Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 47

حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلۡيَقِينُ

“Har mutuwa ta zo mana.”



Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 48

فَمَا تَنفَعُهُمۡ شَفَٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ

Saboda haka ceton masu ceto ba zai amfane su ba



Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 49

فَمَا لَهُمۡ عَنِ ٱلتَّذۡكِرَةِ مُعۡرِضِينَ

To me ya same su ne suke bijire wa wa’azi?



Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 50

كَأَنَّهُمۡ حُمُرٞ مُّسۡتَنفِرَةٞ

Kai ka ce su jakunan jeji ne da aka firgitar



Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 51

فَرَّتۡ مِن قَسۡوَرَةِۭ

Da suka guje wa zaki



Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 52

بَلۡ يُرِيدُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُؤۡتَىٰ صُحُفٗا مُّنَشَّرَةٗ

A’a, kowane mutum daga cikinsu yana so ne a ba shi takardu buxaxxu[1] (kafin su bi Annabi)


1- Watau a ba shi buxaxxen littafi wanda zai ba shi labari cewa Annabi Muhammadu () Manzon Allah ne.


Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 53

كَلَّاۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ

Faufau! A’a, su dai ba sa tsoron ranar lahira ne



Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 54

كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذۡكِرَةٞ

Tabbas, lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne



Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 55

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

To duk wanda ya ga dama sai ya wa’azantu



Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 56

وَمَا يَذۡكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ هُوَ أَهۡلُ ٱلتَّقۡوَىٰ وَأَهۡلُ ٱلۡمَغۡفِرَةِ

Ba sa kuma wa’azantuwa sai idan Allah Ya ga dama. Shi ne Ya cancanci taqawa, kuma Shi ne Ya cancanci yin gafara



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 1

لَآ أُقۡسِمُ بِيَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ

Ina rantsuwa da ranar alqiyama



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 2

وَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلنَّفۡسِ ٱللَّوَّامَةِ

Ina kuma rantsuwa da rai mai yawan zargin (kansa)[1]


1- Watau a kan gazawarsa wajen ayyukan alheri ko a kan aikata laifuka.


Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 3

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ

Yanzu mutum yana tsammanin ba za Mu tattara qasusuwansa ba?



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 4

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ

E, (Mu) Masu iko ne a kan Mu daidaita gavovin yatsunsa



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 5

بَلۡ يُرِيدُ ٱلۡإِنسَٰنُ لِيَفۡجُرَ أَمَامَهُۥ

Ba haka ba ne, mutum yana nufi ne kawai ya gurvata gabansa (da savon Allah)



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 6

يَسۡـَٔلُ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلۡقِيَٰمَةِ

Yana tambaya yaushe ne ranar alqiyamar?



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 7

فَإِذَا بَرِقَ ٱلۡبَصَرُ

To lokacin da gani ya ruxe



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 8

وَخَسَفَ ٱلۡقَمَرُ

Wata kuma ya yi duhu



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 9

وَجُمِعَ ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ

Aka kuma haxe rana da wata (a mafitarsu)



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 10

يَقُولُ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذٍ أَيۡنَ ٱلۡمَفَرُّ

A wannan rana ne mutum zai ce: “Ina wurin gudu?”



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 11

كَلَّا لَا وَزَرَ

Faufau, babu mafaka



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 12

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمُسۡتَقَرُّ

Zuwa ga Ubangijinka ne kawai matabbata take a wannan rana



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 13

يُنَبَّؤُاْ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذِۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ

Za a bai wa mutum labari a wannan rana na abin da ya gabatar da kuma (abin da) ya jinkirtar (na ayyukansa)



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 14

بَلِ ٱلۡإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ بَصِيرَةٞ

A’a, shi dai mutum mai shaida ne a kan kansa



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 15

وَلَوۡ أَلۡقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ

Ko da kuwa ya kawo uzururrukansa



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 16

لَا تُحَرِّكۡ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعۡجَلَ بِهِۦٓ

(Allah ya ce da Annabinsa): Kada ka motsa harshenka da shi (Alqur’ani) don gaggauta (karanta) shi



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 17

إِنَّ عَلَيۡنَا جَمۡعَهُۥ وَقُرۡءَانَهُۥ

Lalle tattara shi (a zuciyarka) da karanta shi yana kanmu



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 18

فَإِذَا قَرَأۡنَٰهُ فَٱتَّبِعۡ قُرۡءَانَهُۥ

Saboda haka idan Muka karanta (maka) shi sai ka bi karatunsa



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 19

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا بَيَانَهُۥ

Sannan kuma bayaninsa yana kanmu



Surah: Suratul Qiyama

Ayah : 20

كَلَّا بَلۡ تُحِبُّونَ ٱلۡعَاجِلَةَ

Haba, ku dai kawai kuna son duniya ne