۞وَٱذۡكُرُواْ ٱللَّهَ فِيٓ أَيَّامٖ مَّعۡدُودَٰتٖۚ فَمَن تَعَجَّلَ فِي يَوۡمَيۡنِ فَلَآ إِثۡمَ عَلَيۡهِ وَمَن تَأَخَّرَ فَلَآ إِثۡمَ عَلَيۡهِۖ لِمَنِ ٱتَّقَىٰۗ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّكُمۡ إِلَيۡهِ تُحۡشَرُونَ
Kuma ku ambaci Allah a cikin wasu kwanaki qididdigaggu. To duk wanda ya yi gaggawar (barin Mina) cikin kwana biyu, to babu laifi a gare shi; wanda kuwa ya yi jinkiri, to babu laifi a gare shi, (amma dukkansu) ga wanda ya yi taqawa. Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku sani cewa, zuwa gare Shi za a tattara ku
وَمِنَ ٱلنَّاسِ مَن يُعۡجِبُكَ قَوۡلُهُۥ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَيُشۡهِدُ ٱللَّهَ عَلَىٰ مَا فِي قَلۡبِهِۦ وَهُوَ أَلَدُّ ٱلۡخِصَامِ
Kuma daga cikin mutane akwai wanda zancensa yake burge ka a rayuwar duniya, kuma yana shaidar da Allah ga abin da yake cikin zuciyarsa, alhali kuwa shi mai tsananin husuma ne
وَإِذَا تَوَلَّىٰ سَعَىٰ فِي ٱلۡأَرۡضِ لِيُفۡسِدَ فِيهَا وَيُهۡلِكَ ٱلۡحَرۡثَ وَٱلنَّسۡلَۚ وَٱللَّهُ لَا يُحِبُّ ٱلۡفَسَادَ
Kuma idan ya juya baya, zai yi ta yawo a cikin qasa don ya yi varna a cikinta, kuma ya lalata amfanin gona da dabbobi. Allah kuwa ba Ya son varna
وَإِذَا قِيلَ لَهُ ٱتَّقِ ٱللَّهَ أَخَذَتۡهُ ٱلۡعِزَّةُ بِٱلۡإِثۡمِۚ فَحَسۡبُهُۥ جَهَنَّمُۖ وَلَبِئۡسَ ٱلۡمِهَادُ
Idan kuma aka ce masa: “Ka kiyaye dokokin Allah” sai girman kai ya kama shi saboda savo. To Jahannama ta ishe shi (makwanci), kuma lalle tir da wannan makwanci
وَمِنَ ٱلنَّاسِ مَن يَشۡرِي نَفۡسَهُ ٱبۡتِغَآءَ مَرۡضَاتِ ٱللَّهِۚ وَٱللَّهُ رَءُوفُۢ بِٱلۡعِبَادِ
Kuma daga cikin mutane akwai wanda yake sayar da kansa don neman yardar Allah. Allah kuwa Mai yawan tausayi ne ga bayi
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱدۡخُلُواْ فِي ٱلسِّلۡمِ كَآفَّةٗ وَلَا تَتَّبِعُواْ خُطُوَٰتِ ٱلشَّيۡطَٰنِۚ إِنَّهُۥ لَكُمۡ عَدُوّٞ مُّبِينٞ
Ya ku waxanda suka yi imani, ku shiga cikin addinin Musulunci gaba xaya, kuma kar ku bi hanyoyin Shaixan. Lalle shi maqiyi ne a gare ku, mai bayyana (qiyayya)
فَإِن زَلَلۡتُم مِّنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَتۡكُمُ ٱلۡبَيِّنَٰتُ فَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ عَزِيزٌ حَكِيمٌ
To idan kuka zame bayan hujjoji bayyanannu sun zo muku, to ku sani cewa, lalle Allah Mabuwayi ne, Mai hikima
هَلۡ يَنظُرُونَ إِلَّآ أَن يَأۡتِيَهُمُ ٱللَّهُ فِي ظُلَلٖ مِّنَ ٱلۡغَمَامِ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَقُضِيَ ٱلۡأَمۡرُۚ وَإِلَى ٱللَّهِ تُرۡجَعُ ٱلۡأُمُورُ
Shin ko akwai abin da suke jira ne, in ban da Allah Ya zo musu a cikin waxansu inuwoyi na gizagizai da mala’iku, sai a zartar da al’amari? Kuma zuwa ga Allah ne ake mayar da al’amura
سَلۡ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ كَمۡ ءَاتَيۡنَٰهُم مِّنۡ ءَايَةِۭ بَيِّنَةٖۗ وَمَن يُبَدِّلۡ نِعۡمَةَ ٱللَّهِ مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَتۡهُ فَإِنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ
Ka tambayi Banu Isra’ila, sau nawa Muka ba su wata aya bayyananniya? Kuma duk wanda ya musanya ni’imar Allah bayan ta zo masa, to lalle Allah Mai tsananin uquba ne
زُيِّنَ لِلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَا وَيَسۡخَرُونَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْۘ وَٱلَّذِينَ ٱتَّقَوۡاْ فَوۡقَهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۗ وَٱللَّهُ يَرۡزُقُ مَن يَشَآءُ بِغَيۡرِ حِسَابٖ
An qawata wa kafirai rayuwar duniya, kuma suna yin izgili ga waxanda suka yi imani. Waxanda kuwa suka yi taqawa su ne a samansu a ranar alqiyama. Kuma Allah Yana arzurta wanda ya ga dama, ba tare da lissafi ba
كَانَ ٱلنَّاسُ أُمَّةٗ وَٰحِدَةٗ فَبَعَثَ ٱللَّهُ ٱلنَّبِيِّـۧنَ مُبَشِّرِينَ وَمُنذِرِينَ وَأَنزَلَ مَعَهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ لِيَحۡكُمَ بَيۡنَ ٱلنَّاسِ فِيمَا ٱخۡتَلَفُواْ فِيهِۚ وَمَا ٱخۡتَلَفَ فِيهِ إِلَّا ٱلَّذِينَ أُوتُوهُ مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَتۡهُمُ ٱلۡبَيِّنَٰتُ بَغۡيَۢا بَيۡنَهُمۡۖ فَهَدَى ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لِمَا ٱخۡتَلَفُواْ فِيهِ مِنَ ٱلۡحَقِّ بِإِذۡنِهِۦۗ وَٱللَّهُ يَهۡدِي مَن يَشَآءُ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٍ
Mutane sun kasance al’umma guda xaya, sai Allah Ya aiko da annabawa, suna masu albishir, kuma masu gargaxi, kuma Ya saukar da littafi tare da su da gaskiya, don ya yi hukunci tsakanin mutane cikin abin da suka yi savani a kansa. Kuma ba wasu ne suka yi savani a kansa ba sai waxanda aka ba wa shi, bayan hujjoji bayyanannu sun zo musu, don zalunci a tsakaninsu; sai Allah Ya shiryar da waxanda suka yi imani ga abin da (mutane) suka yi savani cikinsa na gaskiya da izininsa. Kuma Allah Yana shiryar da wanda Ya ga dama zuwa ga tafarki madaidaici
أَمۡ حَسِبۡتُمۡ أَن تَدۡخُلُواْ ٱلۡجَنَّةَ وَلَمَّا يَأۡتِكُم مَّثَلُ ٱلَّذِينَ خَلَوۡاْ مِن قَبۡلِكُمۖ مَّسَّتۡهُمُ ٱلۡبَأۡسَآءُ وَٱلضَّرَّآءُ وَزُلۡزِلُواْ حَتَّىٰ يَقُولَ ٱلرَّسُولُ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ مَتَىٰ نَصۡرُ ٱللَّهِۗ أَلَآ إِنَّ نَصۡرَ ٱللَّهِ قَرِيبٞ
Shin kun yi tsammanin za ku shiga Aljanna ne, alhalin misalin irin abin da ya shafi waxanda suka shuxe gabaninku bai zo muku ba? Tsananin talauci da cuta sun shafe su; kuma an girgiza su sosai, har Manzo da waxanda suka yi imani tare da shi suka riqa cewa: “Yaushe ne nasarar Allah za ta zo?” Ku saurara, lalle nasarar Allah a kusa take
يَسۡـَٔلُونَكَ مَاذَا يُنفِقُونَۖ قُلۡ مَآ أَنفَقۡتُم مِّنۡ خَيۡرٖ فَلِلۡوَٰلِدَيۡنِ وَٱلۡأَقۡرَبِينَ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينِ وَٱبۡنِ ٱلسَّبِيلِۗ وَمَا تَفۡعَلُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِهِۦ عَلِيمٞ
Suna tambayar ka, me za su ciyar ne? Ka ce: “Duk abin da za ku ciyar na alheri, to ga mahaifa da dangi mafiya kusanci da marayu da miskinai da matafiyi. Kuma duk abin da kuka aikata na alheri, to lalle Allah Masani ne da shi.”
كُتِبَ عَلَيۡكُمُ ٱلۡقِتَالُ وَهُوَ كُرۡهٞ لَّكُمۡۖ وَعَسَىٰٓ أَن تَكۡرَهُواْ شَيۡـٔٗا وَهُوَ خَيۡرٞ لَّكُمۡۖ وَعَسَىٰٓ أَن تُحِبُّواْ شَيۡـٔٗا وَهُوَ شَرّٞ لَّكُمۡۚ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ وَأَنتُمۡ لَا تَعۡلَمُونَ
An wajabta muku yaqi (ku muminai), ga shi kuwa kuna qin sa, kuma zai iya yiwuwa ku qi wani abu alhalin shi alheri ne a gare ku, kuma zai iya yiwuwa ku so wani abu alhalin shi sharri ne a gare ku. Kuma Allah Shi yake da sani, ku ba ku sani ba
يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلشَّهۡرِ ٱلۡحَرَامِ قِتَالٖ فِيهِۖ قُلۡ قِتَالٞ فِيهِ كَبِيرٞۚ وَصَدٌّ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ وَكُفۡرُۢ بِهِۦ وَٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ وَإِخۡرَاجُ أَهۡلِهِۦ مِنۡهُ أَكۡبَرُ عِندَ ٱللَّهِۚ وَٱلۡفِتۡنَةُ أَكۡبَرُ مِنَ ٱلۡقَتۡلِۗ وَلَا يَزَالُونَ يُقَٰتِلُونَكُمۡ حَتَّىٰ يَرُدُّوكُمۡ عَن دِينِكُمۡ إِنِ ٱسۡتَطَٰعُواْۚ وَمَن يَرۡتَدِدۡ مِنكُمۡ عَن دِينِهِۦ فَيَمُتۡ وَهُوَ كَافِرٞ فَأُوْلَـٰٓئِكَ حَبِطَتۡ أَعۡمَٰلُهُمۡ فِي ٱلدُّنۡيَا وَٱلۡأٓخِرَةِۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ
Suna tambayar ka game da wata mai alfarma, yin yaqi a cikinsa. Ka ce: “Yaqi a cikinsa, babban laifi ne, amma hana (mutane) bin tafarkin Allah da kafirce masa da kuma (hana mutane shiga) Masallaci mai alfarma da fitar da mutanensa daga gare shi, su ne mafi girman laifi a wajen Allah. Kuma (laifin) fitina ya fi na kisa girma.”[1] Kuma (kafirai) ba za su gushe ba suna yaqar ku, har sai sun raba ku da addininku, idan da za su sami dama. Kuma duk wanda ya yi ridda daga cikinku, ya bar addininsa, kuma ya mutu yana kafiri, to waxannan ayyukansu sun lalace a duniya da lahira, kuma waxannan su ne ma’abota wuta, suna masu dawwama a cikinta
1- Wannan ayar ta sauka ne bayan da wata runduna ta Musulmi suka kashe wani kafiri mai suna Ibnul Hadhrami a watan Rajab ba su sani ba. Sai kafirai suka riqa aibata su da haka, sai Allah ya saukar da wannan ayar.
إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱلَّذِينَ هَاجَرُواْ وَجَٰهَدُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ أُوْلَـٰٓئِكَ يَرۡجُونَ رَحۡمَتَ ٱللَّهِۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ
Lalle waxanda suka yi imani da kuma waxanda suka yi hijira, kuma suka yi jihadi don Allah, waxannan su ne suke fatan rahamar Allah; Allah kuwa Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai
۞يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلۡخَمۡرِ وَٱلۡمَيۡسِرِۖ قُلۡ فِيهِمَآ إِثۡمٞ كَبِيرٞ وَمَنَٰفِعُ لِلنَّاسِ وَإِثۡمُهُمَآ أَكۡبَرُ مِن نَّفۡعِهِمَاۗ وَيَسۡـَٔلُونَكَ مَاذَا يُنفِقُونَۖ قُلِ ٱلۡعَفۡوَۗ كَذَٰلِكَ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ لَكُمُ ٱلۡأٓيَٰتِ لَعَلَّكُمۡ تَتَفَكَّرُونَ
Suna tambayar ka game da giya da caca. Ka ce: “A cikin lamarinsu akwai zunubi mai girma da kuma waxansu amfanunnuka ga mutane. Amma zunubinsu ya fi amfaninsu girma”[1] Kuma suna tambayar ka, me za su ciyar? Ka ce: “Abin da ya daxu a kan buqatunku.” Kamar haka ne Allah Yake muku bayanin ayoyi don ku yi tunani
1- Wannan matakin farko ne na tsawatarwa game da giya. Allah ya haramta giya gaba xaya a Suratul Ma’ida, aya ta 90-91
فِي ٱلدُّنۡيَا وَٱلۡأٓخِرَةِۗ وَيَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلۡيَتَٰمَىٰۖ قُلۡ إِصۡلَاحٞ لَّهُمۡ خَيۡرٞۖ وَإِن تُخَالِطُوهُمۡ فَإِخۡوَٰنُكُمۡۚ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ ٱلۡمُفۡسِدَ مِنَ ٱلۡمُصۡلِحِۚ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَأَعۡنَتَكُمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَزِيزٌ حَكِيمٞ
Game da lamarin duniya da lahira. Kuma suna tambayar ka game da marayu. Ka ce : “Inganta musu dukiyarsu shi ne mafi alheri, kuma in kuka haxa cimakarku da tasu, to ai ‘yan’uwanku ne. Amma fa Allah Ya san mai son yin varna daga wanda yake son yin gyara. Kuma da Allah Ya ga dama da Ya quntata muku. Lalle Allah Mabuwayi ne, Mai hikima.”
وَلَا تَنكِحُواْ ٱلۡمُشۡرِكَٰتِ حَتَّىٰ يُؤۡمِنَّۚ وَلَأَمَةٞ مُّؤۡمِنَةٌ خَيۡرٞ مِّن مُّشۡرِكَةٖ وَلَوۡ أَعۡجَبَتۡكُمۡۗ وَلَا تُنكِحُواْ ٱلۡمُشۡرِكِينَ حَتَّىٰ يُؤۡمِنُواْۚ وَلَعَبۡدٞ مُّؤۡمِنٌ خَيۡرٞ مِّن مُّشۡرِكٖ وَلَوۡ أَعۡجَبَكُمۡۗ أُوْلَـٰٓئِكَ يَدۡعُونَ إِلَى ٱلنَّارِۖ وَٱللَّهُ يَدۡعُوٓاْ إِلَى ٱلۡجَنَّةِ وَٱلۡمَغۡفِرَةِ بِإِذۡنِهِۦۖ وَيُبَيِّنُ ءَايَٰتِهِۦ لِلنَّاسِ لَعَلَّهُمۡ يَتَذَكَّرُونَ
Kuma kada ku auri mata mushirikai har sai sun yi imani, kuma lalle baiwa mumina ta fi ‘ya mushirika alheri, ko da (mushirikar) ta burge ku. Kuma kada ku aurar wa mushirikai har sai sun yi imani; kuma lalle bawa mumini ya fi (xa) mushiriki alheri, ko da ya burge ku. Su waxancan (kafirai), suna kira ne zuwa ga wuta, Allah kuwa Yana kira ne zuwa ga Aljanna da gafara da izininsa, kuma Yana bayyana ayoyinsa ga mutane don su wa’azantu
وَيَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلۡمَحِيضِۖ قُلۡ هُوَ أَذٗى فَٱعۡتَزِلُواْ ٱلنِّسَآءَ فِي ٱلۡمَحِيضِ وَلَا تَقۡرَبُوهُنَّ حَتَّىٰ يَطۡهُرۡنَۖ فَإِذَا تَطَهَّرۡنَ فَأۡتُوهُنَّ مِنۡ حَيۡثُ أَمَرَكُمُ ٱللَّهُۚ إِنَّ ٱللَّهَ يُحِبُّ ٱلتَّوَّـٰبِينَ وَيُحِبُّ ٱلۡمُتَطَهِّرِينَ
Kuma suna tambayar ka game da jinin haila. Ka ce: “Shi cuta ne, don haka ku qaurace wa mata a (kwanakin) haila, kuma kada ku kusance su har sai sun tsarkaka. To idan suka yi tsarki, sai ku zo musu ta inda Allah Ya umarce ku. Lalle Allah Yana son masu yawan tuba, kuma Yana son masu tsarki.”
نِسَآؤُكُمۡ حَرۡثٞ لَّكُمۡ فَأۡتُواْ حَرۡثَكُمۡ أَنَّىٰ شِئۡتُمۡۖ وَقَدِّمُواْ لِأَنفُسِكُمۡۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّكُم مُّلَٰقُوهُۗ وَبَشِّرِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Matanku gonaki ne a gare ku, don haka ku zaike wa gonakinku ta inda kuka ga dama, kuma ku gabatar wa kawunanku (laduban da shari’a ta tanadar muku). Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku sani cewa, lalle ku masu saduwa ne da Shi. Kuma ka yi albishir ga muminai
وَلَا تَجۡعَلُواْ ٱللَّهَ عُرۡضَةٗ لِّأَيۡمَٰنِكُمۡ أَن تَبَرُّواْ وَتَتَّقُواْ وَتُصۡلِحُواْ بَيۡنَ ٱلنَّاسِۚ وَٱللَّهُ سَمِيعٌ عَلِيمٞ
Kuma kada ku mayar da Allah Ya zamanto kariya ga rantse-rantsenku don su hana ku aiki na xa’a ko na taqawa ko na sulhu tsakanin mutane. Kuma Allah Mai ji ne, Masani
لَّا يُؤَاخِذُكُمُ ٱللَّهُ بِٱللَّغۡوِ فِيٓ أَيۡمَٰنِكُمۡ وَلَٰكِن يُؤَاخِذُكُم بِمَا كَسَبَتۡ قُلُوبُكُمۡۗ وَٱللَّهُ غَفُورٌ حَلِيمٞ
Allah ba zai kama ku da yasasshen zance a cikin rantse-rantsenku ba, sai dai zai kama ku da abin da zukatanku suka qudurce. Kuma Allah Mai yawan gafara ne, Mai yawan haquri
لِّلَّذِينَ يُؤۡلُونَ مِن نِّسَآئِهِمۡ تَرَبُّصُ أَرۡبَعَةِ أَشۡهُرٖۖ فَإِن فَآءُو فَإِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ
Waxanda suke rantsuwar ba za su sadu da matansu ba, za a yi musu jinkiri na wata huxu; to idan sun dawo, to lalle Allah Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai
وَإِنۡ عَزَمُواْ ٱلطَّلَٰقَ فَإِنَّ ٱللَّهَ سَمِيعٌ عَلِيمٞ
Idan kuwa suka yi niyyar saki (a cikin zukatansu), to lalle Allah Mai ji ne, kuma Masani
وَٱلۡمُطَلَّقَٰتُ يَتَرَبَّصۡنَ بِأَنفُسِهِنَّ ثَلَٰثَةَ قُرُوٓءٖۚ وَلَا يَحِلُّ لَهُنَّ أَن يَكۡتُمۡنَ مَا خَلَقَ ٱللَّهُ فِيٓ أَرۡحَامِهِنَّ إِن كُنَّ يُؤۡمِنَّ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِۚ وَبُعُولَتُهُنَّ أَحَقُّ بِرَدِّهِنَّ فِي ذَٰلِكَ إِنۡ أَرَادُوٓاْ إِصۡلَٰحٗاۚ وَلَهُنَّ مِثۡلُ ٱلَّذِي عَلَيۡهِنَّ بِٱلۡمَعۡرُوفِۚ وَلِلرِّجَالِ عَلَيۡهِنَّ دَرَجَةٞۗ وَٱللَّهُ عَزِيزٌ حَكِيمٌ
Kuma mata waxanda aka saki za su dakatar da kawunansu (tsawon) qur’i[1] uku, kuma ba ya halatta a gare su su voye abin da Allah Ya halitta a cikin mahaifarsu, in sun kasance suna yin imani da Allah da ranar qarshe; kuma mazajensu su suka fi cancantar dawo da su a cikin wancan lokaci in sun yi nufin sulhu[2]; kuma su (mata) suna da haqqi kwatankwacin irin wanda yake kansu ta hanyar da aka sani, kuma mazaje suna da fifiko a kansu. Allah Kuma Mabuwayi ne, Mai hikima
1- Qur’i a Larabci yana nufin ‘haila’ ko ‘tsarki’, A ra’ayin manyan sahabbai, har da Halifofi huxu da wasu tabi’ai, sun ce, ana nufin ‘jinin haila’. Watau iddar wadda aka saki tana qare wa da xaukewar jinin al’adar ta ta uku bayan sakin.
2- Mijin da ya saki matarsa saki na farko, ko na biyu, zai iya dawo da ita matuqar suna son su ci gaba da zama da juna cikin mutuntawa da kyautatawa.
ٱلطَّلَٰقُ مَرَّتَانِۖ فَإِمۡسَاكُۢ بِمَعۡرُوفٍ أَوۡ تَسۡرِيحُۢ بِإِحۡسَٰنٖۗ وَلَا يَحِلُّ لَكُمۡ أَن تَأۡخُذُواْ مِمَّآ ءَاتَيۡتُمُوهُنَّ شَيۡـًٔا إِلَّآ أَن يَخَافَآ أَلَّا يُقِيمَا حُدُودَ ٱللَّهِۖ فَإِنۡ خِفۡتُمۡ أَلَّا يُقِيمَا حُدُودَ ٱللَّهِ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡهِمَا فِيمَا ٱفۡتَدَتۡ بِهِۦۗ تِلۡكَ حُدُودُ ٱللَّهِ فَلَا تَعۡتَدُوهَاۚ وَمَن يَتَعَدَّ حُدُودَ ٱللَّهِ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ
Saki sau biyu ne (xaya bayan xaya), don haka ko dai ya riqe ta ta hanyar da aka sani, ko kuma ya sake ta tare da kyautatawa. Kuma bai halatta gare ku ba ku karvi wani abu daga cikin abin da kuka ba su, sai fa idan su (ma’aurata) biyu sun ji tsoron ba za su tsayar da dokokin Allah ba. To idan kuka ji tsoron ba za su tsayar da dokokin Allah ba, to babu laifi a gare su game da abin da ta fanshi kanta da shi[1]. Waxannan iyakokin Allah ne, kada ku qetare su, kuma duk wanda ya qetare iyakokin Allah, to waxannan su ne azzalumai
1- Idan mace ta ga ba za ta iya zama da mijinta ba, to babu laifi ta mayar masa abin da ya kashe, sai su rabu. Wannan shi ne: Khul’u.
فَإِن طَلَّقَهَا فَلَا تَحِلُّ لَهُۥ مِنۢ بَعۡدُ حَتَّىٰ تَنكِحَ زَوۡجًا غَيۡرَهُۥۗ فَإِن طَلَّقَهَا فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡهِمَآ أَن يَتَرَاجَعَآ إِن ظَنَّآ أَن يُقِيمَا حُدُودَ ٱللَّهِۗ وَتِلۡكَ حُدُودُ ٱللَّهِ يُبَيِّنُهَا لِقَوۡمٖ يَعۡلَمُونَ
To idan ya sake sakin ta, ba za ta halatta a gare shi ba bayan haka har sai ta auri wani mijin daban[1]. To idan ya sake ta, to babu laifi gare su su koma, idan sun yi zaton cewa za su tsayar da dokokin Allah. Waxannan dokokin Allah ne, Yake bayyana su ga mutanen da suke da sani
1- Watau aure sahihi, kuma mijin ya tare da ita. Idan daga baya ya sake ta ta kammala iddarta, to za ta iya koma wa wajen mijinta na farko, amma bayan an sake xaura musu aure.
وَإِذَا طَلَّقۡتُمُ ٱلنِّسَآءَ فَبَلَغۡنَ أَجَلَهُنَّ فَأَمۡسِكُوهُنَّ بِمَعۡرُوفٍ أَوۡ سَرِّحُوهُنَّ بِمَعۡرُوفٖۚ وَلَا تُمۡسِكُوهُنَّ ضِرَارٗا لِّتَعۡتَدُواْۚ وَمَن يَفۡعَلۡ ذَٰلِكَ فَقَدۡ ظَلَمَ نَفۡسَهُۥۚ وَلَا تَتَّخِذُوٓاْ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ هُزُوٗاۚ وَٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتَ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡ وَمَآ أَنزَلَ عَلَيۡكُم مِّنَ ٱلۡكِتَٰبِ وَٱلۡحِكۡمَةِ يَعِظُكُم بِهِۦۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ
Kuma idan kuka saki mata, sai wa’adin iddarsu ya kusa, (idan kuna son su) sai ku riqe su ta hanyar da ta dace (a shari’ance) ko kuma ku qyale su ta hanyar da ta dace (a shari’ance); kuma kada ku riqe su da nufin cutarwa don ku qetare iyakar (Ubangiji). Duk wanda ya aikata haka kuwa, to haqiqa ya zalunci kansa. Kuma kada ku mayar da ayoyin Allah abin izgili, kuma ku tuna ni’imar Allah da Ya yi muku da abin da Ya saukar muku na Littafi da Hikima Yana yi muku wa’azi da shi. Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku sani lalle Allah Masanin komai ne
وَإِذَا طَلَّقۡتُمُ ٱلنِّسَآءَ فَبَلَغۡنَ أَجَلَهُنَّ فَلَا تَعۡضُلُوهُنَّ أَن يَنكِحۡنَ أَزۡوَٰجَهُنَّ إِذَا تَرَٰضَوۡاْ بَيۡنَهُم بِٱلۡمَعۡرُوفِۗ ذَٰلِكَ يُوعَظُ بِهِۦ مَن كَانَ مِنكُمۡ يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِۗ ذَٰلِكُمۡ أَزۡكَىٰ لَكُمۡ وَأَطۡهَرُۚ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ وَأَنتُمۡ لَا تَعۡلَمُونَ
Kuma idan kun saki mata sai suka cika wa’adin iddarsu, to (ku waliyyai) kada ku hana su su auri mazajensu (na da) idan sun yi yarjejeniya a tsakaninsu ta hanyar da ta dace (a shari’a). Wannan (abin da aka ambata) shi ne wanda ake yin wa’azi da shi ga wanda ya kasance daga cikinku, yana imani da Allah da ranar lahira. Wannan shi ne abin da ya fi alheri a gare ku kuma ya fi tsarki; kuma Allah Shi ne Yake da sani, ku ba ku sani ba