Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 214

وَأَنذِرۡ عَشِيرَتَكَ ٱلۡأَقۡرَبِينَ

Kuma ka gargaxi danginka mafiya kusanci



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 215

وَٱخۡفِضۡ جَنَاحَكَ لِمَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Ka kuma tausasa ga wanda ya bi ka daga muminai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 216

فَإِنۡ عَصَوۡكَ فَقُلۡ إِنِّي بَرِيٓءٞ مِّمَّا تَعۡمَلُونَ

To idan suka sava maka sai ka ce: “Ni lalle ba ruwana da abin da kuke aikatawa.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 217

وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱلۡعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ

Ka kuma dogara ga Mabuwayi, Mai rahama



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 218

ٱلَّذِي يَرَىٰكَ حِينَ تَقُومُ

Wanda Yake ganin ka yayin da kake tashi (don yin salla)



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 219

وَتَقَلُّبَكَ فِي ٱلسَّـٰجِدِينَ

Da kuma (yayin) jujjuyawarka cikin masu sujjada[1]


1- Watau masallata a sallar jam’i.


Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 220

إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Haqiqa Shi Mai ji ne, Masani



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 221

هَلۡ أُنَبِّئُكُمۡ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ ٱلشَّيَٰطِينُ

Shin ba Na ba ku labari ba game da wanda shexanu suke saukar masa?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 222

تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٖ

Suna sauka ne a kan duk wani maqaryaci mai yawan laifi



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 223

يُلۡقُونَ ٱلسَّمۡعَ وَأَكۡثَرُهُمۡ كَٰذِبُونَ

Suna jefa wa (bokaye) abin da suka sato jinsa, yawancinsu kuwa maqaryata ne



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 224

وَٱلشُّعَرَآءُ يَتَّبِعُهُمُ ٱلۡغَاوُۥنَ

Mawaqa kuwa vatattu ne suke bin su



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 225

أَلَمۡ تَرَ أَنَّهُمۡ فِي كُلِّ وَادٖ يَهِيمُونَ

Ba ka ga cewa su kutsawa suke yi cikin kowanne kwari ba[1]?


1- Watau suna kutsawa cikin kowane saqo-saqo na waqe-waqe, wani lokaci ta hanyar yabo, wani lokaci kuma ya hanyar zambo ko alfahari, su faxi qarya da gaskiya.


Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 226

وَأَنَّهُمۡ يَقُولُونَ مَا لَا يَفۡعَلُونَ

Lalle kuma suna faxar abin da ba sa aikatawa



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 227

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَذَكَرُواْ ٱللَّهَ كَثِيرٗا وَٱنتَصَرُواْ مِنۢ بَعۡدِ مَا ظُلِمُواْۗ وَسَيَعۡلَمُ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ أَيَّ مُنقَلَبٖ يَنقَلِبُونَ

Sai dai waxanda suka yi imani kuma suka yi aiki nagari, kuma suka ambaci Allah da yawa, suka kuma yi sakayya bayan an zalunce su[1]. Waxanda suka yi zalunci kuwa ba da daxewa ba za su san kowace makomar za su koma


1- Watau mawaqan Musulmi waxanda suke mayar da martani a kan mawaqan kafirai masu sukan Musulunci.


Surah: Suratun Namli

Ayah : 1

طسٓۚ تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡقُرۡءَانِ وَكِتَابٖ مُّبِينٍ

XA SIN[1]. Waxannan ayoyin Alqur’ani ne kuma Littafi mabayyani


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Surah: Suratun Namli

Ayah : 2

هُدٗى وَبُشۡرَىٰ لِلۡمُؤۡمِنِينَ

(Kuma) shiriya da albishir ne ga muminai



Surah: Suratun Namli

Ayah : 3

ٱلَّذِينَ يُقِيمُونَ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤۡتُونَ ٱلزَّكَوٰةَ وَهُم بِٱلۡأٓخِرَةِ هُمۡ يُوقِنُونَ

Waxanda suke tsai da salla, suke kuma ba da zakka suna masu sakankancewa da ranar lahira



Surah: Suratun Namli

Ayah : 4

إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ زَيَّنَّا لَهُمۡ أَعۡمَٰلَهُمۡ فَهُمۡ يَعۡمَهُونَ

Lalle waxanda ba sa imani da ranar lahira Mun qawata musu ayyukansu, don haka suke ximuwa



Surah: Suratun Namli

Ayah : 5

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ لَهُمۡ سُوٓءُ ٱلۡعَذَابِ وَهُمۡ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ هُمُ ٱلۡأَخۡسَرُونَ

Waxannan su ne waxanda suke da mummunar azaba, kuma su ne suka fi hasara a lahira



Surah: Suratun Namli

Ayah : 6

وَإِنَّكَ لَتُلَقَّى ٱلۡقُرۡءَانَ مِن لَّدُنۡ حَكِيمٍ عَلِيمٍ

Lalle kuma kai tabbas ana yi maka wahayin Alqur’ani ne daga wajen (Allah) Mai hikima, Masani



Surah: Suratun Namli

Ayah : 7

إِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِأَهۡلِهِۦٓ إِنِّيٓ ءَانَسۡتُ نَارٗا سَـَٔاتِيكُم مِّنۡهَا بِخَبَرٍ أَوۡ ءَاتِيكُم بِشِهَابٖ قَبَسٖ لَّعَلَّكُمۡ تَصۡطَلُونَ

Ka tuna lokacin da Musa ya ce da iyalinsa: “Lalle ni na hango wata wuta, to (zan je) in zo muku da labari, ko kuma in zo muku da xosanen garwashi don ku ji xumi.”



Surah: Suratun Namli

Ayah : 8

فَلَمَّا جَآءَهَا نُودِيَ أَنۢ بُورِكَ مَن فِي ٱلنَّارِ وَمَنۡ حَوۡلَهَا وَسُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

To lokacin da ya zo mata (wutar) sai aka kira shi cewa, an tsarkake wanda yake cikin wutar da waxanda suke daura da ita (wato mala’iku), kuma tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai



Surah: Suratun Namli

Ayah : 9

يَٰمُوسَىٰٓ إِنَّهُۥٓ أَنَا ٱللَّهُ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Ya Musa, lalle lamarin dai, Ni ne Allah Mabuwayi, Mai hikima



Surah: Suratun Namli

Ayah : 10

وَأَلۡقِ عَصَاكَۚ فَلَمَّا رَءَاهَا تَهۡتَزُّ كَأَنَّهَا جَآنّٞ وَلَّىٰ مُدۡبِرٗا وَلَمۡ يُعَقِّبۡۚ يَٰمُوسَىٰ لَا تَخَفۡ إِنِّي لَا يَخَافُ لَدَيَّ ٱلۡمُرۡسَلُونَ

Kuma ka jefar da sandarka. To lokacin da ya gan ta tana jujjuyawa kamar macijiya, sai ya juya da baya a guje bai dawo ba. (Allah ya ce): Ya Musa, kada ka ji tsoro, lalle Ni manzanni ba sa jin tsoro a wurina



Surah: Suratun Namli

Ayah : 11

إِلَّا مَن ظَلَمَ ثُمَّ بَدَّلَ حُسۡنَۢا بَعۡدَ سُوٓءٖ فَإِنِّي غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Sai dai wanda ya zalunci (kansa), sannan ya musanya kyakkyawa bayan mummuna, to lalle Ni Mai gafara ne, Mai jin qai



Surah: Suratun Namli

Ayah : 12

وَأَدۡخِلۡ يَدَكَ فِي جَيۡبِكَ تَخۡرُجۡ بَيۡضَآءَ مِنۡ غَيۡرِ سُوٓءٖۖ فِي تِسۡعِ ءَايَٰتٍ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ وَقَوۡمِهِۦٓۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمٗا فَٰسِقِينَ

Kuma ka saka hannunka cikin wuyan rigarka, zai fito fari fat ba na cuta ba; (wannan aya ce) daga cikin ayoyi tara zuwa ga Fir’auna da mutanensa. Lalle su sun kasance mutane ne fasiqai



Surah: Suratun Namli

Ayah : 13

فَلَمَّا جَآءَتۡهُمۡ ءَايَٰتُنَا مُبۡصِرَةٗ قَالُواْ هَٰذَا سِحۡرٞ مُّبِينٞ

To lokacin da ayoyinmu waxanda suke a sarari suka zo musu, sai suka ce: “Wannan sihiri ne mabayyani.”



Surah: Suratun Namli

Ayah : 14

وَجَحَدُواْ بِهَا وَٱسۡتَيۡقَنَتۡهَآ أَنفُسُهُمۡ ظُلۡمٗا وَعُلُوّٗاۚ فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُفۡسِدِينَ

Suka kuma musanta su don zalunci da girman kai, alhali kuwa zukatansu sun sakankance da su[1]. To sai ka duba ka ga yadda qarshen mavarnata ya kasance


1- Watau a zukatansu sun san gaskiya ce, su kuma a kan qarya suke, amma son zuciya ya hana su su sallama.


Surah: Suratun Namli

Ayah : 15

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا دَاوُۥدَ وَسُلَيۡمَٰنَ عِلۡمٗاۖ وَقَالَا ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِي فَضَّلَنَا عَلَىٰ كَثِيرٖ مِّنۡ عِبَادِهِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Haqiqa kuma Mun bai wa Dawuda da Sulaimana ilimi; suka kuma ce: “Godiya ta tabbata ga Allah wanda Ya fifita mu a kan masu yawa daga bayinsa muminai.”



Surah: Suratun Namli

Ayah : 16

وَوَرِثَ سُلَيۡمَٰنُ دَاوُۥدَۖ وَقَالَ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ عُلِّمۡنَا مَنطِقَ ٱلطَّيۡرِ وَأُوتِينَا مِن كُلِّ شَيۡءٍۖ إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلۡفَضۡلُ ٱلۡمُبِينُ

Sulaimanu kuma ya gaji Dawuda[1]; ya kuma ce: “Ya ku waxannan mutane, (watau Yahudawa), an sanar da mu zancen tsuntsaye, kuma an ba mu daga kowane abu (na tafiyar da mulki); lalle wannan tabbas ita ce bayyananniyar falala.”


1- Watau gadon ilimi da annabta da Allah ya ba shi, kamar yadda kuma ya gaji mulkinsa.