Surah: Suratun Najm

Ayah : 12

أَفَتُمَٰرُونَهُۥ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ

Yanzu kwa riqa jayayya da shi kan abin da yake gani?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 13

وَلَقَدۡ رَءَاهُ نَزۡلَةً أُخۡرَىٰ

Haqiqa ya gan shi (Jibrilu) a wani karon ma[1]


1- Watau lokacin Isra’i da Mi’iraji, inda ya gan shi a halittarsa ta asali.


Surah: Suratun Najm

Ayah : 14

عِندَ سِدۡرَةِ ٱلۡمُنتَهَىٰ

A wurin Magaryar tuqewa



Surah: Suratun Najm

Ayah : 15

عِندَهَا جَنَّةُ ٱلۡمَأۡوَىٰٓ

A wurinta ne Aljannar makoma take



Surah: Suratun Najm

Ayah : 16

إِذۡ يَغۡشَى ٱلسِّدۡرَةَ مَا يَغۡشَىٰ

A yayin da abin da ya lulluve Magaryar (na ban mamaki) ya lulluve ta



Surah: Suratun Najm

Ayah : 17

مَا زَاغَ ٱلۡبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ

Ganin (nasa) bai karkace ba, kuma bai zarme ba



Surah: Suratun Najm

Ayah : 18

لَقَدۡ رَأَىٰ مِنۡ ءَايَٰتِ رَبِّهِ ٱلۡكُبۡرَىٰٓ

Haqiqa ya ga wasu ayoyin Ubangijinsa manya-manya



Surah: Suratun Najm

Ayah : 19

أَفَرَءَيۡتُمُ ٱللَّـٰتَ وَٱلۡعُزَّىٰ

Ku ba ni labarin (gumakan) Lata da Uzza



Surah: Suratun Najm

Ayah : 20

وَمَنَوٰةَ ٱلثَّالِثَةَ ٱلۡأُخۡرَىٰٓ

Da Manata cikon ta ukunsu



Surah: Suratun Najm

Ayah : 21

أَلَكُمُ ٱلذَّكَرُ وَلَهُ ٱلۡأُنثَىٰ

Yanzu xa namiji zai zama naku, Shi kuma Ya tashi da ‘ya mace?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 22

تِلۡكَ إِذٗا قِسۡمَةٞ ضِيزَىٰٓ

Idan haka ne wannan rabon na zalunci ne[1]


1- Domin ya qunshi Fifita mahaluki a kan Mahalicci.


Surah: Suratun Najm

Ayah : 23

إِنۡ هِيَ إِلَّآ أَسۡمَآءٞ سَمَّيۡتُمُوهَآ أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُم مَّآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلۡطَٰنٍۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ وَمَا تَهۡوَى ٱلۡأَنفُسُۖ وَلَقَدۡ جَآءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ ٱلۡهُدَىٰٓ

Su ba komai ba ne face sunaye da kuka sa musu, ku da iyayenku, Allah bai saukar muku da wata hujja ba game da su. Ba abin da suke bi sai zato da son zuciya. Haqiqa kuwa shiriya ta zo musu daga Ubangijinsu



Surah: Suratun Najm

Ayah : 24

أَمۡ لِلۡإِنسَٰنِ مَا تَمَنَّىٰ

Ko kuwa sai mutum ya sami abin da yake buri ne?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 25

فَلِلَّهِ ٱلۡأٓخِرَةُ وَٱلۡأُولَىٰ

To lahira da duniya duka na Allah ne



Surah: Suratun Najm

Ayah : 26

۞وَكَم مِّن مَّلَكٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغۡنِي شَفَٰعَتُهُمۡ شَيۡـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ أَن يَأۡذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرۡضَىٰٓ

Mala’iku nawa ne a cikin sammai cetonsu ba ya amfanar da komai sai da izinin Allah ga waxanda Ya ga dama Ya kuma yarda (da shi)?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 27

إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ لَيُسَمُّونَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ تَسۡمِيَةَ ٱلۡأُنثَىٰ

Lalle waxanda ba sa yin imani da ranar lahira suna kiran mala’iku da sunan mata



Surah: Suratun Najm

Ayah : 28

وَمَا لَهُم بِهِۦ مِنۡ عِلۡمٍۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّۖ وَإِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـٔٗا

Kuma ba su da wani ilimi game da haka; ba abin da suke bi sai zato; shi kuma zato, lalle ba ya wadatar da komai game da gaskiya



Surah: Suratun Najm

Ayah : 29

فَأَعۡرِضۡ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكۡرِنَا وَلَمۡ يُرِدۡ إِلَّا ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا

Sai ka kau da kai daga duk wanda ya ba da baya daga ambatonmu, bai kuma yi nufin komai ba sai rayuwar duniya



Surah: Suratun Najm

Ayah : 30

ذَٰلِكَ مَبۡلَغُهُم مِّنَ ٱلۡعِلۡمِۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِمَنِ ٱهۡتَدَىٰ

Wannan ne maqurar iliminsu. Lalle Ubangijinka Shi ne Ya fi sanin wanda ya vace daga hanyarsa kuma Shi Ya fi sanin wanda ya shiriya



Surah: Suratun Najm

Ayah : 31

وَلِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ لِيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ أَسَـٰٓـُٔواْ بِمَا عَمِلُواْ وَيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ أَحۡسَنُواْ بِٱلۡحُسۡنَى

Kuma abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa na Allah ne, don Ya saka wa waxanda suka munana da irin abin da suka aikata, Ya kuma saka wa waxanda suka kyautata da mafi kyan sakamako



Surah: Suratun Najm

Ayah : 32

ٱلَّذِينَ يَجۡتَنِبُونَ كَبَـٰٓئِرَ ٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡفَوَٰحِشَ إِلَّا ٱللَّمَمَۚ إِنَّ رَبَّكَ وَٰسِعُ ٱلۡمَغۡفِرَةِۚ هُوَ أَعۡلَمُ بِكُمۡ إِذۡ أَنشَأَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ وَإِذۡ أَنتُمۡ أَجِنَّةٞ فِي بُطُونِ أُمَّهَٰتِكُمۡۖ فَلَا تُزَكُّوٓاْ أَنفُسَكُمۡۖ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَنِ ٱتَّقَىٰٓ

(Su ne) waxanda suke nisantar manya-manyan zunubai da munanan ayyukan savo, sai dai ‘yan qananan zunubai. Lalle Ubangijinka Mayalwacin gafara ne. Shi ne Ya fi sanin ku, tun sanda Ya halicce ku daga qasa, sai ga ku kun zama ‘yan tayi a cikin cikin iyayenku mata; to kada ku tsarkake kanku; Shi ne Ya fi sanin wanda ya fi taqawa



Surah: Suratun Najm

Ayah : 33

أَفَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي تَوَلَّىٰ

Ka ba ni labarin wanda ya ba da baya



Surah: Suratun Najm

Ayah : 34

وَأَعۡطَىٰ قَلِيلٗا وَأَكۡدَىٰٓ

Ya kuma bayar da dukiya kaxan kuma ya yi rowa



Surah: Suratun Najm

Ayah : 35

أَعِندَهُۥ عِلۡمُ ٱلۡغَيۡبِ فَهُوَ يَرَىٰٓ

Shin yana da ilimin gaibu ne don haka yana ganin (komai)?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 36

أَمۡ لَمۡ يُنَبَّأۡ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىٰ

Ko ba a ba shi labarin abin da yake cikin takardun Musa ba ne?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 37

وَإِبۡرَٰهِيمَ ٱلَّذِي وَفَّىٰٓ

Da kuma Ibrahimu wanda ya cika alqawari?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 38

أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٞ وِزۡرَ أُخۡرَىٰ

Cewa: “Wani rai ba ya xaukar nauyin laifin wani



Surah: Suratun Najm

Ayah : 39

وَأَن لَّيۡسَ لِلۡإِنسَٰنِ إِلَّا مَا سَعَىٰ

“Kuma mutum bai mallaki wani sakamako ba sai na abin da ya aikata



Surah: Suratun Najm

Ayah : 40

وَأَنَّ سَعۡيَهُۥ سَوۡفَ يُرَىٰ

“Kuma lalle aikin nasa ba da daxewa ba za a gan shi



Surah: Suratun Najm

Ayah : 41

ثُمَّ يُجۡزَىٰهُ ٱلۡجَزَآءَ ٱلۡأَوۡفَىٰ

“Sannan a saka masa da cikakken sakamako