Surah: Suratul Baqara

Ayah : 253

۞تِلۡكَ ٱلرُّسُلُ فَضَّلۡنَا بَعۡضَهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖۘ مِّنۡهُم مَّن كَلَّمَ ٱللَّهُۖ وَرَفَعَ بَعۡضَهُمۡ دَرَجَٰتٖۚ وَءَاتَيۡنَا عِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ ٱلۡبَيِّنَٰتِ وَأَيَّدۡنَٰهُ بِرُوحِ ٱلۡقُدُسِۗ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ مَا ٱقۡتَتَلَ ٱلَّذِينَ مِنۢ بَعۡدِهِم مِّنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَتۡهُمُ ٱلۡبَيِّنَٰتُ وَلَٰكِنِ ٱخۡتَلَفُواْ فَمِنۡهُم مَّنۡ ءَامَنَ وَمِنۡهُم مَّن كَفَرَۚ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ مَا ٱقۡتَتَلُواْ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ يَفۡعَلُ مَا يُرِيدُ

Waxannan manzanni, Mun fifita sashinsu a kan sashi. Cikinsu akwai wanda Allah Ya yi magana da shi, kuma Ya xaukaka wasunsu da darajoji. Kuma Mun bai wa Isa xan Maryam hujjoji bayyanannu, kuma Mun qarfafe shi da Ruhi mai tsarki. Da kuma Allah Ya ga dama da waxanda suka zo bayansu ba su yaqi juna ba bayan hujjoji bayanannu sun zo musu, sai dai kuma sun yi savani; cikinsu akwai wanda ya yi imani, kuma cikinsu akwai wanda ya kafirce, kuma da Allah Ya ga dama da ba su yaqi juna ba, sai dai Allah Yana aikata abin da Yake nufi



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 254

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَنفِقُواْ مِمَّا رَزَقۡنَٰكُم مِّن قَبۡلِ أَن يَأۡتِيَ يَوۡمٞ لَّا بَيۡعٞ فِيهِ وَلَا خُلَّةٞ وَلَا شَفَٰعَةٞۗ وَٱلۡكَٰفِرُونَ هُمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku ciyar daga abin da Muka arzurta ku (da shi) tun kafin wani yini ya zo wanda babu ciniki a cikinsa kuma babu abokantaka, kuma babu ceto. Kafirai kuwa su ne azzalumai



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 255

ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ ٱلۡحَيُّ ٱلۡقَيُّومُۚ لَا تَأۡخُذُهُۥ سِنَةٞ وَلَا نَوۡمٞۚ لَّهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۗ مَن ذَا ٱلَّذِي يَشۡفَعُ عِندَهُۥٓ إِلَّا بِإِذۡنِهِۦۚ يَعۡلَمُ مَا بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَمَا خَلۡفَهُمۡۖ وَلَا يُحِيطُونَ بِشَيۡءٖ مِّنۡ عِلۡمِهِۦٓ إِلَّا بِمَا شَآءَۚ وَسِعَ كُرۡسِيُّهُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَۖ وَلَا يَـُٔودُهُۥ حِفۡظُهُمَاۚ وَهُوَ ٱلۡعَلِيُّ ٱلۡعَظِيمُ

Allah, babu wani abin bauta wa da cancanta sai Shi, Rayayye, Tsayayye da Zatinsa; gyangyaxi ba ya kama shi, ballantana barci. Abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa nasa ne shi kaxai. Wane ne ya isa ya yi ceto a wurinsa in ba da izininsa ba? Ya san abin da yake tare da su a yanzu da kuma abin da zai biyo bayansu; kuma ba sa iya sanin wani abu cikin iliminsa sai abin da Ya ga dama. Kursiyyunsa ya yalwaci sammai da qasa, kuma kiyaye su ba zai nauyaye Shi ba, kuma Shi ne Maxaukaki Mai girma



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 256

لَآ إِكۡرَاهَ فِي ٱلدِّينِۖ قَد تَّبَيَّنَ ٱلرُّشۡدُ مِنَ ٱلۡغَيِّۚ فَمَن يَكۡفُرۡ بِٱلطَّـٰغُوتِ وَيُؤۡمِنۢ بِٱللَّهِ فَقَدِ ٱسۡتَمۡسَكَ بِٱلۡعُرۡوَةِ ٱلۡوُثۡقَىٰ لَا ٱنفِصَامَ لَهَاۗ وَٱللَّهُ سَمِيعٌ عَلِيمٌ

Babu tilastawa a addini, haqiqa shiriya ta riga ta bayyana daban da vata. Don haka duk wanda ya kafirce wa Xagutu, kuma ya yi imani da Allah, to haqiqa ya yi riqo da igiya mafi qarfi wadda ba ta tsinkewa. Kuma Allah Mai ji ne, Masani



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 257

ٱللَّهُ وَلِيُّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ يُخۡرِجُهُم مِّنَ ٱلظُّلُمَٰتِ إِلَى ٱلنُّورِۖ وَٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَوۡلِيَآؤُهُمُ ٱلطَّـٰغُوتُ يُخۡرِجُونَهُم مِّنَ ٱلنُّورِ إِلَى ٱلظُّلُمَٰتِۗ أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Allah Shi ne Majivincin lamarin waxanda suka yi imani, Yana fitar da su daga duffai zuwa ga haske; waxanda suka kafirce kuwa, majivinta lamarinsu su ne xagutai, suna fitar da su daga haske zuwa duffai. Waxannan su ne ‘yan wuta; su masu dawwama ne a cikinta



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 258

أَلَمۡ تَرَ إِلَى ٱلَّذِي حَآجَّ إِبۡرَٰهِـۧمَ فِي رَبِّهِۦٓ أَنۡ ءَاتَىٰهُ ٱللَّهُ ٱلۡمُلۡكَ إِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِـۧمُ رَبِّيَ ٱلَّذِي يُحۡيِۦ وَيُمِيتُ قَالَ أَنَا۠ أُحۡيِۦ وَأُمِيتُۖ قَالَ إِبۡرَٰهِـۧمُ فَإِنَّ ٱللَّهَ يَأۡتِي بِٱلشَّمۡسِ مِنَ ٱلۡمَشۡرِقِ فَأۡتِ بِهَا مِنَ ٱلۡمَغۡرِبِ فَبُهِتَ ٱلَّذِي كَفَرَۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Shin ba ka ga wanda ya yi jayayya da Ibrahim ba game da lamarin Ubangijinsa, don Allah ya ba shi mulki, yayin da Ibrahimu ya ce: “Ubangijina Shi ne Yake rayawa, kuma Yake kashewa.” Sai ya ce: “Ai ni ma ina rayawa, kuma ina kashewa.” Sai Ibrahim ya ce: “To Allah Yana kawo rana daga gabas, to kai ka kawo ta daga yamma.” Sai wanda ya kafirta ya kixime. Kuma Allah ba Ya shiryar da azzaluman mutane



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 259

أَوۡ كَٱلَّذِي مَرَّ عَلَىٰ قَرۡيَةٖ وَهِيَ خَاوِيَةٌ عَلَىٰ عُرُوشِهَا قَالَ أَنَّىٰ يُحۡيِۦ هَٰذِهِ ٱللَّهُ بَعۡدَ مَوۡتِهَاۖ فَأَمَاتَهُ ٱللَّهُ مِاْئَةَ عَامٖ ثُمَّ بَعَثَهُۥۖ قَالَ كَمۡ لَبِثۡتَۖ قَالَ لَبِثۡتُ يَوۡمًا أَوۡ بَعۡضَ يَوۡمٖۖ قَالَ بَل لَّبِثۡتَ مِاْئَةَ عَامٖ فَٱنظُرۡ إِلَىٰ طَعَامِكَ وَشَرَابِكَ لَمۡ يَتَسَنَّهۡۖ وَٱنظُرۡ إِلَىٰ حِمَارِكَ وَلِنَجۡعَلَكَ ءَايَةٗ لِّلنَّاسِۖ وَٱنظُرۡ إِلَى ٱلۡعِظَامِ كَيۡفَ نُنشِزُهَا ثُمَّ نَكۡسُوهَا لَحۡمٗاۚ فَلَمَّا تَبَيَّنَ لَهُۥ قَالَ أَعۡلَمُ أَنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Ko kuma kamar mutumin da ya wuce ta wata alqarya alhalin ta zama kango, sai ya ce: “Ta yaya Allah zai raya wannan bayan mutuwarta?” Sai Allah Ya karvi rayuwarsa tsawon shekara xari, sannan Ya tashe shi, Ya ce: “Mene ne tsawon lokacin da ka zauna?” Sai ya ce: “Ai na zauna yini xaya ne ko ma wani sashi na yinin.” Sai Ya ce: “Ai ka zauna tsawon shekara xari ne, don haka dubi abincinka da abin shanka bai canja ba, kuma ka dubi jakinka mana, don Mu sanya ka ka zamanto aya ga mutane, kuma ka dubi qasusuwan ka gani yadda za Mu haxa su, sannan Mu lulluve su da nama.”To lokacin da komai ya bayyana a gare shi, sai ya ce: “Na sani lalle Allah Mai iko ne a kan komai.”



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 260

وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِـۧمُ رَبِّ أَرِنِي كَيۡفَ تُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰۖ قَالَ أَوَلَمۡ تُؤۡمِنۖ قَالَ بَلَىٰ وَلَٰكِن لِّيَطۡمَئِنَّ قَلۡبِيۖ قَالَ فَخُذۡ أَرۡبَعَةٗ مِّنَ ٱلطَّيۡرِ فَصُرۡهُنَّ إِلَيۡكَ ثُمَّ ٱجۡعَلۡ عَلَىٰ كُلِّ جَبَلٖ مِّنۡهُنَّ جُزۡءٗا ثُمَّ ٱدۡعُهُنَّ يَأۡتِينَكَ سَعۡيٗاۚ وَٱعۡلَمۡ أَنَّ ٱللَّهَ عَزِيزٌ حَكِيمٞ

Kuma ka tuna lokacin da Ibrahimu ya ce: “Ya Ubangijina, Ka nuna mini yadda Kake rayar da matattu.” Sai ya ce: “Shin ko ba ka yi imani ba ne?” Ya ce: “A’a, (na yi imani), sai dai ina son zuciyata ta qara samun nutsuwa.” Sai Ya ce: “To ka kama tsuntsaye huxu ka tara su wajenka, sannan ka sanya yanka xaya-xaya nasu a kan kowane saman dutse, sannan ka kira su; za su zo maka da gaggawa. Kuma ka sani cewa lalle Allah Mabuwayi ne, Mai hikima.”



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 261

مَّثَلُ ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ كَمَثَلِ حَبَّةٍ أَنۢبَتَتۡ سَبۡعَ سَنَابِلَ فِي كُلِّ سُنۢبُلَةٖ مِّاْئَةُ حَبَّةٖۗ وَٱللَّهُ يُضَٰعِفُ لِمَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ وَٰسِعٌ عَلِيمٌ

Misalin waxanda suke ciyar da dukiyoyinsu a hanyar Allah, kamar misalin qwaya xaya ce da ta fitar da zangarniya bakwai, a cikinta kowace zangarniya kuma (aka sami) qwaya xari. Kuma Allah Yana ninninkawa ga wanda Ya ga dama, kuma Allah Mai yalwa ne, Masani



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 262

ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ ثُمَّ لَا يُتۡبِعُونَ مَآ أَنفَقُواْ مَنّٗا وَلَآ أَذٗى لَّهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Waxanda suke ciyar da dukiyoyinsu a hanyar Allah, sannan ba sa bin abin da suka ciyar da gori ko cuta, (waxannan) suna da ladansu a wajen Ubangijinsu, kuma babu tsoro a tare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 263

۞قَوۡلٞ مَّعۡرُوفٞ وَمَغۡفِرَةٌ خَيۡرٞ مِّن صَدَقَةٖ يَتۡبَعُهَآ أَذٗىۗ وَٱللَّهُ غَنِيٌّ حَلِيمٞ

Kyakkyawar magana da yafiya sun fi sadakar da cutarwa za ta biyo bayanta alheri. Kuma Allah Shi ne Wadatacce, Mai haquri



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 264

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تُبۡطِلُواْ صَدَقَٰتِكُم بِٱلۡمَنِّ وَٱلۡأَذَىٰ كَٱلَّذِي يُنفِقُ مَالَهُۥ رِئَآءَ ٱلنَّاسِ وَلَا يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِۖ فَمَثَلُهُۥ كَمَثَلِ صَفۡوَانٍ عَلَيۡهِ تُرَابٞ فَأَصَابَهُۥ وَابِلٞ فَتَرَكَهُۥ صَلۡدٗاۖ لَّا يَقۡدِرُونَ عَلَىٰ شَيۡءٖ مِّمَّا كَسَبُواْۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku vata sadaqoqinku da gori da cutarwa, kamar wanda yake ciyar da dukiyarsa don mutane su gani, kuma ba ya imani da Allah da ranar lahira; to misalinsa kamar misalin kamfa ne da turvaya take a kansa sai ruwan sama mamako ya same shi, sai ya bar shi tatas. Ba za su amfana da komai daga abin da suka aikata ba. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane kafirai



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 265

وَمَثَلُ ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُمُ ٱبۡتِغَآءَ مَرۡضَاتِ ٱللَّهِ وَتَثۡبِيتٗا مِّنۡ أَنفُسِهِمۡ كَمَثَلِ جَنَّةِۭ بِرَبۡوَةٍ أَصَابَهَا وَابِلٞ فَـَٔاتَتۡ أُكُلَهَا ضِعۡفَيۡنِ فَإِن لَّمۡ يُصِبۡهَا وَابِلٞ فَطَلّٞۗ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٌ

Kuma misalin waxanda suke ciyar da dukiyoyinsu don neman yardar Allah da tabbatar da (imani) a zukatansu, kamar misalin gona ce a kan jigawa sai ruwan sama mamako ya same ta, sai ta ba da amfaninta rivi-biyu. To idan mamakon ruwan bai same ta ba, sai yayyafi (ya wadatar da ita). Kuma Allah Mai ganin abin da kuke aikatawa ne



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 266

أَيَوَدُّ أَحَدُكُمۡ أَن تَكُونَ لَهُۥ جَنَّةٞ مِّن نَّخِيلٖ وَأَعۡنَابٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ لَهُۥ فِيهَا مِن كُلِّ ٱلثَّمَرَٰتِ وَأَصَابَهُ ٱلۡكِبَرُ وَلَهُۥ ذُرِّيَّةٞ ضُعَفَآءُ فَأَصَابَهَآ إِعۡصَارٞ فِيهِ نَارٞ فَٱحۡتَرَقَتۡۗ كَذَٰلِكَ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ لَكُمُ ٱلۡأٓيَٰتِ لَعَلَّكُمۡ تَتَفَكَّرُونَ

Shin yanzu xayanku zai yi fatan a ce yana da wata gona ta itacen dabino da kuma inabai, wadda qoramu suke gudana a qarqashinta, yana da dukkan wasu nau’uka na ‘ya’yan itace a cikinta, sai kuma girma ya kama shi, kuma ga shi yana da yara raunana, sai kuma wata irin guguwa mai xauke da wuta ta same ta, sai (gonar gaba xaya) ta qone? Kamar haka ne Allah Yake bayyana muku ayoyi don ku riqa yin tunani



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 267

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَنفِقُواْ مِن طَيِّبَٰتِ مَا كَسَبۡتُمۡ وَمِمَّآ أَخۡرَجۡنَا لَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِۖ وَلَا تَيَمَّمُواْ ٱلۡخَبِيثَ مِنۡهُ تُنفِقُونَ وَلَسۡتُم بِـَٔاخِذِيهِ إِلَّآ أَن تُغۡمِضُواْ فِيهِۚ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ غَنِيٌّ حَمِيدٌ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku ciyar daga daxaxan abin da kuka tsuwurwuta da kuma abin da muka fitar muku shi daga cikin qasa, kuma kar ku nufaci mummuna daga cikinsa ku ce daga gare shi ne za ku ciyar, alhalin ku ma kanku (idan an ba ku) ba za ku karve shi ba sai kun runtse idanu. Kuma ku sani cewa lalle Allah Mawadaci ne, Sha-yabo



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 268

ٱلشَّيۡطَٰنُ يَعِدُكُمُ ٱلۡفَقۡرَ وَيَأۡمُرُكُم بِٱلۡفَحۡشَآءِۖ وَٱللَّهُ يَعِدُكُم مَّغۡفِرَةٗ مِّنۡهُ وَفَضۡلٗاۗ وَٱللَّهُ وَٰسِعٌ عَلِيمٞ

Shaixan ne yake tsoratar da ku da talauci, kuma yana umartar ku da alfasha; Allah kuwa Yana yi muku alqawarin gafara ta musamman daga gare Shi da kuma falala. Kuma Allah Mai yalwa ne, Masani



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 269

يُؤۡتِي ٱلۡحِكۡمَةَ مَن يَشَآءُۚ وَمَن يُؤۡتَ ٱلۡحِكۡمَةَ فَقَدۡ أُوتِيَ خَيۡرٗا كَثِيرٗاۗ وَمَا يَذَّكَّرُ إِلَّآ أُوْلُواْ ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Yana bayar da hikima ga wanda Ya ga dama; kuma dukkan wanda aka bai wa hikima, to haqiqa an ba shi alheri mai tarin yawa. Kuma ba wanda yake wa’azantuwa sai ma’abota hankula



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 270

وَمَآ أَنفَقۡتُم مِّن نَّفَقَةٍ أَوۡ نَذَرۡتُم مِّن نَّذۡرٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُهُۥۗ وَمَا لِلظَّـٰلِمِينَ مِنۡ أَنصَارٍ

Kuma abin da kuka ciyar na abin ciyarwa ko kuka yi alwashi na bakance, to lalle Allah Yana sane da shi. Kuma azzalumai ba su da waxansu mataimaka



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 271

إِن تُبۡدُواْ ٱلصَّدَقَٰتِ فَنِعِمَّا هِيَۖ وَإِن تُخۡفُوهَا وَتُؤۡتُوهَا ٱلۡفُقَرَآءَ فَهُوَ خَيۡرٞ لَّكُمۡۚ وَيُكَفِّرُ عَنكُم مِّن سَيِّـَٔاتِكُمۡۗ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٞ

In da za ku bayyanar da sadakoki a fili, to madalla da hakan, kuma idan kuka voye sadaqar, kuma kuka ba da ita ga talakawa, to hakan shi ya fi alheri a gare ku, kuma zai kankare muku kurakurenku, kuma Allah Masanin abin da kuke aikatawa ne



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 272

۞لَّيۡسَ عَلَيۡكَ هُدَىٰهُمۡ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ يَهۡدِي مَن يَشَآءُۗ وَمَا تُنفِقُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَلِأَنفُسِكُمۡۚ وَمَا تُنفِقُونَ إِلَّا ٱبۡتِغَآءَ وَجۡهِ ٱللَّهِۚ وَمَا تُنفِقُواْ مِنۡ خَيۡرٖ يُوَفَّ إِلَيۡكُمۡ وَأَنتُمۡ لَا تُظۡلَمُونَ

Shiryar da su ba a kanka yake ba, sai dai Allah ne Yake shiryar da wanda Ya ga dama, kuma duk abin da kuka ciyar na alheri, to domin kawunanku ne, kuma ba za ku ciyar ba sai don neman yardar Allah; kuma duk abin da kuka ciyar na alheri, za a cika muku ladansa, alhali kuma ba za a zalunce ku ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 273

لِلۡفُقَرَآءِ ٱلَّذِينَ أُحۡصِرُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ لَا يَسۡتَطِيعُونَ ضَرۡبٗا فِي ٱلۡأَرۡضِ يَحۡسَبُهُمُ ٱلۡجَاهِلُ أَغۡنِيَآءَ مِنَ ٱلتَّعَفُّفِ تَعۡرِفُهُم بِسِيمَٰهُمۡ لَا يَسۡـَٔلُونَ ٱلنَّاسَ إِلۡحَافٗاۗ وَمَا تُنفِقُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِهِۦ عَلِيمٌ

Ga mabuqata waxanda aka tsare saboda Allah, ba su da ikon yawatawa a bayan qasa, har wanda ya jahilci halinsu yana zato su mawadata ne saboda kame kai; za ka gane su ne da alamominsu, ba sa naciyar roqar mutane, kuma duk abin da kuka ciyar na alheri, to Allah Yana sane da shi



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 274

ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُم بِٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِ سِرّٗا وَعَلَانِيَةٗ فَلَهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Waxanda suke ciyar da dukiyoyinsu dare da rana a voye da kuma a sarari, to suna da ladansu a wajen Ubangijinsu, kuma babu tsoro a tare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 275

ٱلَّذِينَ يَأۡكُلُونَ ٱلرِّبَوٰاْ لَا يَقُومُونَ إِلَّا كَمَا يَقُومُ ٱلَّذِي يَتَخَبَّطُهُ ٱلشَّيۡطَٰنُ مِنَ ٱلۡمَسِّۚ ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ قَالُوٓاْ إِنَّمَا ٱلۡبَيۡعُ مِثۡلُ ٱلرِّبَوٰاْۗ وَأَحَلَّ ٱللَّهُ ٱلۡبَيۡعَ وَحَرَّمَ ٱلرِّبَوٰاْۚ فَمَن جَآءَهُۥ مَوۡعِظَةٞ مِّن رَّبِّهِۦ فَٱنتَهَىٰ فَلَهُۥ مَا سَلَفَ وَأَمۡرُهُۥٓ إِلَى ٱللَّهِۖ وَمَنۡ عَادَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Waxanda suke cin riba ba za su tashi ba (daga qaburburansu) sai kamar tashin mutumin da Shaixan yake bige shi da hauka. Hakan zai faru ne don sun ce: “Lalle kasuwanci kamar riba yake.” Kuma Allah Ya halatta kasuwanci, kuma Ya haramta riba. To duk wanda wa’azi ya zo masa daga wurin Ubangijinsa, sai ya daina, to abin da ya wuce a baya ya zama nasa, kuma al’amarinsa yana wurin Allah; wanda kuma ya sake komawa daga baya, to waxannan su ne ma’abota wuta, suna masu dawwama a cikinta



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 276

يَمۡحَقُ ٱللَّهُ ٱلرِّبَوٰاْ وَيُرۡبِي ٱلصَّدَقَٰتِۗ وَٱللَّهُ لَا يُحِبُّ كُلَّ كَفَّارٍ أَثِيمٍ

Allah Yana shafe albarkar riba, Yana kuma havaka sadaqa. Kuma Allah ba Ya son dukkan wani mai yawan kafircewa, mai yawan savo



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 277

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَأَقَامُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتَوُاْ ٱلزَّكَوٰةَ لَهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Lalle waxanda suka yi imani kuma suka yi ayyuka nagari kuma suka tsayar da salla, kuma suka bayar da zakka, to suna da ladansu a wajen Ubangijinsu, kuma babu jin tsoro a gare su, kuma ba za su yi baqin ciki ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 278

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَذَرُواْ مَا بَقِيَ مِنَ ٱلرِّبَوٰٓاْ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku rabu da abin da ya yi ragowa na riba in har kun kasance muminai



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 279

فَإِن لَّمۡ تَفۡعَلُواْ فَأۡذَنُواْ بِحَرۡبٖ مِّنَ ٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦۖ وَإِن تُبۡتُمۡ فَلَكُمۡ رُءُوسُ أَمۡوَٰلِكُمۡ لَا تَظۡلِمُونَ وَلَا تُظۡلَمُونَ

Idan kuwa ba ku aikata haka ba, to ku saurari wani yaqi daga Allah da Manzonsa; idan kuwa kun tuba, to uwar kuxin taku ce, ba za ku yi zalunci ba, ku ma kuma ba za a zalunce ku ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 280

وَإِن كَانَ ذُو عُسۡرَةٖ فَنَظِرَةٌ إِلَىٰ مَيۡسَرَةٖۚ وَأَن تَصَدَّقُواْ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Kuma idan (mai cin bashin) ya kasance ma’abocin matsi, to sai a yi masa jinkiri zuwa lokacin da zai sami sauqi, kuma in da za ku yi sadaqa shi ya fi alheri a gare ku in kun kasance kuna da masaniya



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 281

وَٱتَّقُواْ يَوۡمٗا تُرۡجَعُونَ فِيهِ إِلَى ٱللَّهِۖ ثُمَّ تُوَفَّىٰ كُلُّ نَفۡسٖ مَّا كَسَبَتۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Kuma ku kiyayi wani yini da za a mayar da ku zuwa ga Allah a cikinsa, sannan kowane rai za a cika masa abin da ya aiwatar na aiki, kuma su ba za a zalunce su ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 282

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِذَا تَدَايَنتُم بِدَيۡنٍ إِلَىٰٓ أَجَلٖ مُّسَمّٗى فَٱكۡتُبُوهُۚ وَلۡيَكۡتُب بَّيۡنَكُمۡ كَاتِبُۢ بِٱلۡعَدۡلِۚ وَلَا يَأۡبَ كَاتِبٌ أَن يَكۡتُبَ كَمَا عَلَّمَهُ ٱللَّهُۚ فَلۡيَكۡتُبۡ وَلۡيُمۡلِلِ ٱلَّذِي عَلَيۡهِ ٱلۡحَقُّ وَلۡيَتَّقِ ٱللَّهَ رَبَّهُۥ وَلَا يَبۡخَسۡ مِنۡهُ شَيۡـٔٗاۚ فَإِن كَانَ ٱلَّذِي عَلَيۡهِ ٱلۡحَقُّ سَفِيهًا أَوۡ ضَعِيفًا أَوۡ لَا يَسۡتَطِيعُ أَن يُمِلَّ هُوَ فَلۡيُمۡلِلۡ وَلِيُّهُۥ بِٱلۡعَدۡلِۚ وَٱسۡتَشۡهِدُواْ شَهِيدَيۡنِ مِن رِّجَالِكُمۡۖ فَإِن لَّمۡ يَكُونَا رَجُلَيۡنِ فَرَجُلٞ وَٱمۡرَأَتَانِ مِمَّن تَرۡضَوۡنَ مِنَ ٱلشُّهَدَآءِ أَن تَضِلَّ إِحۡدَىٰهُمَا فَتُذَكِّرَ إِحۡدَىٰهُمَا ٱلۡأُخۡرَىٰۚ وَلَا يَأۡبَ ٱلشُّهَدَآءُ إِذَا مَا دُعُواْۚ وَلَا تَسۡـَٔمُوٓاْ أَن تَكۡتُبُوهُ صَغِيرًا أَوۡ كَبِيرًا إِلَىٰٓ أَجَلِهِۦۚ ذَٰلِكُمۡ أَقۡسَطُ عِندَ ٱللَّهِ وَأَقۡوَمُ لِلشَّهَٰدَةِ وَأَدۡنَىٰٓ أَلَّا تَرۡتَابُوٓاْ إِلَّآ أَن تَكُونَ تِجَٰرَةً حَاضِرَةٗ تُدِيرُونَهَا بَيۡنَكُمۡ فَلَيۡسَ عَلَيۡكُمۡ جُنَاحٌ أَلَّا تَكۡتُبُوهَاۗ وَأَشۡهِدُوٓاْ إِذَا تَبَايَعۡتُمۡۚ وَلَا يُضَآرَّ كَاتِبٞ وَلَا شَهِيدٞۚ وَإِن تَفۡعَلُواْ فَإِنَّهُۥ فُسُوقُۢ بِكُمۡۗ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَۖ وَيُعَلِّمُكُمُ ٱللَّهُۗ وَٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka ba wa junanku bashi zuwa wani lokaci sananne, to ku rubuta shi, kuma a sami wani marubuci da zai rubuta a tsakaninku da adalci, kuma marubucin kar ya qi rubutawa kamar yadda Allah ya sanar da shi. Don haka ya rubuta, kuma shi wanda haqqi yake kansa sai ya yi shifta gare shi, kuma ya ji tsoron Allah Ubangijinsa, kuma kada ya tauye wani abu a cikinsa. To idan wanda haqqi yake kansa ya kasance wawa ne ko mai rauni ko ba shi da ikon ya yi shifta shi da kansa, to sai majivincin lamarinsa ya yi shifta (a madadinsa) da adalci. Kuma ku kafa shaidu biyu cikin mazajenku; kuma idan ba su kasance mazaje biyu ba, to sai a nemi namiji xaya da mata biyu daga shaidun da kuka yarda da su, saboda idan xaya daga cikinsu ta manta sai xayar ta tuna mata, kuma kada shaidun su qi zuwa idan an kiraye su, kuma kada ku qosa, ku rubuta shi, kaxan ne ko da yawa, zuwa cikar wa’adinsa. Abin da aka ambata mukun nan shi ne ya fi zama adalci a wajen Allah, kuma ya fi daidaita shaida, kuma shi ya fi kusata ku ta yadda ba za ku yi shakka ba, sai dai idan ya kasance ciniki ne hannu da hannu da kuke gudanar da shi tsakaninku; to babu laifi a kanku idan ba ku rubuta shi ba. Kuma ku kafa shaida idan kun yi hulxa ta ciniki, kuma kada marubuci ya yi cuta, haka shi ma mai shaida (kada ya yi cuta)[1]. Idan kuwa har kuka aikata haka, to lalle wannan fasiqanci ne a gare ku. Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kuma Allah Yana sanar da ku (dokokinsa). Kuma Allah Masanin komai ne


1- Hakanan ayar tana nufin cewa, su ma kuma kada a cutar da su.