Surah: Suratul Adiyat

Ayah : 7

وَإِنَّهُۥ عَلَىٰ ذَٰلِكَ لَشَهِيدٞ

Lalle kuma shi shaida ne a kan haka



Surah: Suratul Adiyat

Ayah : 8

وَإِنَّهُۥ لِحُبِّ ٱلۡخَيۡرِ لَشَدِيدٌ

Lalle shi kuma mai tsananin son alheri ne[1]


1- Watau yana da tsananin son dukiya, wannan ne kuma yake sanya shi rowa.


Surah: Suratul Adiyat

Ayah : 9

۞أَفَلَا يَعۡلَمُ إِذَا بُعۡثِرَ مَا فِي ٱلۡقُبُورِ

Shin bai sani ba ne idan aka bankaxo abubuwan da suke cikin qaburbura?



Surah: Suratul Adiyat

Ayah : 10

وَحُصِّلَ مَا فِي ٱلصُّدُورِ

Aka kuma tattaro abubuwan da suke cikin qiraza?



Surah: Suratul Adiyat

Ayah : 11

إِنَّ رَبَّهُم بِهِمۡ يَوۡمَئِذٖ لَّخَبِيرُۢ

Lalle a wannan ranar tabbas Ubangijinsu Masani ne game da su



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 1

ٱلۡقَارِعَةُ

Mai qwanqwasa (zukata da tsoro)



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 2

مَا ٱلۡقَارِعَةُ

Mece ce mai qwanqwsa (zukata da tsoro)?



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 3

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡقَارِعَةُ

Kuma me ya sanar da kai mece ce mai qwanqwasa (zukata da tsoro)?



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 4

يَوۡمَ يَكُونُ ٱلنَّاسُ كَٱلۡفَرَاشِ ٱلۡمَبۡثُوثِ

(Ita ce) ranar da mutane za su zama kamar xangon fari masu bazuwa



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 5

وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ ٱلۡمَنفُوشِ

Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga[1]


1- Watau saboda rashin nauyinsu da warwatsuwarsu a cikin sararin sama.


Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 6

فَأَمَّا مَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ

To amma wanda ma’aunan ayyukansa suka yi nauyi



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 7

فَهُوَ فِي عِيشَةٖ رَّاضِيَةٖ

To shi kam yana cikin rayuwa mai gamsarwa



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 8

وَأَمَّا مَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ

Amma kuma duk wanda ma’aunan ayyukansa suka yi shafal



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 9

فَأُمُّهُۥ هَاوِيَةٞ

To shi makomarsa (wutar) Hawiya ce



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 10

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا هِيَهۡ

Kuma me ya sanar da kai mece ce ita?



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 11

نَارٌ حَامِيَةُۢ

Wuta ce mai tsananin zafi



Surah: Suratut Takasur

Ayah : 1

أَلۡهَىٰكُمُ ٱلتَّكَاثُرُ

Alfahari da yawan (‘ya’ya da dukiya) ya shagaltar da ku[1]


1- Watau su xauke musu hankali har su kai ga barin xa’ar Allah.


Surah: Suratut Takasur

Ayah : 2

حَتَّىٰ زُرۡتُمُ ٱلۡمَقَابِرَ

Har kuka (mutu kuka) ziyarci qaburbura



Surah: Suratut Takasur

Ayah : 3

كَلَّا سَوۡفَ تَعۡلَمُونَ

A’aha! (haka bai kamace ku ba) da sannu za ku sani



Surah: Suratut Takasur

Ayah : 4

ثُمَّ كَلَّا سَوۡفَ تَعۡلَمُونَ

Sannan a’aha, da sannu za ku sani



Surah: Suratut Takasur

Ayah : 5

كَلَّا لَوۡ تَعۡلَمُونَ عِلۡمَ ٱلۡيَقِينِ

Tabbas da za ku yi sani, sani na sakankancewa[1]


1- Watau wanda babu kokwanto ko kaxan a cikinsa.


Surah: Suratut Takasur

Ayah : 6

لَتَرَوُنَّ ٱلۡجَحِيمَ

Tabbas haqiqa za ku ga wutar Jahimu



Surah: Suratut Takasur

Ayah : 7

ثُمَّ لَتَرَوُنَّهَا عَيۡنَ ٱلۡيَقِينِ

Sannan tabbas haqiqa za ku gan ta gani da ido na sakankancewa



Surah: Suratut Takasur

Ayah : 8

ثُمَّ لَتُسۡـَٔلُنَّ يَوۡمَئِذٍ عَنِ ٱلنَّعِيمِ

Sannan kuma tabbas lalle za a tambaye ku a wannan ranar game da ni’imomin (da kuka mora a duniya)



Surah: Suratul Asr

Ayah : 1

وَٱلۡعَصۡرِ

Na rantse da zamani[1]


1- Wannan ya qunshi dare da rana waxanda su ne mahallin dukkan ayyukan bayi.


Surah: Suratul Asr

Ayah : 2

إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَفِي خُسۡرٍ

Lalle mutum yana cikin asara



Surah: Suratul Asr

Ayah : 3

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡحَقِّ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ

Sai dai waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, suka kuma yi wa juna wasiyya da gaskiya, suka kuma yi wa juna wasiyya da haquri



Surah: Suratul Humaza

Ayah : 1

وَيۡلٞ لِّكُلِّ هُمَزَةٖ لُّمَزَةٍ

Tsananin azaba ya tabbata ga duk wani mai yawan qyafice mai yawan suka[1]


1- Watau yawan qyafice ga mutane, yana kuma yawan sukan su da aibata su a bayan idanuwansu..


Surah: Suratul Humaza

Ayah : 2

ٱلَّذِي جَمَعَ مَالٗا وَعَدَّدَهُۥ

Wanda ya tara dukiya ya qididdige ta



Surah: Suratul Humaza

Ayah : 3

يَحۡسَبُ أَنَّ مَالَهُۥٓ أَخۡلَدَهُۥ

Yana zaton cewa dukiyarsa za ta dawwamar da shi