Surah: Suratul Qamar

Ayah : 40

وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun sauqaqe Alqur’ani don tunatarwa, to ko akwai mai wa’azantuwa?



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 41

وَلَقَدۡ جَآءَ ءَالَ فِرۡعَوۡنَ ٱلنُّذُرُ

Kuma haqiqa gargaxi ya zo wa mutanen Fir’auna



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 42

كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذۡنَٰهُمۡ أَخۡذَ عَزِيزٖ مُّقۡتَدِرٍ

Suka qaryata ayoyinmu dukkaninsu, sai Muka kama su irin kamu na Mabuwayi, Mai iko



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 43

أَكُفَّارُكُمۡ خَيۡرٞ مِّنۡ أُوْلَـٰٓئِكُمۡ أَمۡ لَكُم بَرَآءَةٞ فِي ٱلزُّبُرِ

Yanzu kafiranku (ku mutanen Makka) su ne suka fi waxancan alheri, ko kuwa kuna da wata hanya ta kuvuta ne a cikin littattafan da aka saukar?



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 44

أَمۡ يَقُولُونَ نَحۡنُ جَمِيعٞ مُّنتَصِرٞ

A’a, suna dai cewa ne: “Mu jama’a ce wadda za ta ci nasara.”



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 45

سَيُهۡزَمُ ٱلۡجَمۡعُ وَيُوَلُّونَ ٱلدُّبُرَ

To ba da daxewa ba za a karya jama’ar tasu[1], su kuma su ba da baya


1- Haka kuwa ya faru a yaqin Badar lokacin da aka karya lagon kafiran Makka, aka kashe manyansu da dama.


Surah: Suratul Qamar

Ayah : 46

بَلِ ٱلسَّاعَةُ مَوۡعِدُهُمۡ وَٱلسَّاعَةُ أَدۡهَىٰ وَأَمَرُّ

A’a, alqiyama ita ce lokacin yi musu azaba, alqiyama kuwa ita ta fi bala’i, ta kuma fi xaci



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 47

إِنَّ ٱلۡمُجۡرِمِينَ فِي ضَلَٰلٖ وَسُعُرٖ

Lalle masu manyan laifuka suna cikin vata da azabar wuta



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 48

يَوۡمَ يُسۡحَبُونَ فِي ٱلنَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمۡ ذُوقُواْ مَسَّ سَقَرَ

Ranar da za a ja su cikin wuta a kan fuskokinsu (a ce da su): “Ku xanxani azabar wutar Saqara.”



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 49

إِنَّا كُلَّ شَيۡءٍ خَلَقۡنَٰهُ بِقَدَرٖ

Lalle Mu, kowane abu Mun halitta shi da qaddara



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 50

وَمَآ أَمۡرُنَآ إِلَّا وَٰحِدَةٞ كَلَمۡحِۭ بِٱلۡبَصَرِ

Kuma al’amarinmu bai zamanto ba face kalma xaya kamar qiftawar ido



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 51

وَلَقَدۡ أَهۡلَكۡنَآ أَشۡيَاعَكُمۡ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun hallakar da ire-irenku[1], to ko akwai mai wa’azantuwa?


1- Watau kafirai irinsu masu taurin kai.


Surah: Suratul Qamar

Ayah : 52

وَكُلُّ شَيۡءٖ فَعَلُوهُ فِي ٱلزُّبُرِ

Kuma kowane abu da suka aikata yana cikin littattafai



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 53

وَكُلُّ صَغِيرٖ وَكَبِيرٖ مُّسۡتَطَرٌ

Kowane qaramin abu da babba kuma suna nan a rubuce



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 54

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَنَهَرٖ

Lalle masu taqawa suna cikin gidajen Aljanna da qoramu



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 55

فِي مَقۡعَدِ صِدۡقٍ عِندَ مَلِيكٖ مُّقۡتَدِرِۭ

A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko