ٱلَّذِينَ قَالُوٓاْ إِنَّ ٱللَّهَ عَهِدَ إِلَيۡنَآ أَلَّا نُؤۡمِنَ لِرَسُولٍ حَتَّىٰ يَأۡتِيَنَا بِقُرۡبَانٖ تَأۡكُلُهُ ٱلنَّارُۗ قُلۡ قَدۡ جَآءَكُمۡ رُسُلٞ مِّن قَبۡلِي بِٱلۡبَيِّنَٰتِ وَبِٱلَّذِي قُلۡتُمۡ فَلِمَ قَتَلۡتُمُوهُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ
Su ne waxanda suka ce: “Lalle Allah Ya yi alqawari da mu kar mu yi imani da kowane manzo har sai ya zo mana da wata sadaka wadda wuta za ta cinye ta.” Ka ce: “Haqiqa manzanni sun zo muku tun kafin ni, da hujjoji da kuma abin da kuka ce xin, to don me kuka kashe su in kun kasance masu gaskiya?”
فَإِن كَذَّبُوكَ فَقَدۡ كُذِّبَ رُسُلٞ مِّن قَبۡلِكَ جَآءُو بِٱلۡبَيِّنَٰتِ وَٱلزُّبُرِ وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُنِيرِ
To idan sun qaryata ka, to haqiqa an qaryata manzanni kafinka, waxanda suka zo da hujjoji da littattafai da Littafi mai haskakawa
كُلُّ نَفۡسٖ ذَآئِقَةُ ٱلۡمَوۡتِۗ وَإِنَّمَا تُوَفَّوۡنَ أُجُورَكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۖ فَمَن زُحۡزِحَ عَنِ ٱلنَّارِ وَأُدۡخِلَ ٱلۡجَنَّةَ فَقَدۡ فَازَۗ وَمَا ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَآ إِلَّا مَتَٰعُ ٱلۡغُرُورِ
Kowane rai zai xanxani mutuwa. Kuma a ranar alqiyama ne za a cika muku ladan ayyukanku; to duk wanda aka nisanta shi daga wuta, kuma aka shigar da shi Aljanna, to haqiqa ya rabauta. Kuma rayuwar duniya ba komai ba ce face jin daxi mai ruxarwa
۞لَتُبۡلَوُنَّ فِيٓ أَمۡوَٰلِكُمۡ وَأَنفُسِكُمۡ وَلَتَسۡمَعُنَّ مِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ مِن قَبۡلِكُمۡ وَمِنَ ٱلَّذِينَ أَشۡرَكُوٓاْ أَذٗى كَثِيرٗاۚ وَإِن تَصۡبِرُواْ وَتَتَّقُواْ فَإِنَّ ذَٰلِكَ مِنۡ عَزۡمِ ٱلۡأُمُورِ
Lalle za a jarrabe ku a cikin dukiyoyinku da rayukanku, kuma lalle za ku riqa jin cutarwa mai yawa daga waxanda aka bai wa Littafi kafinku, haka kuma daga waxanda suke mushirikai. Amma idan har kuka yi haquri, kuma kuka tsare dokar Allah, to lalle wannan yana daga cikin manyan al’amura
وَإِذۡ أَخَذَ ٱللَّهُ مِيثَٰقَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ لَتُبَيِّنُنَّهُۥ لِلنَّاسِ وَلَا تَكۡتُمُونَهُۥ فَنَبَذُوهُ وَرَآءَ ظُهُورِهِمۡ وَٱشۡتَرَوۡاْ بِهِۦ ثَمَنٗا قَلِيلٗاۖ فَبِئۡسَ مَا يَشۡتَرُونَ
Kuma ka tuna lokacin da Allah Ya xauki alqawari daga waxanda aka bai wa Littafi cewa: “Lalle ku bayyana shi ga mutane, kuma kada ku voye shi.” Sai suka jefar da shi can bayansu, kuma suka musanya shi da wani xan farashi qanqani. To tir da abin da suke yin musanye da shi
لَا تَحۡسَبَنَّ ٱلَّذِينَ يَفۡرَحُونَ بِمَآ أَتَواْ وَّيُحِبُّونَ أَن يُحۡمَدُواْ بِمَا لَمۡ يَفۡعَلُواْ فَلَا تَحۡسَبَنَّهُم بِمَفَازَةٖ مِّنَ ٱلۡعَذَابِۖ وَلَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ
Kada ka yi tsammanin waxanda suke yin farin ciki da irin abin da suka aikata, kuma suna son a riqa yabon su da abin da ba su aikata ba, to kada ka yi tsammanin za su tsira daga azaba, kuma suna da azaba mai raxaxi
وَلِلَّهِ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۗ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ
Kuma ga Allah ne mulkin sammai da qasa yake. Kuma Allah Mai iko ne a kan komai
إِنَّ فِي خَلۡقِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَٱخۡتِلَٰفِ ٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِ لَأٓيَٰتٖ لِّأُوْلِي ٱلۡأَلۡبَٰبِ
Lalle a cikin halittar sammai da qasa da sassavawar dare da rana, tabbas akwai ayoyi ga ma’abota hankula
ٱلَّذِينَ يَذۡكُرُونَ ٱللَّهَ قِيَٰمٗا وَقُعُودٗا وَعَلَىٰ جُنُوبِهِمۡ وَيَتَفَكَّرُونَ فِي خَلۡقِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ رَبَّنَا مَا خَلَقۡتَ هَٰذَا بَٰطِلٗا سُبۡحَٰنَكَ فَقِنَا عَذَابَ ٱلنَّارِ
Waxanda suke ambaton Allah a tsaye da kuma zaune da kuma kishingixe, suna kuma tunani a kan halittar sammai da qasa, (suna cewa): “Ya Ubangijinmu, ba Ka halicci wannan a banza ba, tsarki ya tabbata gare Ka, Ka tserar da mu daga azabar wuta
رَبَّنَآ إِنَّكَ مَن تُدۡخِلِ ٱلنَّارَ فَقَدۡ أَخۡزَيۡتَهُۥۖ وَمَا لِلظَّـٰلِمِينَ مِنۡ أَنصَارٖ
“Ya Ubangijinmu, lalle duk wanda Ka shigar da shi wuta, to haqiqa Ka kunyata shi; kuma azzalumai ba su da mai taimakon su
رَّبَّنَآ إِنَّنَا سَمِعۡنَا مُنَادِيٗا يُنَادِي لِلۡإِيمَٰنِ أَنۡ ءَامِنُواْ بِرَبِّكُمۡ فَـَٔامَنَّاۚ رَبَّنَا فَٱغۡفِرۡ لَنَا ذُنُوبَنَا وَكَفِّرۡ عَنَّا سَيِّـَٔاتِنَا وَتَوَفَّنَا مَعَ ٱلۡأَبۡرَارِ
“Ya Ubangijinmu, lalle mu mun ji wani mai kira yana yin kira zuwa imani cewa: “Ku yi imani da Ubangijinku;” sai muka yi imani. Ya Ubangijinmu, Ka gafarta mana zunubanmu, kuma Ka kankare mana kurakuranmu, kuma Ka karvi rayukanmu tare da mutane masu xa’a
رَبَّنَا وَءَاتِنَا مَا وَعَدتَّنَا عَلَىٰ رُسُلِكَ وَلَا تُخۡزِنَا يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۖ إِنَّكَ لَا تُخۡلِفُ ٱلۡمِيعَادَ
“Ya Ubangijinmu, kuma Ka ba mu abin da Ka yi mana alqawari da shi ta harshen manzanninka, kuma kada Ka kunyatar da mu ranar alqiyama. Lalle Kai ba Ka sava alqawari.”
فَٱسۡتَجَابَ لَهُمۡ رَبُّهُمۡ أَنِّي لَآ أُضِيعُ عَمَلَ عَٰمِلٖ مِّنكُم مِّن ذَكَرٍ أَوۡ أُنثَىٰۖ بَعۡضُكُم مِّنۢ بَعۡضٖۖ فَٱلَّذِينَ هَاجَرُواْ وَأُخۡرِجُواْ مِن دِيَٰرِهِمۡ وَأُوذُواْ فِي سَبِيلِي وَقَٰتَلُواْ وَقُتِلُواْ لَأُكَفِّرَنَّ عَنۡهُمۡ سَيِّـَٔاتِهِمۡ وَلَأُدۡخِلَنَّهُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ ثَوَابٗا مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِۚ وَٱللَّهُ عِندَهُۥ حُسۡنُ ٱلثَّوَابِ
Sai Ubangijinsu Ya amsa musu (cewa): “Lalle Ni ba zan tozarta aikin wani mai aiki daga cikinku ba, namiji ne ko mace; sashinku yana tare da sashe. To waxanda suka yi hijira kuma aka fitar da su daga gidajensu kuma aka cutar da su wajen bin tafarkina kuma suka yi yaqi kuma aka kashe su, lalle zan kankare musu kurakuransu, kuma lalle zan shigar da su gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. (Wannan) lada ne daga wajen Allah, kuma a wurin Allah ne mafi kyawun lada yake.”
لَا يَغُرَّنَّكَ تَقَلُّبُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ
Kada zirga-zirgar kafirai a cikin garuruwa ta ruxe ka
مَتَٰعٞ قَلِيلٞ ثُمَّ مَأۡوَىٰهُمۡ جَهَنَّمُۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمِهَادُ
Wani xan jin daxi ne qanqani, sannan makomarsu Jahannama. Kuma tir da wannan shimfixar
لَٰكِنِ ٱلَّذِينَ ٱتَّقَوۡاْ رَبَّهُمۡ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَا نُزُلٗا مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِۗ وَمَا عِندَ ٱللَّهِ خَيۡرٞ لِّلۡأَبۡرَارِ
Amma waxanda suka bi dokokin Ubangijinsu suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, za su dawwama a cikinsu, wannan liyafa ce ta musamman daga wajen Allah. Kuma abin da yake wajen Allah shi ne mafi alheri ga masu biyayya
وَإِنَّ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ لَمَن يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَمَآ أُنزِلَ إِلَيۡكُمۡ وَمَآ أُنزِلَ إِلَيۡهِمۡ خَٰشِعِينَ لِلَّهِ لَا يَشۡتَرُونَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ ثَمَنٗا قَلِيلًاۚ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡۗ إِنَّ ٱللَّهَ سَرِيعُ ٱلۡحِسَابِ
Kuma lalle a cikin Ma’abota Littafi, tabbas akwai waxanda suke yin imani da Allah da kuma abin da aka saukar muku da kuma abin da aka saukar musu, suna masu qasqantar da kai ga Allah, ba sa musanya ayoyin Allah da wani xan farashi qanqani. Waxannan suna da lada a wajen Ubangijinsu. Lalle Allah Mai gaggawar hisabi ne
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱصۡبِرُواْ وَصَابِرُواْ وَرَابِطُواْ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ
Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi haquri, kuma ku jure matuqa ga yin haquri, kuma ku tsare iyakokin qasa, kuma ku kiyaye dokokin Allah don ku sami rabauta
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱتَّقُواْ رَبَّكُمُ ٱلَّذِي خَلَقَكُم مِّن نَّفۡسٖ وَٰحِدَةٖ وَخَلَقَ مِنۡهَا زَوۡجَهَا وَبَثَّ مِنۡهُمَا رِجَالٗا كَثِيرٗا وَنِسَآءٗۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ ٱلَّذِي تَسَآءَلُونَ بِهِۦ وَٱلۡأَرۡحَامَۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلَيۡكُمۡ رَقِيبٗا
Ya ku mutane, ku kiyaye dokokin Ubangijinku Wanda Ya halicce ku daga rai guda xaya, kuma Ya halicci matarsa daga shi, kuma Ya yaxa maza da mata masu yawa daga gare su. Kuma ku kiyaye dokokin Allah Wanda kuke yi wa juna magiya da Shi, kuma ku kiyaye (yanke) zumunci. Lalle Allah Mai kula da ku ne
وَءَاتُواْ ٱلۡيَتَٰمَىٰٓ أَمۡوَٰلَهُمۡۖ وَلَا تَتَبَدَّلُواْ ٱلۡخَبِيثَ بِٱلطَّيِّبِۖ وَلَا تَأۡكُلُوٓاْ أَمۡوَٰلَهُمۡ إِلَىٰٓ أَمۡوَٰلِكُمۡۚ إِنَّهُۥ كَانَ حُوبٗا كَبِيرٗا
Kuma ku bai wa marayu dukiyoyinsu; kuma kada ku musanya kyakkyawa da mummuna; kuma kada ku ci dukiyoyinsu haxe da dukiyoyinku. Lalle yin hakan ya tabbata zunubi ne mai girma
وَإِنۡ خِفۡتُمۡ أَلَّا تُقۡسِطُواْ فِي ٱلۡيَتَٰمَىٰ فَٱنكِحُواْ مَا طَابَ لَكُم مِّنَ ٱلنِّسَآءِ مَثۡنَىٰ وَثُلَٰثَ وَرُبَٰعَۖ فَإِنۡ خِفۡتُمۡ أَلَّا تَعۡدِلُواْ فَوَٰحِدَةً أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُكُمۡۚ ذَٰلِكَ أَدۡنَىٰٓ أَلَّا تَعُولُواْ
Kuma idan kun ji tsoron cewa ba za ku iya yin adalci ba dangane da marayu, to ku auri matan da kuke so, ko dai bibbiyu ko uku-uku ko kuma hurhuxu. To idan kun ji tsoron ba za ku iya yin adalci ba, to sai ku taqaita a kan xaya ko kuma abin da kuka mallaka na qwarqwarori. Hakan shi ya fi nisanta ku daga zalunci
وَءَاتُواْ ٱلنِّسَآءَ صَدُقَٰتِهِنَّ نِحۡلَةٗۚ فَإِن طِبۡنَ لَكُمۡ عَن شَيۡءٖ مِّنۡهُ نَفۡسٗا فَكُلُوهُ هَنِيٓـٔٗا مَّرِيٓـٔٗا
Kuma ku bai wa mata sadakinsu kyauta. Amma idan suka ba ku wani abu cikin daxin rai, to ku ci shi yana mai daxi da sauqin haxiya
وَلَا تُؤۡتُواْ ٱلسُّفَهَآءَ أَمۡوَٰلَكُمُ ٱلَّتِي جَعَلَ ٱللَّهُ لَكُمۡ قِيَٰمٗا وَٱرۡزُقُوهُمۡ فِيهَا وَٱكۡسُوهُمۡ وَقُولُواْ لَهُمۡ قَوۡلٗا مَّعۡرُوفٗا
Kuma kada ku bai wa (marayu) wawaye dukiyoyinku wadda Allah Ya sanya rayuwarku take tsaye a kai, kuma ku ciyar da su, kuma ku tufatar da su daga cikinta, kuma ku faxa musu magana mai daxi
وَٱبۡتَلُواْ ٱلۡيَتَٰمَىٰ حَتَّىٰٓ إِذَا بَلَغُواْ ٱلنِّكَاحَ فَإِنۡ ءَانَسۡتُم مِّنۡهُمۡ رُشۡدٗا فَٱدۡفَعُوٓاْ إِلَيۡهِمۡ أَمۡوَٰلَهُمۡۖ وَلَا تَأۡكُلُوهَآ إِسۡرَافٗا وَبِدَارًا أَن يَكۡبَرُواْۚ وَمَن كَانَ غَنِيّٗا فَلۡيَسۡتَعۡفِفۡۖ وَمَن كَانَ فَقِيرٗا فَلۡيَأۡكُلۡ بِٱلۡمَعۡرُوفِۚ فَإِذَا دَفَعۡتُمۡ إِلَيۡهِمۡ أَمۡوَٰلَهُمۡ فَأَشۡهِدُواْ عَلَيۡهِمۡۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ حَسِيبٗا
Kuma ku jarraba hankulan marayu, har lokacin da suka isa aure, to idan kun ga alamar hankali tare da su, sai ku ba su dukiyoyinsu; kuma kada ku ci dukiyarsu ta hanyar almubazzaranci da kuma gaggawa don gudun kada su girma. Duk kuma wanda ya kasance mawadaci ne, to ya kame kansa; wanda kuma ya kasance mabuqaci ne, to ya ci ta hanyar da ta dace. To idan za ku miqa musu dukiyoyinsu, sai ku kafa musu shaidu. Kuma Allah Ya isa Mai hisabi
لِّلرِّجَالِ نَصِيبٞ مِّمَّا تَرَكَ ٱلۡوَٰلِدَانِ وَٱلۡأَقۡرَبُونَ وَلِلنِّسَآءِ نَصِيبٞ مِّمَّا تَرَكَ ٱلۡوَٰلِدَانِ وَٱلۡأَقۡرَبُونَ مِمَّا قَلَّ مِنۡهُ أَوۡ كَثُرَۚ نَصِيبٗا مَّفۡرُوضٗا
Mazaje suna da wani kaso daga abin da mahaifa da dangi mafiya kusanci suka bari, haka mata su ma suna da wani kaso cikin abin da mahaifa da dangi mafiya kusanci suka bari, daga abin da yake xan kaxan ko mai yawa. Kaso ne wanda an riga an rarraba shi
وَإِذَا حَضَرَ ٱلۡقِسۡمَةَ أُوْلُواْ ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينُ فَٱرۡزُقُوهُم مِّنۡهُ وَقُولُواْ لَهُمۡ قَوۡلٗا مَّعۡرُوفٗا
Kuma idan dangi makusanta da marayu da mabuqata suka halarci rabon gado, to ku arzurta su daga cikin wannan dukiya, kuma ku faxa musu magana mai daxi
وَلۡيَخۡشَ ٱلَّذِينَ لَوۡ تَرَكُواْ مِنۡ خَلۡفِهِمۡ ذُرِّيَّةٗ ضِعَٰفًا خَافُواْ عَلَيۡهِمۡ فَلۡيَتَّقُواْ ٱللَّهَ وَلۡيَقُولُواْ قَوۡلٗا سَدِيدًا
Waxanda suke jin tsoron za su mutu su bar ‘ya’ya raunana a bayansu, suna kuma jin tsoron a zalunce su, to su kiyaye dokokin Allah, kuma su faxi magana ta daidai
إِنَّ ٱلَّذِينَ يَأۡكُلُونَ أَمۡوَٰلَ ٱلۡيَتَٰمَىٰ ظُلۡمًا إِنَّمَا يَأۡكُلُونَ فِي بُطُونِهِمۡ نَارٗاۖ وَسَيَصۡلَوۡنَ سَعِيرٗا
Lalle waxanda suke cin dukiyar marayu bisa zalunci, wuta ce kawai suke ci a cikkunansu; kuma da sannu za su shiga wuta mai tsananin quna
يُوصِيكُمُ ٱللَّهُ فِيٓ أَوۡلَٰدِكُمۡۖ لِلذَّكَرِ مِثۡلُ حَظِّ ٱلۡأُنثَيَيۡنِۚ فَإِن كُنَّ نِسَآءٗ فَوۡقَ ٱثۡنَتَيۡنِ فَلَهُنَّ ثُلُثَا مَا تَرَكَۖ وَإِن كَانَتۡ وَٰحِدَةٗ فَلَهَا ٱلنِّصۡفُۚ وَلِأَبَوَيۡهِ لِكُلِّ وَٰحِدٖ مِّنۡهُمَا ٱلسُّدُسُ مِمَّا تَرَكَ إِن كَانَ لَهُۥ وَلَدٞۚ فَإِن لَّمۡ يَكُن لَّهُۥ وَلَدٞ وَوَرِثَهُۥٓ أَبَوَاهُ فَلِأُمِّهِ ٱلثُّلُثُۚ فَإِن كَانَ لَهُۥٓ إِخۡوَةٞ فَلِأُمِّهِ ٱلسُّدُسُۚ مِنۢ بَعۡدِ وَصِيَّةٖ يُوصِي بِهَآ أَوۡ دَيۡنٍۗ ءَابَآؤُكُمۡ وَأَبۡنَآؤُكُمۡ لَا تَدۡرُونَ أَيُّهُمۡ أَقۡرَبُ لَكُمۡ نَفۡعٗاۚ فَرِيضَةٗ مِّنَ ٱللَّهِۗ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلِيمًا حَكِيمٗا
Allah Yana yi muku wasiyya game da ‘ya’yanku; namiji xaya yana da rabon ‘ya’ya mata biyu. Amma idan sun kasance mata ne biyu ko fiye da biyu, to suna da kaso biyu bisa uku na abin da ya bari; kuma idan ta kasance ‘ya ce guda xaya to tana da rabi. Kuma kowane xaya daga cikin mahaifansa biyu yana da kaso xaya bisa shida daga cikin abin da ya bari in ya kasance yana da xa ko ‘ya[1]. Idan kuma ya kasance ba shi da xa ko ‘ya, kuma mahaifansa biyu ne za su ci gadonsa, to mahaifiyarsa tana da kaso xaya bisa uku. Amma idan yana da ‘yan’uwa[2], to mahaifiyarsa tana da kaso xaya bisa shida; bayan an fitar da wasiyyar da aka yi ko kuma bashi[3]. Iyayenku da ‘ya’yanku, ba ku san daga cikinsu wane ne zai fi yi muku amfani ba. Rabo ne daga Allah. Lalle Allah Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai cikakkiyar hikima
1- Ko kuma jika na vangaren ‘ya’ya maza.
2- Watau Shaqiqai ko li’abbai ko li’ummai.
3- Ana fara fitar da bashi, sannan wasiyya wadda ba za ta wuce xaya bisa uku na dukiyar mamaci ba. Kuma babu wasiyya ga wanda yake da gado.
۞وَلَكُمۡ نِصۡفُ مَا تَرَكَ أَزۡوَٰجُكُمۡ إِن لَّمۡ يَكُن لَّهُنَّ وَلَدٞۚ فَإِن كَانَ لَهُنَّ وَلَدٞ فَلَكُمُ ٱلرُّبُعُ مِمَّا تَرَكۡنَۚ مِنۢ بَعۡدِ وَصِيَّةٖ يُوصِينَ بِهَآ أَوۡ دَيۡنٖۚ وَلَهُنَّ ٱلرُّبُعُ مِمَّا تَرَكۡتُمۡ إِن لَّمۡ يَكُن لَّكُمۡ وَلَدٞۚ فَإِن كَانَ لَكُمۡ وَلَدٞ فَلَهُنَّ ٱلثُّمُنُ مِمَّا تَرَكۡتُمۚ مِّنۢ بَعۡدِ وَصِيَّةٖ تُوصُونَ بِهَآ أَوۡ دَيۡنٖۗ وَإِن كَانَ رَجُلٞ يُورَثُ كَلَٰلَةً أَوِ ٱمۡرَأَةٞ وَلَهُۥٓ أَخٌ أَوۡ أُخۡتٞ فَلِكُلِّ وَٰحِدٖ مِّنۡهُمَا ٱلسُّدُسُۚ فَإِن كَانُوٓاْ أَكۡثَرَ مِن ذَٰلِكَ فَهُمۡ شُرَكَآءُ فِي ٱلثُّلُثِۚ مِنۢ بَعۡدِ وَصِيَّةٖ يُوصَىٰ بِهَآ أَوۡ دَيۡنٍ غَيۡرَ مُضَآرّٖۚ وَصِيَّةٗ مِّنَ ٱللَّهِۗ وَٱللَّهُ عَلِيمٌ حَلِيمٞ
Kuma kuna da rabin abin da matanku suka bari in ya kasance ba su da xa ko ‘ya, amma idan sun kasance suna da xa ko ‘ya, to kuna da kaso xaya bisa huxu na abin da suka bari, bayan zartar da wasiyyar da suka yi ko kuma bashi. Kuma suna da kaso xaya bisa huxu[1] na abin da kuka bari, in ya kasance ba ku da xa ko ‘ya. Amma idan ya kasance kuna da xa ko ‘ya to (matanku) suna da kaso xaya cikin takwas na abin da kuka bari, bayan zartar da wasiyyar da kuka yi ko kuma bashi. Amma idan namiji ne za a gaje shi a matsayin kalala[2] ko mace, kuma yana da xan’uwa guda xaya ko ‘yar’uwa guda xaya, to kowanne xaya yana da kaso xaya bisa shida. Amma idan sun fi haka yawa, to za su yi tarayya cikin kaso xaya bisa uku, bayan zartar da wasiyyar da aka yi ko kuma bashi, ba wanda zai cutar da (magadansa) ba. Allah Yana yi muku wasiyya matuqar wasiyya. Allah kuma Mai cikakken sani ne, Mai haquri
1- Idan sama da mace xaya ce, to za su yi tarayya ne a cikin wannan kason.
2- Kalala shi ne mamaci; namiji ko mace da bai bar ‘ya’ya ko iyaye ba, sai ‘yan’uwa.