Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 47

وَإِذۡ يَتَحَآجُّونَ فِي ٱلنَّارِ فَيَقُولُ ٱلضُّعَفَـٰٓؤُاْ لِلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُوٓاْ إِنَّا كُنَّا لَكُمۡ تَبَعٗا فَهَلۡ أَنتُم مُّغۡنُونَ عَنَّا نَصِيبٗا مِّنَ ٱلنَّارِ

(Ka tuna) kuma lokacin da suke ta yin jayayya a cikin wuta, sai raunanan su riqa ce wa waxanda suka yi girman kai: “Lalle mun kasance mabiyanku (a duniya), to shin za ku iya xauke mana wani kaso na (azabar) wuta?”



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 48

قَالَ ٱلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُوٓاْ إِنَّا كُلّٞ فِيهَآ إِنَّ ٱللَّهَ قَدۡ حَكَمَ بَيۡنَ ٱلۡعِبَادِ

Waxanda suka yi girman kai sai su ce: “Lalle mu duka a cikinta muke, lalle Allah Ya riga Ya yi hukunci tsakanin bayi.”



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 49

وَقَالَ ٱلَّذِينَ فِي ٱلنَّارِ لِخَزَنَةِ جَهَنَّمَ ٱدۡعُواْ رَبَّكُمۡ يُخَفِّفۡ عَنَّا يَوۡمٗا مِّنَ ٱلۡعَذَابِ

Kuma waxanda suke cikin wuta suka ce da masu tsaron Jahannama: “Ku roqa mana Ubangijinku mana Ya sauqaqe mana azaba ta wuni (xaya).”



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 50

قَالُوٓاْ أَوَلَمۡ تَكُ تَأۡتِيكُمۡ رُسُلُكُم بِٱلۡبَيِّنَٰتِۖ قَالُواْ بَلَىٰۚ قَالُواْ فَٱدۡعُواْۗ وَمَا دُعَـٰٓؤُاْ ٱلۡكَٰفِرِينَ إِلَّا فِي ضَلَٰلٍ

Suka ce: “Yanzu manzanninku ba su kasance suna zo muku da (ayoyi) bayyanannu ba?” Suka ce: “Haka ne (sun zo)”. Sai su ce: “To sai ku yi ta roqon. Roqon kafirai kuwa bai zamo ba sai a tave.”



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 51

إِنَّا لَنَنصُرُ رُسُلَنَا وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَيَوۡمَ يَقُومُ ٱلۡأَشۡهَٰدُ

Lalle Mu tabbas Muna taimakon manzanninmu da kuma waxanda suka yi imani a rayuwar duniya da kuma ranar da shedu za su tsaya



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 52

يَوۡمَ لَا يَنفَعُ ٱلظَّـٰلِمِينَ مَعۡذِرَتُهُمۡۖ وَلَهُمُ ٱللَّعۡنَةُ وَلَهُمۡ سُوٓءُ ٱلدَّارِ

Ranar da hanzarin azzulamai ba zai amfane su ba; la’ana kuma ta tabbata a kansu, suna kuma da mummunan gida



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 53

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡهُدَىٰ وَأَوۡرَثۡنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱلۡكِتَٰبَ

Kuma haqiqa Mun bai wa Musa shiriya, Muka kuwa gadar wa Banu-Isra’ila littafin (Attaura)



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 54

هُدٗى وَذِكۡرَىٰ لِأُوْلِي ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Don shiriya da wa’azantuwa ga masu hankali



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 55

فَٱصۡبِرۡ إِنَّ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٞ وَٱسۡتَغۡفِرۡ لِذَنۢبِكَ وَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ بِٱلۡعَشِيِّ وَٱلۡإِبۡكَٰرِ

Sai ka yi haquri, lalle alqawarin Allah gaskiya ne, ka kuma nemi gafarar zunubinka, kuma ka yi tasbihi da yabon Ubangijinka a maraice da safiya



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 56

إِنَّ ٱلَّذِينَ يُجَٰدِلُونَ فِيٓ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ بِغَيۡرِ سُلۡطَٰنٍ أَتَىٰهُمۡ إِن فِي صُدُورِهِمۡ إِلَّا كِبۡرٞ مَّا هُم بِبَٰلِغِيهِۚ فَٱسۡتَعِذۡ بِٱللَّهِۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡبَصِيرُ

Lalle waxanda suke yin jayayya game da ayoyin Allah ba tare da wata hujja da ta zo musu ba, ba komai a cikin zukatansu sai neman xaukaka wadda ba za su same ta ba. Sai ka nemi tsari daga Allah; lalle Shi Mai ji ne, Mai gani



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 57

لَخَلۡقُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ أَكۡبَرُ مِنۡ خَلۡقِ ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Tabbas halittar sammai da qasa ta fi girma a kan halittar mutane, sai dai kuma yawancin mutane ba sa sanin (haka)



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 58

وَمَا يَسۡتَوِي ٱلۡأَعۡمَىٰ وَٱلۡبَصِيرُ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَلَا ٱلۡمُسِيٓءُۚ قَلِيلٗا مَّا تَتَذَكَّرُونَ

Kuma makaho da mai gani ba za su yi daidai ba, kuma waxanda suka yi imani suka yi aiki nagari ba za su yi (daidai) da mai mummunan aiki ba. Kaxan ne qwarai kuke wa’azantuwa



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 59

إِنَّ ٱلسَّاعَةَ لَأٓتِيَةٞ لَّا رَيۡبَ فِيهَا وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يُؤۡمِنُونَ

Lalle alqiyama tabbas za ta zo babu kokwanto a cikinta, sai dai kuma yawancin mutane ba sa yin imani



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 60

وَقَالَ رَبُّكُمُ ٱدۡعُونِيٓ أَسۡتَجِبۡ لَكُمۡۚ إِنَّ ٱلَّذِينَ يَسۡتَكۡبِرُونَ عَنۡ عِبَادَتِي سَيَدۡخُلُونَ جَهَنَّمَ دَاخِرِينَ

Ubangijinku kuma Ya ce: “Ku roqe Ni zan amsa muku. Lalle waxanda suke yin girman kai game da bauta min, ba da daxewa ba za su shiga Jahannama a wulaqance.”



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 61

ٱللَّهُ ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلَّيۡلَ لِتَسۡكُنُواْ فِيهِ وَٱلنَّهَارَ مُبۡصِرًاۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَذُو فَضۡلٍ عَلَى ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَشۡكُرُونَ

Allah ne wanda Ya halitta muku dare don ku natsu a cikinsa, rana kuma don ku ga (yadda za ku yi harka). Lalle Allah Mai falala ne ga mutane, sai dai kuma yawancinsu ba sa godewa



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 62

ذَٰلِكُمُ ٱللَّهُ رَبُّكُمۡ خَٰلِقُ كُلِّ شَيۡءٖ لَّآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ فَأَنَّىٰ تُؤۡفَكُونَ

Wannan Shi ne Allah Ubangijinku, Mahaliccin komai, babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi; to ina ne ake kautar da ku?



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 63

كَذَٰلِكَ يُؤۡفَكُ ٱلَّذِينَ كَانُواْ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ يَجۡحَدُونَ

Kamar haka ne ake karkatar da waxanda suka zamanto suna musanta ayoyin Allah



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 64

ٱللَّهُ ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلۡأَرۡضَ قَرَارٗا وَٱلسَّمَآءَ بِنَآءٗ وَصَوَّرَكُمۡ فَأَحۡسَنَ صُوَرَكُمۡ وَرَزَقَكُم مِّنَ ٱلطَّيِّبَٰتِۚ ذَٰلِكُمُ ٱللَّهُ رَبُّكُمۡۖ فَتَبَارَكَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Allah ne wanda Ya sanya muku qasa ta zama wurin zama, sama kuma ta zama rufi, Ya kuma suranta ku, sai Ya kyautata surorinku, Ya kuma arzuta ku da daxaxan abubuwa. Wannan fa Shi ne Allah Ubangijinku. To Allah Ubangijin talikai albarkatunsa sun yawaita



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 65

هُوَ ٱلۡحَيُّ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ فَٱدۡعُوهُ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَۗ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Shi Rayayye ne, babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi, sai ku roqe Shi kuna masu tsantsanta addini a gare Shi. Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 66

۞قُلۡ إِنِّي نُهِيتُ أَنۡ أَعۡبُدَ ٱلَّذِينَ تَدۡعُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ لَمَّا جَآءَنِيَ ٱلۡبَيِّنَٰتُ مِن رَّبِّي وَأُمِرۡتُ أَنۡ أُسۡلِمَ لِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ka ce: “Lalle ni an hana ni in bauta wa waxanda kuke bauta wa ba Allah ba a yayin da (ayoyi) bayyanannu suka zo min daga Ubangijina, an kuma umarce ni da in miqa wuya ga Ubangijin talikai



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 67

هُوَ ٱلَّذِي خَلَقَكُم مِّن تُرَابٖ ثُمَّ مِن نُّطۡفَةٖ ثُمَّ مِنۡ عَلَقَةٖ ثُمَّ يُخۡرِجُكُمۡ طِفۡلٗا ثُمَّ لِتَبۡلُغُوٓاْ أَشُدَّكُمۡ ثُمَّ لِتَكُونُواْ شُيُوخٗاۚ وَمِنكُم مَّن يُتَوَفَّىٰ مِن قَبۡلُۖ وَلِتَبۡلُغُوٓاْ أَجَلٗا مُّسَمّٗى وَلَعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

“Shi ne wanda Ya halicce ku daga qasa, sannan daga xigon maniyyi, sannan daga gudan jini, daga nan Ya fito da ku kuna jarirai, sannan don ku kai qarfinku, sannan kuma ku zama tsofaffi. Daga cikinku kuma akwai wanda ake karvar ransa kafin wannan; don kuma ku isa zuwa wani lokaci qayyadajje[1], don kuma ku hankalta


1- Wanda ba za su rage ba ba kuma za su qara ba, watau lokacin mutuwarsu.


Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 68

هُوَ ٱلَّذِي يُحۡيِۦ وَيُمِيتُۖ فَإِذَا قَضَىٰٓ أَمۡرٗا فَإِنَّمَا يَقُولُ لَهُۥ كُن فَيَكُونُ

“Shi ne wanda Yake rayawa Yake kuma kashewa; to idan zai hukunta wani al’amari sai kawai Ya ce da shi: ‘Kasance’, sai ya kasance.”



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 69

أَلَمۡ تَرَ إِلَى ٱلَّذِينَ يُجَٰدِلُونَ فِيٓ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ أَنَّىٰ يُصۡرَفُونَ

Ba ka ganin waxanda suke jayayya game da ayoyin Allah, to ta yaya ake kautar da su?



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 70

ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِٱلۡكِتَٰبِ وَبِمَآ أَرۡسَلۡنَا بِهِۦ رُسُلَنَاۖ فَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ

(Su ne) waxanda suka qaryata Alqur’ani da kuma abin da Muka aiko manzanninmu da shi; to ba da daxewa ba za su sani



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 71

إِذِ ٱلۡأَغۡلَٰلُ فِيٓ أَعۡنَٰقِهِمۡ وَٱلسَّلَٰسِلُ يُسۡحَبُونَ

A yayin da ququmai suke a wuyoyinsu, da kuma sarqoqi ana jan su



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 72

فِي ٱلۡحَمِيمِ ثُمَّ فِي ٱلنَّارِ يُسۡجَرُونَ

A cikin tafasasshen ruwan, sannan kuma ana qona su a cikin wuta



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 73

ثُمَّ قِيلَ لَهُمۡ أَيۡنَ مَا كُنتُمۡ تُشۡرِكُونَ

Sannan kuma a ce da su: “Ina abin da kuka kasance kuna shirka da shi?



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 74

مِن دُونِ ٱللَّهِۖ قَالُواْ ضَلُّواْ عَنَّا بَل لَّمۡ نَكُن نَّدۡعُواْ مِن قَبۡلُ شَيۡـٔٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ ٱلۡكَٰفِرِينَ

“Wanda ba Allah ba?” Suka ce: “Sun vace mana; ai ba mu kasance muna bauta wa wani abu ba a da”. Kamar haka ne Allah Yake vatar da kafirai



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 75

ذَٰلِكُم بِمَا كُنتُمۡ تَفۡرَحُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ بِغَيۡرِ ٱلۡحَقِّ وَبِمَا كُنتُمۡ تَمۡرَحُونَ

Wannan fa (ya same ku ne) saboda abin da kuka kasance kuna yin girman kai da shi a bayan qasa ba da wata hujja ba, da kuma abin da kuka kasance kuna yin walwala da shi



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 76

ٱدۡخُلُوٓاْ أَبۡوَٰبَ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَاۖ فَبِئۡسَ مَثۡوَى ٱلۡمُتَكَبِّرِينَ

(Za a ce da su): “Ku shiga qofofin Jahannama kuna masu dawwama a cikinta”; to makomar masu girman kai ta munana