فَلۡيَدۡعُ نَادِيَهُۥ
To ya kirawo majalisar tasa
سَنَدۡعُ ٱلزَّبَانِيَةَ
Mu kuma lalle za Mu kirawo (mala’iku) zabaniyawa
كَلَّا لَا تُطِعۡهُ وَٱسۡجُدۡۤ وَٱقۡتَرِب۩
Faufau! Kada ka bi shi, ka kuma yi salla, ka kusanta (ga Allah)
إِنَّآ أَنزَلۡنَٰهُ فِي لَيۡلَةِ ٱلۡقَدۡرِ
Lalle Mu Muka saukar da shi (Alqur’ani) a daren Lailatul-Qadari[1] (dare mai daraja)
1- Watau lokacin da aka fara saukar da jumullarsa a sama ta kusa, kamar yadda a cikin watan Ramadana ne ake fara saukar da shi ga Manzon Allah () a kogon Hira.
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا لَيۡلَةُ ٱلۡقَدۡرِ
Mene ne ya sanar da kai mece ce Lailatul-Qadari?
لَيۡلَةُ ٱلۡقَدۡرِ خَيۡرٞ مِّنۡ أَلۡفِ شَهۡرٖ
(Daren) Lailatul-Qadari ya fi wata dubu alheri
تَنَزَّلُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ فِيهَا بِإِذۡنِ رَبِّهِم مِّن كُلِّ أَمۡرٖ
Mala’iku da Jibrilu suna ta saukowa da dukkanin al’amura a cikinsa da izinin Ubangijinsu
سَلَٰمٌ هِيَ حَتَّىٰ مَطۡلَعِ ٱلۡفَجۡرِ
Aminci ne shi (daren dukkansa) har zuwa hudowar alfijir
لَمۡ يَكُنِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ مُنفَكِّينَ حَتَّىٰ تَأۡتِيَهُمُ ٱلۡبَيِّنَةُ
Waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushirikai ba su zamanto masu barin abin da suke kai (na kafirci) ba har sai hujja bayyananniya ta zo musu
رَسُولٞ مِّنَ ٱللَّهِ يَتۡلُواْ صُحُفٗا مُّطَهَّرَةٗ
(Watau) Manzo daga Allah da zai riqa karanta (musu) takardu masu tsarki
فِيهَا كُتُبٞ قَيِّمَةٞ
(Waxanda) a cikinsu akwai hukunce-hukunce masu qima
وَمَا تَفَرَّقَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَتۡهُمُ ٱلۡبَيِّنَةُ
Waxanda kuma aka bai wa littafi ba su rarraba ba[1] sai bayan da hujja bayyananniya ta zo musu
1- Watau Yahudawa da Nasara ba su rarrabu ba suka zama qungiya-qungiya wasu suka yi imani da Manzo Allah (), wasu kuma suka kafirce.
وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ حُنَفَآءَ وَيُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤۡتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَذَٰلِكَ دِينُ ٱلۡقَيِّمَةِ
Ba a kuma umarce su ba sai don su bauta wa Allah suna masu tsantsanta addini gare Shi, suna masu kauce wa varna, suna kuma tsayar da salla, kuma suna ba da zakka. Wannan kuwa shi ne addinin miqaqqiyar hanya
إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ فِي نَارِ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَآۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمۡ شَرُّ ٱلۡبَرِيَّةِ
Lalle waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushirikai suna cikin wutar Jahannama suna madawwama a cikinta. Waxannan su ne mafiya sharrin halitta
إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمۡ خَيۡرُ ٱلۡبَرِيَّةِ
Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, waxannan su ne mafiya alherin halitta
جَزَآؤُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتُ عَدۡنٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدٗاۖ رَّضِيَ ٱللَّهُ عَنۡهُمۡ وَرَضُواْ عَنۡهُۚ ذَٰلِكَ لِمَنۡ خَشِيَ رَبَّهُۥ
Sakamakonsu a wajen Ubangijinsu gidajen Aljanna ne na dawwama waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu suna madawwama a cikinsu har abada; Allah Ya yarda da su, su ma sun yarda da Shi. Wannan kuma (sakamako ne) ga wanda ya ji tsoron Ubangijinsa
إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا
Idan aka girgiza qasa matuqar girgiza ta
وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا
Qasar kuma ta fitar da nauyaye-nauyayenta[1]
1- Watau ta fitar da mutanen da ke cikinta da sauran ma’adanan qarqashinta.
وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا
Mutum kuma ya ce: “Me ya same ta?”
يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا
A wannan ranar ne za ta ba da labaranta[1]
1- Watau ayyukan da aka yi a kanta masu kyau da munana.
بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا
Don Ubangijinka Ya umarce ta (da yin haka)
يَوۡمَئِذٖ يَصۡدُرُ ٱلنَّاسُ أَشۡتَاتٗا لِّيُرَوۡاْ أَعۡمَٰلَهُمۡ
A wannan ranar mutane za su fito a warwatse, don a nuna musu ayyukansu
فَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٍ خَيۡرٗا يَرَهُۥ
To duk wanda ya yi aikin alheri daidai da zarra zai gan shi
وَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ شَرّٗا يَرَهُۥ
Wanda kuma duk ya yi aikin sharri daidai da zarra zai gan shi
وَٱلۡعَٰدِيَٰتِ ضَبۡحٗا
Na rantse da (dawaki) masu sukuwa suna kukan ciki
فَٱلۡمُورِيَٰتِ قَدۡحٗا
Sannan masu bugun qyastu da kofatai[1]
1- Watau suna qyasta wuta da kofatansu idan suka daki duwatsu da su.
فَٱلۡمُغِيرَٰتِ صُبۡحٗا
Sannan masu kai hari da asuba
فَأَثَرۡنَ بِهِۦ نَقۡعٗا
Sai suka tayar da qura da ita (sukawar tasu)
فَوَسَطۡنَ بِهِۦ جَمۡعًا
Sai kuma suka shiga tsakiyar taro (da mahayansu)
إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لِرَبِّهِۦ لَكَنُودٞ
Lalle mutum tabbas mai yawan butulci ne ga Ubangijinsa