَلَفَۗ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

An haramta muku auren iyayenku mata da ‘ya’yanku mata da ‘yan’uwanku mata da gwaggonninku da yagwalgwalanku da ‘ya’yan xan’uwa da ‘ya’yan ‘yar’uwa da iyayenku waxanda suka shayar da ku da ‘yan’uwanku mata ta wajen shayarwa, da iyayen matanku[1] da agololinku waxanda suke cikin gidajenku, waxanda matan da kuka tava saduwa da su suka haife su, in kuwa ba ku tava saduwa da su ba, to babu laifi a kanku, da matan ‘ya’yanku maza waxanda suke na tsatsonku; haramun ne kuma ku haxa ‘yan’uwa mata biyu, sai dai abin da ya wuce a baya[2]. Lalle Allah Ya kasance Mai yawan gafara ne, Mai jin qai


1- Daga zarar an xaura auren mutum da mace, to uwarta ta haramta gare shi, ko ba su tare ba.


2- Haramun ne mutum ya auri ya da qanwa lokaci xaya. Hakanan haramun ne ya haxa mace da gwaggonta ko innarta lokaci xaya.