وَهَدَيۡنَٰهُ ٱلنَّجۡدَيۡنِ
Muka kuma bayyana masa hanyoyi biyu[1]?
1- Watau hanyar alheri da hanyar sharri.
Share :
فَلَا ٱقۡتَحَمَ ٱلۡعَقَبَةَ
Sai bai qetare hanya mai wahala[1] ba?
1- Watau hanyar da ta raba tsakaninsa da gidan Aljanna.
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡعَقَبَةُ
Me kuma ya sanar da kai mece ce hanya mai wahala?
فَكُّ رَقَبَةٍ
(Watau) ‘yanta wuyaye (bawa ko baiwa)
أَوۡ إِطۡعَٰمٞ فِي يَوۡمٖ ذِي مَسۡغَبَةٖ
Ko kuma ciyarwa a wata rana ta yunwa
يَتِيمٗا ذَا مَقۡرَبَةٍ
Ga maraya ma’abocin kusanci
أَوۡ مِسۡكِينٗا ذَا مَتۡرَبَةٖ
Ko miskini ma’abocin talauci
ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡمَرۡحَمَةِ
Sannan kuma ya zama daga waxanda suka yi imani, suka yi wa junansu wasiyya da yin haquri kuma suka yi wa juna wasiyya da tausayawa
أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ
Waxannan su ne ma’abota dama[1]
1- Watau ‘yan Aljanna.
وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِنَا هُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ
Waxanda kuwa suka kafirce wa ayoyinmu, su ne ma’abota hagu[1]
1- Watau ‘yan wuta.
عَلَيۡهِمۡ نَارٞ مُّؤۡصَدَةُۢ
A kansu akwai wuta abar kullewa
وَٱلشَّمۡسِ وَضُحَىٰهَا
Na rantse da rana da walaharta
وَٱلۡقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا
Da kuma wata idan ya bi ta (wato ranar)[1]
1- Watau ya biyo bayan faxuwar rana.
وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا
Da kuma wuni idan ya bayyana ta
وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰهَا
Da kuma dare idan ya lulluve ta
وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا
Da kuma sama da gininta
وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا طَحَىٰهَا
Da kuma qasa da shimfixarta
وَنَفۡسٖ وَمَا سَوَّىٰهَا
Da kuma rai da daidaitarsa
فَأَلۡهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقۡوَىٰهَا
Sai Ya kimsa masa (gane) lalacewarsa da taqawarsa
قَدۡ أَفۡلَحَ مَن زَكَّىٰهَا
Haqiqa wanda ya tsarkake shi (ran) ya rabauta
وَقَدۡ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا
Haqiqa kuma wanda ya binne shi da savo ya tave
كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِطَغۡوَىٰهَآ
Samudawa sun qaryata saboda xagawarsu
إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشۡقَىٰهَا
Yayin da mafi tsagerancinsu ya zabura
فَقَالَ لَهُمۡ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقۡيَٰهَا
Sai Manzon Allah[1] ya ce da su: “Ku bar taguwar Allah da (ranar) shanta.”
1- Watau Annabi Salihu ().
فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمۡدَمَ عَلَيۡهِمۡ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمۡ فَسَوَّىٰهَا
Sai suka qaryata shi sannan suka soke ta, sai Ubangijinsu Ya kama su da azaba saboda zunubinsu, sai Ya daidaita ta (watau qabilar wajen azaba)
وَلَا يَخَافُ عُقۡبَٰهَا
Kuma ba Ya tsoron abin da zai biyo bayanta[1]
1- Watau ba ya jin tsoron wani abu da hallaka su za ta haifar nan gaba.
وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰ
Na rantse da dare idan ya lulluve (da duhunsa)
وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ
Da kuma wuni idan ya bayyana
وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ
Da kuma halittar namiji da mace
إِنَّ سَعۡيَكُمۡ لَشَتَّىٰ
Lalle aikinku ya sha bamban