Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 6

لَّيۡسَ لَهُمۡ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٖ

Ba su da wani abinci sai na qayar tsidau



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 7

لَّا يُسۡمِنُ وَلَا يُغۡنِي مِن جُوعٖ

Ba ya sa qiba kuma ba ya maganin yunwa



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 8

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ نَّاعِمَةٞ

Waxansu fuskokin kuwa a wannan ranar ni’imtattu ne



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 9

لِّسَعۡيِهَا رَاضِيَةٞ

Masu gamsuwa ne da (sakamakon) ayyukansu



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 10

فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٖ

(Suna) cikin Aljanna maxaukakiya[1]


1- Watau xaukaka ta daraja da xaukaka ta muhalli, domin gidajen Aljanna benaye ne wasu kan wasu.


Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 11

لَّا تَسۡمَعُ فِيهَا لَٰغِيَةٗ

Ba a jin zancen banza a cikinta



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 12

فِيهَا عَيۡنٞ جَارِيَةٞ

A cikinta akwai marmaro mai gudana



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 13

فِيهَا سُرُرٞ مَّرۡفُوعَةٞ

A cikinta akwai gadaje maxaukaka



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 14

وَأَكۡوَابٞ مَّوۡضُوعَةٞ

Da kofuna a ajijjiye



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 15

وَنَمَارِقُ مَصۡفُوفَةٞ

Da matasan kai a jejjere



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 16

وَزَرَابِيُّ مَبۡثُوثَةٌ

Da dardumai a shisshimfixe



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 17

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلۡإِبِلِ كَيۡفَ خُلِقَتۡ

Shin ba sa duban raqumi yadda aka halicce shi?



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 18

وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيۡفَ رُفِعَتۡ

Da kuma sama yadda aka xaga ta?



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 19

وَإِلَى ٱلۡجِبَالِ كَيۡفَ نُصِبَتۡ

Da kuma duwatsu yadda aka kakkafa su?



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 20

وَإِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَيۡفَ سُطِحَتۡ

Da kuma qasa yadda aka shimfixa ta?



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 21

فَذَكِّرۡ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٞ

To ka yi wa’azi, lalle kai mai wa’azi ne kawai



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 22

لَّسۡتَ عَلَيۡهِم بِمُصَيۡطِرٍ

Kai ba mai tilasta su ba ne



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 23

إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ

Sai dai wanda ya ba da baya ya kuma kafirce



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 24

فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَكۡبَرَ

To Allah zai azabtar da shi azaba mafi girma[1]


1- Watau wutar Jahannama inda zai dawwama a cikinta har abada.


Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 25

إِنَّ إِلَيۡنَآ إِيَابَهُمۡ

Lalle zuwa gare Mu ne makomarsu take



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 26

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا حِسَابَهُم

Sannan kuma a kanmu ne hisabinsu yake



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 1

وَٱلۡفَجۡرِ

Na rantse da alfijir



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 2

وَلَيَالٍ عَشۡرٖ

Da kuma darare goma[1]


1- Watau kwanaki goma na farkon watan Zulhijja.


Surah: Suratul Fajr

Ayah : 3

وَٱلشَّفۡعِ وَٱلۡوَتۡرِ

Da kuma abin da yake cika[1] da kuma mara[2]


1- Watau bibbiyu ko hurhuxu ko shida-shida da sauransu.


2- Watau xaya ko uku ko biyar da sauransu.


Surah: Suratul Fajr

Ayah : 4

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَسۡرِ

Da kuma dare lokacin da yake tafiya (cikin duhu)



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 5

هَلۡ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٞ لِّذِي حِجۡرٍ

Shin a game da waxannan akwai rantsuwa (mai gamsarwa) ga mai hankali[1]?


1- Watau duk mai hankali zai gamsu da waxannan rantse-rantse.


Surah: Suratul Fajr

Ayah : 6

أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ

Shin ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ba ga Adawa?



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 7

إِرَمَ ذَاتِ ٱلۡعِمَادِ

(Watau qabilar) Iramu ma’abociyar tsawo



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 8

ٱلَّتِي لَمۡ يُخۡلَقۡ مِثۡلُهَا فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Wadda ba a halicci irinta ba a cikin garuruwa (a tsananin qarfi)



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 9

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُواْ ٱلصَّخۡرَ بِٱلۡوَادِ

Da kuma Samudawa waxanda suka fafe duwatsu a wurin da ake kira Wadil-Qura