يَوۡمَ نَحۡشُرُ ٱلۡمُتَّقِينَ إِلَى ٱلرَّحۡمَٰنِ وَفۡدٗا
Ranar da za Mu tayar da masu taqawa zuwa ga (Allah) Mai rahama a matsayin manyan baqi
وَنَسُوقُ ٱلۡمُجۡرِمِينَ إِلَىٰ جَهَنَّمَ وِرۡدٗا
Mu kuma kora kafirai zuwa Jahannama cikin tsananin qishirwa
لَّا يَمۡلِكُونَ ٱلشَّفَٰعَةَ إِلَّا مَنِ ٱتَّخَذَ عِندَ ٱلرَّحۡمَٰنِ عَهۡدٗا
Ba wani mai ikon yin ceto sai wanda yake da alqawari a wurin (Allah) Mai rahama[1]
1- Watau ya riqe alqawarin da ya yi na imani da Allah da manzanninsa.
وَقَالُواْ ٱتَّخَذَ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَلَدٗا
Suka kuma ce: “(Allah) Mai rahama (wai) yana da xa
لَّقَدۡ جِئۡتُمۡ شَيۡـًٔا إِدّٗا
Haqiqa kun zo da babban abu (marar daxin ji)
تَكَادُ ٱلسَّمَٰوَٰتُ يَتَفَطَّرۡنَ مِنۡهُ وَتَنشَقُّ ٱلۡأَرۡضُ وَتَخِرُّ ٱلۡجِبَالُ هَدًّا
Sama ta kusa ta kece saboda shi (mummunan furucin), qasa kuma ta tsage, duwatsu kuma su zube su yi rugu-rugu
أَن دَعَوۡاْ لِلرَّحۡمَٰنِ وَلَدٗا
Saboda sun yi da’awar Allah Yana da xa!
وَمَا يَنۢبَغِي لِلرَّحۡمَٰنِ أَن يَتَّخِذَ وَلَدًا
Bai kuwa dace da (Allah) Mai rahama Ya zama Yana da xa ba
إِن كُلُّ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ إِلَّآ ءَاتِي ٱلرَّحۡمَٰنِ عَبۡدٗا
Ba wani abu da yake cikin sammai da qasa face ya zo wa (Allah) Mai rahama a matsayin bawa
لَّقَدۡ أَحۡصَىٰهُمۡ وَعَدَّهُمۡ عَدّٗا
Lalle Ya kiyaye da su Ya kuma qididdige su sosai
وَكُلُّهُمۡ ءَاتِيهِ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فَرۡدًا
Kuma dukkansu kowa zai zo masa a ranar alqiyama shi kaxai
إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ سَيَجۡعَلُ لَهُمُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وُدّٗا
Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki na gari, to (Allah) Mai rahama zai sanya musu qauna[1]
1- Watau zanya farin jininsu a zukatan masoyansa a sama da qasa. Shi ma kuma zai qaunace su.
فَإِنَّمَا يَسَّرۡنَٰهُ بِلِسَانِكَ لِتُبَشِّرَ بِهِ ٱلۡمُتَّقِينَ وَتُنذِرَ بِهِۦ قَوۡمٗا لُّدّٗا
To Mun dai sauqaqe shi (Alqur’ani) da harshenka ne don kawai ka yi wa masu taqawa albishir da shi, ka kuma gargaxi mutane masu tsananin jayayya da shi
وَكَمۡ أَهۡلَكۡنَا قَبۡلَهُم مِّن قَرۡنٍ هَلۡ تُحِسُّ مِنۡهُم مِّنۡ أَحَدٍ أَوۡ تَسۡمَعُ لَهُمۡ رِكۡزَۢا
Al’umma nawa Muka hallaka a gabaninsu, shin kana jin xuriyar wani daga cikinsu, ko kuwa kana jin ‘yar muryarsu?
طه
Xa Ha[1]
1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.
مَآ أَنزَلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡقُرۡءَانَ لِتَشۡقَىٰٓ
Ba Mu saukar maka da Alqur’ani don ka wahala ba
إِلَّا تَذۡكِرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰ
Sai don wa’azi ga wanda zai ji tsoron (haxuwa da Allah)
تَنزِيلٗا مِّمَّنۡ خَلَقَ ٱلۡأَرۡضَ وَٱلسَّمَٰوَٰتِ ٱلۡعُلَى
Saukakke ne daga wanda Ya halicci qasa da sammai masu xaukaka
ٱلرَّحۡمَٰنُ عَلَى ٱلۡعَرۡشِ ٱسۡتَوَىٰ
(Allah) Mai rahama, Ya daidaita a kan Al’arshi[1]
1- Duba Suratul A’arafi, aya ta 54, hashiya ta 126.
لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا وَمَا تَحۡتَ ٱلثَّرَىٰ
Abin da yake sammai da qasa, da abin da yake tsakaninsu da kuma abin da yake qarqashin qasa, (duka) nasa ne
وَإِن تَجۡهَرۡ بِٱلۡقَوۡلِ فَإِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلسِّرَّ وَأَخۡفَى
Idan kuma ka xaga murya da furuci to lalle Shi Yana sane da sirri da abin da ya fi (sirri) vuya
ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ لَهُ ٱلۡأَسۡمَآءُ ٱلۡحُسۡنَىٰ
Allah (Shi ne wanda) babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi; Yana da sunaye mafiya kyau
وَهَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ
Shin kuwa labarin Musa ya zo maka?
إِذۡ رَءَا نَارٗا فَقَالَ لِأَهۡلِهِ ٱمۡكُثُوٓاْ إِنِّيٓ ءَانَسۡتُ نَارٗا لَّعَلِّيٓ ءَاتِيكُم مِّنۡهَا بِقَبَسٍ أَوۡ أَجِدُ عَلَى ٱلنَّارِ هُدٗى
Lokacin da ya gano wuta sai ya ce da iyalinsa: “Ku zauna (a nan), lalle ni fa na hangi wuta, (zan je) ko na zo muku da garwashinta ko kuma in sami mai nuna mini (hanya) a wurin wutar.”
فَلَمَّآ أَتَىٰهَا نُودِيَ يَٰمُوسَىٰٓ
To lokacin da ya zo wurinta (wato wutar), sai aka kira shi (cewa): “Ya Musa
إِنِّيٓ أَنَا۠ رَبُّكَ فَٱخۡلَعۡ نَعۡلَيۡكَ إِنَّكَ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوٗى
“Lalle Ni, Ni ne fa Ubangijinka, sai ka tuve takalmanka; lalle kana a tsarkakakken kwarin Xuwa ne
وَأَنَا ٱخۡتَرۡتُكَ فَٱسۡتَمِعۡ لِمَا يُوحَىٰٓ
“Kuma Ni Na zave ka (da manzanci), sai ka ji abin da za a yiwo ma wahayi (da shi)
إِنَّنِيٓ أَنَا ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّآ أَنَا۠ فَٱعۡبُدۡنِي وَأَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَ لِذِكۡرِيٓ
“Lalle Ni, Ni ne Allah, babu wani abin bauta sai Ni, to ka bauta mini, kuma ka tsai da salla don tuna Ni
إِنَّ ٱلسَّاعَةَ ءَاتِيَةٌ أَكَادُ أُخۡفِيهَا لِتُجۡزَىٰ كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا تَسۡعَىٰ
“Lalle alqiyama za ta zo, ina nufin voye ta ne don a saka wa kowanne rai da irin abin da yake aikatawa
فَلَا يَصُدَّنَّكَ عَنۡهَا مَن لَّا يُؤۡمِنُ بِهَا وَٱتَّبَعَ هَوَىٰهُ فَتَرۡدَىٰ
“To kada wanda bai yi imani da ita ba ya kuma bi son ransa ya hana ka gaskata ta, sai ka hallaka