وَجَعَلۡنَا بَيۡنَهُمۡ وَبَيۡنَ ٱلۡقُرَى ٱلَّتِي بَٰرَكۡنَا فِيهَا قُرٗى ظَٰهِرَةٗ وَقَدَّرۡنَا فِيهَا ٱلسَّيۡرَۖ سِيرُواْ فِيهَا لَيَالِيَ وَأَيَّامًا ءَامِنِينَ
Muka kuma sanya wasu alqaryu mabayyana a tsakaninsu (mutan Saba’u) da alqaryar da Muka sa albarka a cikinta (wato qasar Sham)[1], Muka kuma taqaita zangon tafiya a tsakaninsu (alqaryun; Muka ce): “Ku yi tafiya a cikinsu dare da rana cikin aminci.”
1- Watau Allah () ya sanya wasu fitattun alqaryu da matafiya kan iya hango su daga nesa, wanda hakan ya sauqaqa musu tafiye-tafiyensu.
فَقَالُواْ رَبَّنَا بَٰعِدۡ بَيۡنَ أَسۡفَارِنَا وَظَلَمُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ فَجَعَلۡنَٰهُمۡ أَحَادِيثَ وَمَزَّقۡنَٰهُمۡ كُلَّ مُمَزَّقٍۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّكُلِّ صَبَّارٖ شَكُورٖ
Sai suka ce: “Ya Ubangijinmu, Ka qaddara nisa tsakanin zangunan tafiyarmu,” suka kuwa zalunci kansu, sai Muka mai da su tarihi[1], Muka kuma warwatsa su wuri-wuri. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga duk wani mai yin haquri, mai yin godiya
1- Watau Allah () ya tarwatsa su suka warwatsu a garuruwa daban-daban har haxuwa da junansu ta yi musu wahala.
وَلَقَدۡ صَدَّقَ عَلَيۡهِمۡ إِبۡلِيسُ ظَنَّهُۥ فَٱتَّبَعُوهُ إِلَّا فَرِيقٗا مِّنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Kuma haqiqa Iblisu ya tabbatar da zatonsa a kansu gaskiya ne[1], sai suka bi shi, in ban da wata qungiya ta muminai
1- Watau na cewa zai iya vatar da su ya raba su da gaskiya.
وَمَا كَانَ لَهُۥ عَلَيۡهِم مِّن سُلۡطَٰنٍ إِلَّا لِنَعۡلَمَ مَن يُؤۡمِنُ بِٱلۡأٓخِرَةِ مِمَّنۡ هُوَ مِنۡهَا فِي شَكّٖۗ وَرَبُّكَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٍ حَفِيظٞ
Shi kuwa ba shi da wani qarfi a kansu, sai dai (Mun yi haka ne) don Mu bayyana wanda yake imani da ranar lahira da kuma wanda yake cikin shakka game da ita. Ubangijinka kuwa Mai kiyaye komai ne
قُلِ ٱدۡعُواْ ٱلَّذِينَ زَعَمۡتُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ لَا يَمۡلِكُونَ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَلَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا لَهُمۡ فِيهِمَا مِن شِرۡكٖ وَمَا لَهُۥ مِنۡهُم مِّن ظَهِيرٖ
Ka ce: “Ku kirawo waxanda kuka riya (cewa su ne iyayen giji) ba Allah ba;” ba sa mallakar wani abu daidai da qwayar zarra a cikin sammai ko a cikin qasa, ba kuma su da wata tarayya a cikinsu, ba Shi kuma da wani mataimaki daga cikinsu
وَلَا تَنفَعُ ٱلشَّفَٰعَةُ عِندَهُۥٓ إِلَّا لِمَنۡ أَذِنَ لَهُۥۚ حَتَّىٰٓ إِذَا فُزِّعَ عَن قُلُوبِهِمۡ قَالُواْ مَاذَا قَالَ رَبُّكُمۡۖ قَالُواْ ٱلۡحَقَّۖ وَهُوَ ٱلۡعَلِيُّ ٱلۡكَبِيرُ
Kuma ceto ba ya amfani a wurinsa sai ga wanda Ya yi wa izinin yin sa. Har idan an cire tsoro daga cikin zukatansu[1], sai su ce: “Me Ubangijinku Ya ce ne?” Suka ce: “Gaskiya Ya faxa, kuma Shi ne Maxaukaki, Mai girma.”
1- Saboda cikar mulkin Allah idan ya yi wata magana mala’iku gaba xaya sukan buga fukafukansu suna masu rusunawa ga maganarsa, suna masu cike da tsoro.
۞قُلۡ مَن يَرۡزُقُكُم مِّنَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ قُلِ ٱللَّهُۖ وَإِنَّآ أَوۡ إِيَّاكُمۡ لَعَلَىٰ هُدًى أَوۡ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ
Ka ce: “Wane ne yake arzuta ku daga sammai da qasa?” Ka ce: “Allah ne; kuma mu ko ku (xaya daga cikinmu) lalle yana a kan shiriya ko kuma yana cikin vata mabayyani.”
قُل لَّا تُسۡـَٔلُونَ عَمَّآ أَجۡرَمۡنَا وَلَا نُسۡـَٔلُ عَمَّا تَعۡمَلُونَ
Ka ce: “Ba za a tambaye ku ba game da laifin da muka yi, mu ma kuma ba za a tambaye mu ba game da abin da kuke aikatawa.”
قُلۡ يَجۡمَعُ بَيۡنَنَا رَبُّنَا ثُمَّ يَفۡتَحُ بَيۡنَنَا بِٱلۡحَقِّ وَهُوَ ٱلۡفَتَّاحُ ٱلۡعَلِيمُ
Ka ce: “Ubangijinmu zai tattara mu sannan Ya yi hukunci a tsakaninmu da gaskiya, Shi ne kuwa Mai hukunci, Masani.”
قُلۡ أَرُونِيَ ٱلَّذِينَ أَلۡحَقۡتُم بِهِۦ شُرَكَآءَۖ كَلَّاۚ بَلۡ هُوَ ٱللَّهُ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ
Ka ce: “Ku nuna min waxanda kuka riskar da su a matsayin abokan tarayya da Shi; ku bar wannan magana! Shi ne Allah Mabuwayi Mai hikima.”
وَمَآ أَرۡسَلۡنَٰكَ إِلَّا كَآفَّةٗ لِّلنَّاسِ بَشِيرٗا وَنَذِيرٗا وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ
Ba Mu kuma aiko ka ba sai ga mutane baki xaya kana mai albishir mai kuma gargaxi, sai dai kuma yawancin mutane ba sa sanin (hakan)
وَيَقُولُونَ مَتَىٰ هَٰذَا ٱلۡوَعۡدُ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ
Suna kuma cewa: “Yaushe ne wannan alqawarin (na ranar alqiyama) zai zo, idan kun kasance masu gaskiya?”
قُل لَّكُم مِّيعَادُ يَوۡمٖ لَّا تَسۡتَـٔۡخِرُونَ عَنۡهُ سَاعَةٗ وَلَا تَسۡتَقۡدِمُونَ
Ka ce: “Kuna da ajiyayyar rana da ba za ku jinkirta ba daga gare ta daidai da sa’a, ba kuma za ku wuce ta ba.”
وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَن نُّؤۡمِنَ بِهَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانِ وَلَا بِٱلَّذِي بَيۡنَ يَدَيۡهِۗ وَلَوۡ تَرَىٰٓ إِذِ ٱلظَّـٰلِمُونَ مَوۡقُوفُونَ عِندَ رَبِّهِمۡ يَرۡجِعُ بَعۡضُهُمۡ إِلَىٰ بَعۡضٍ ٱلۡقَوۡلَ يَقُولُ ٱلَّذِينَ ٱسۡتُضۡعِفُواْ لِلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُواْ لَوۡلَآ أَنتُمۡ لَكُنَّا مُؤۡمِنِينَ
Kuma kafirai suka ce: “Ba za mu yi imani da wannan Alqur’ani ba, haka ma da wanda yake gabaninsa (na saukakkun littattafai).” Da kuwa za ka ga lokacin da za a tsai da azzalumai wajen Ubangijinsu suna mayar wa da juna magana, masu rauninsu (mabiya) suna ce wa masu girman kai (watau shugabanninsu): “Ba don ku ba da mun zamanto muminai.”
قَالَ ٱلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُواْ لِلَّذِينَ ٱسۡتُضۡعِفُوٓاْ أَنَحۡنُ صَدَدۡنَٰكُمۡ عَنِ ٱلۡهُدَىٰ بَعۡدَ إِذۡ جَآءَكُمۖ بَلۡ كُنتُم مُّجۡرِمِينَ
Masu girman kan suka ce wa raunanan: “Yanzu mu muka hana ku ku shiriya bayan ta zo muku? Ba haka ba ne, kun dai kasance masu laifi ne.”
وَقَالَ ٱلَّذِينَ ٱسۡتُضۡعِفُواْ لِلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُواْ بَلۡ مَكۡرُ ٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِ إِذۡ تَأۡمُرُونَنَآ أَن نَّكۡفُرَ بِٱللَّهِ وَنَجۡعَلَ لَهُۥٓ أَندَادٗاۚ وَأَسَرُّواْ ٱلنَّدَامَةَ لَمَّا رَأَوُاْ ٱلۡعَذَابَۚ وَجَعَلۡنَا ٱلۡأَغۡلَٰلَ فِيٓ أَعۡنَاقِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۖ هَلۡ يُجۡزَوۡنَ إِلَّا مَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ
Raunanan kuma suka ce da manyan masu girman kan: “Ba haka ba ne, makircin dare da na rana ne (da kuke qulla mana ya hana mu shiriya), yayin da kuke umartar mu da mu kafirce wa Allah, mu kuma sanya masa abokan tarayya.” Suka kuma bayyana nadama lokacin da suka ga azaba, kuma Muka sanya ququmi a wuyan waxanda suka kafirta, ba kuwa za a saka musu da komai ba sai da irin abin da suka kasance suna aikatawa
وَمَآ أَرۡسَلۡنَا فِي قَرۡيَةٖ مِّن نَّذِيرٍ إِلَّا قَالَ مُتۡرَفُوهَآ إِنَّا بِمَآ أُرۡسِلۡتُم بِهِۦ كَٰفِرُونَ
Ba Mu tava aiko wani mai gargaxi cikin wata alqarya ba sai mawadatan cikinta sun ce: “Mu dai masu kafirce wa abin da aka aiko ku da shi ne.”
وَقَالُواْ نَحۡنُ أَكۡثَرُ أَمۡوَٰلٗا وَأَوۡلَٰدٗا وَمَا نَحۡنُ بِمُعَذَّبِينَ
Suka kuma ce: “Mu muka fi kowa yawan dukiya da ‘ya’ya, kuma mu ba waxanda za a azabtar ba ne.”
قُلۡ إِنَّ رَبِّي يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ وَيَقۡدِرُ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ
Ka ce: “Lalle Ubangijina Yana shimfixa arziki ga wanda Ya ga dama, Ya kuma quntata, sai dai kuma yawancin mutane ba su san (haka) ba.”
وَمَآ أَمۡوَٰلُكُمۡ وَلَآ أَوۡلَٰدُكُم بِٱلَّتِي تُقَرِّبُكُمۡ عِندَنَا زُلۡفَىٰٓ إِلَّا مَنۡ ءَامَنَ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا فَأُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ جَزَآءُ ٱلضِّعۡفِ بِمَا عَمِلُواْ وَهُمۡ فِي ٱلۡغُرُفَٰتِ ءَامِنُونَ
Kuma ba dukiyoyinku da ‘ya’yanku ne za su kusantar da ku gare Mu ba, sai wanda ya yi imani ya kuma yi aiki nagari, to waxannan suna da sakamako ninkin-baninki saboda abin da suka aikata, suna kuma amintattu cikin benaye
وَٱلَّذِينَ يَسۡعَوۡنَ فِيٓ ءَايَٰتِنَا مُعَٰجِزِينَ أُوْلَـٰٓئِكَ فِي ٱلۡعَذَابِ مُحۡضَرُونَ
Waxanda kuwa suke yin qoqari na vata ayoyinmu, don su nuna gazawarmu, waxannan cikin azaba za a halartar da su
قُلۡ إِنَّ رَبِّي يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦ وَيَقۡدِرُ لَهُۥۚ وَمَآ أَنفَقۡتُم مِّن شَيۡءٖ فَهُوَ يُخۡلِفُهُۥۖ وَهُوَ خَيۡرُ ٱلرَّـٰزِقِينَ
Ka ce: “Lalle Ubangijna Yana shimfixa arziki ga wanda ya ga dama cikin bayinsa, Yana kuma quntata masa. Kuma duk abin da kuka ciyar (don Allah), to Shi ne zai ba ku madadinsa, Shi ne kuwa Fiyayyen masu arzutawa.”
وَيَوۡمَ يَحۡشُرُهُمۡ جَمِيعٗا ثُمَّ يَقُولُ لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ أَهَـٰٓؤُلَآءِ إِيَّاكُمۡ كَانُواْ يَعۡبُدُونَ
Kuma (ka tuna) ranar da zai tattaro su gaba xaya sannan Ya ce da mala’iku: “Ashe yanzu ku ne waxannan suka kasance suna bauta wa?”
قَالُواْ سُبۡحَٰنَكَ أَنتَ وَلِيُّنَا مِن دُونِهِمۖ بَلۡ كَانُواْ يَعۡبُدُونَ ٱلۡجِنَّۖ أَكۡثَرُهُم بِهِم مُّؤۡمِنُونَ
Suka ce: “Tsarki ya tabbata a gare Ka, Kai ne Majivincinmu ba su ba.” Ba haka ba ne, sun kasance suna bauta wa aljannu ne; mafiya yawansu masu yin imani da su ne
فَٱلۡيَوۡمَ لَا يَمۡلِكُ بَعۡضُكُمۡ لِبَعۡضٖ نَّفۡعٗا وَلَا ضَرّٗا وَنَقُولُ لِلَّذِينَ ظَلَمُواْ ذُوقُواْ عَذَابَ ٱلنَّارِ ٱلَّتِي كُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ
(Sai Allah Ya ce): “To yau shashinku ba zai mallaki amfani ga wani sashi ba ko cutarwa,” za kuma Mu ce da waxanda suka kafirta: “Ku xanxani azabar wutar da kuka kasance kuna qaryata ta.”
وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ قَالُواْ مَا هَٰذَآ إِلَّا رَجُلٞ يُرِيدُ أَن يَصُدَّكُمۡ عَمَّا كَانَ يَعۡبُدُ ءَابَآؤُكُمۡ وَقَالُواْ مَا هَٰذَآ إِلَّآ إِفۡكٞ مُّفۡتَرٗىۚ وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لِلۡحَقِّ لَمَّا جَآءَهُمۡ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ مُّبِينٞ
Idan kuma ana karanta musu ayoyinmu mabayyana sai su ce: “Wannan ai ba wani ba ne sai wani mutum da yake nufin ya hana ku (bauta wa) abin da iyayenku suka kasance suna bauta wa.” Suka kuma ce: “Wannan ai ba wani abu ba ne in ban da qarya da aka qirqira.” Waxanda kuma suka kafirta suka ce game da gaskiya yayin da ta zo musu: “Wannan ba wani abu ba ne sai sihiri mabayyani.”
وَمَآ ءَاتَيۡنَٰهُم مِّن كُتُبٖ يَدۡرُسُونَهَاۖ وَمَآ أَرۡسَلۡنَآ إِلَيۡهِمۡ قَبۡلَكَ مِن نَّذِيرٖ
Kuma ba Mu kawo musu wasu littattafai da suke karantawa ba, kuma ba Mu aiko musu da wani mai gargaxi ba gabaninka
وَكَذَّبَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ وَمَا بَلَغُواْ مِعۡشَارَ مَآ ءَاتَيۡنَٰهُمۡ فَكَذَّبُواْ رُسُلِيۖ فَكَيۡفَ كَانَ نَكِيرِ
Kuma waxanda suka gabace su sun qaryata (annabawa; kafiran Makka) kuwa ba su kai ushurin abin da Muka ba su ba, to su ma sun qaryata manzannina; to yaya tsawatarwata ta kasance (gare su)?
۞قُلۡ إِنَّمَآ أَعِظُكُم بِوَٰحِدَةٍۖ أَن تَقُومُواْ لِلَّهِ مَثۡنَىٰ وَفُرَٰدَىٰ ثُمَّ تَتَفَكَّرُواْۚ مَا بِصَاحِبِكُم مِّن جِنَّةٍۚ إِنۡ هُوَ إِلَّا نَذِيرٞ لَّكُم بَيۡنَ يَدَيۡ عَذَابٖ شَدِيدٖ
Ka ce: “Ni dai kawai ina yi muku wa’azi ne da abu xaya; cewa ku tsaya don Allah; bibbiyu da kuma xai-xai, sannan ku yi tunani. Ba wata hauka tare da mutuminku, shi ba wani ne ba, sai mai yi muku gargaxin azaba mai tsanani da take gabanku.”
قُلۡ مَا سَأَلۡتُكُم مِّنۡ أَجۡرٖ فَهُوَ لَكُمۡۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَى ٱللَّهِۖ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٞ
Ka ce: “Abin da na tambaye ku na wani lada to naku ne[1]; ladana yana wajen Allah kawai; kuma Shi Mai shaida ne a kan komai.”
1- Watau ko da kuwa a ce ya nemi su bayar da wani lada a kan hakan, to ladan nasu ne, ba nasa ba ne, shi sakamakonsa yana wajen Allah shi kaxai.