Surah: Suratux Xariq

Ayah : 12

وَٱلۡأَرۡضِ ذَاتِ ٱلصَّدۡعِ

Da kuma qasa ma’abociyar tsagewa (shuka ta fito)



Surah: Suratux Xariq

Ayah : 13

إِنَّهُۥ لَقَوۡلٞ فَصۡلٞ

Lalle shi (Alqur’ani) magana ce mai tsage gaskiya



Surah: Suratux Xariq

Ayah : 14

وَمَا هُوَ بِٱلۡهَزۡلِ

Kuma shi ba zancen banza ba ne



Surah: Suratux Xariq

Ayah : 15

إِنَّهُمۡ يَكِيدُونَ كَيۡدٗا

Lalle su (kafirai) suna qulla mummunan makirci



Surah: Suratux Xariq

Ayah : 16

وَأَكِيدُ كَيۡدٗا

Ni kuma ina shirya musu mummunan sakamako



Surah: Suratux Xariq

Ayah : 17

فَمَهِّلِ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَمۡهِلۡهُمۡ رُوَيۡدَۢا

To sai ka saurara wa kafirai, ka saurara musu kaxan



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 1

سَبِّحِ ٱسۡمَ رَبِّكَ ٱلۡأَعۡلَى

Ka tsarkake sunan Ubangijinka Mafi xaukaka



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 2

ٱلَّذِي خَلَقَ فَسَوَّىٰ

Wanda Ya yi halitta sai Ya daidaita (ta)



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 3

وَٱلَّذِي قَدَّرَ فَهَدَىٰ

Wanda kuma Ya qaddara (abubuwa) sannan Ya shiryar (da halittarsa)



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 4

وَٱلَّذِيٓ أَخۡرَجَ ٱلۡمَرۡعَىٰ

Wanda kuma Ya fitar da makiyaya



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 5

فَجَعَلَهُۥ غُثَآءً أَحۡوَىٰ

Sai Ya mayar da ita duddugaggiya mai baqi



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 6

سَنُقۡرِئُكَ فَلَا تَنسَىٰٓ

Za Mu karantar da kai (Alqur’ani) don haka ba za ka manta ba



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 7

إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلۡجَهۡرَ وَمَا يَخۡفَىٰ

Sai abin da Allah Ya ga dama, Lalle Shi Yana sane da bayyanannen (abu) da kuma abin da yake vuya



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 8

وَنُيَسِّرُكَ لِلۡيُسۡرَىٰ

Kuma za Mu sauqaqe maka (al’umara) mafiya sauqi[1]


1- Watau al’ummuransa na addini da na rayuwa, domin ya sa damar da saqon Allah a cikin nutsuwa.


Surah: Suratul A’ala

Ayah : 9

فَذَكِّرۡ إِن نَّفَعَتِ ٱلذِّكۡرَىٰ

To ka yi wa’azi idan wa’azin zai yi amfani



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 10

سَيَذَّكَّرُ مَن يَخۡشَىٰ

Wanda yake tsoron Allah zai wa’azantu



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 11

وَيَتَجَنَّبُهَا ٱلۡأَشۡقَى

Mafi shaqiyanci[1] kuma zai nesance shi


1- Watau kafiri tavavve.


Surah: Suratul A’ala

Ayah : 12

ٱلَّذِي يَصۡلَى ٱلنَّارَ ٱلۡكُبۡرَىٰ

Wanda zai shiga wuta mafi girma



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 13

ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحۡيَىٰ

Sannan ba zai mutu a cikinta ba kuma ba zai rayu (rayuwa mai daxi) ba



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 14

قَدۡ أَفۡلَحَ مَن تَزَكَّىٰ

Haqiqa wanda ya tsarkaka ya rabauta



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 15

وَذَكَرَ ٱسۡمَ رَبِّهِۦ فَصَلَّىٰ

Ya kuma ambaci sunan Ubangijinsa sannan ya yi salla



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 16

بَلۡ تُؤۡثِرُونَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا

Ba haka ba, ku dai kuna fifita rayuwar duniya ne



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 17

وَٱلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ وَأَبۡقَىٰٓ

Lahira kuwa ita ta fi alheri ta kuma fi wanzuwa



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 18

إِنَّ هَٰذَا لَفِي ٱلصُّحُفِ ٱلۡأُولَىٰ

Lalle wannan (batu) tabbas yana cikin littattafan farko



Surah: Suratul A’ala

Ayah : 19

صُحُفِ إِبۡرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ

Littattafan Ibrahimu da Musa



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 1

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلۡغَٰشِيَةِ

Shin labarin mai lulluvewa da (tsoro) ya zo maka?



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 2

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ خَٰشِعَةٌ

Wasu fuskoki a wannan ranar qasqantattu ne



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 3

عَامِلَةٞ نَّاصِبَةٞ

Masu aiki ne (tuquru)[1] masu shan wahala


1- Watau a wutar Jahannama.


Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 4

تَصۡلَىٰ نَارًا حَامِيَةٗ

Za su shiga wuta mai tsananin quna



Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 5

تُسۡقَىٰ مِنۡ عَيۡنٍ ءَانِيَةٖ

Za a shayar da su daga idon ruwa mai tsananin zafi