Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 39

وَمَا لَا تُبۡصِرُونَ

Da kuma abin da ba kwa gani



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 40

إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ

Lalle shi (Alqur’ani) tabbas zance ne na wani manzo mai girma



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 41

وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَاعِرٖۚ قَلِيلٗا مَّا تُؤۡمِنُونَ

Shi kuwa ba zancen mawaqi ba ne. Kaxan ne qwarai kuke yin imani



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 42

وَلَا بِقَوۡلِ كَاهِنٖۚ قَلِيلٗا مَّا تَذَكَّرُونَ

Ba kuma zance ne na boka ba. Kaxan ne qwarai kuke wa’azantuwa



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 43

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Shi saukakke ne daga Ubangijin halittu



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 44

وَلَوۡ تَقَوَّلَ عَلَيۡنَا بَعۡضَ ٱلۡأَقَاوِيلِ

Kuma da ya qaga Mana wasu maganganu



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 45

لَأَخَذۡنَا مِنۡهُ بِٱلۡيَمِينِ

Tabbas da Mun kama shi da qarfi



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 46

ثُمَّ لَقَطَعۡنَا مِنۡهُ ٱلۡوَتِينَ

Sannan da Mun yanke masa jijiyar zuciyarsa



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 47

فَمَا مِنكُم مِّنۡ أَحَدٍ عَنۡهُ حَٰجِزِينَ

Sannan kuma ba wani xaya daga cikinku da zai kare shi



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 48

وَإِنَّهُۥ لَتَذۡكِرَةٞ لِّلۡمُتَّقِينَ

Lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne ga masu kiyaye dokokin Allah



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 49

وَإِنَّا لَنَعۡلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ

Lalle kuma Mu Muna sane da cewa a cikinku akwai masu qaryatawa



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 50

وَإِنَّهُۥ لَحَسۡرَةٌ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma lalle shi tabbas nadama ce ga kafirai



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 51

وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلۡيَقِينِ

Kuma lalle shi tabbas gaskiya ce ta sakankancewa



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 52

فَسَبِّحۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلۡعَظِيمِ

Saboda haka ka yi tasbihi da sunan Ubangijinka Mai girma



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 1

سَأَلَ سَآئِلُۢ بِعَذَابٖ وَاقِعٖ

Mai tambaya ya yi tambaya game da wata azaba mai aukuwa[1]


1- Watau wadda Annabi () yake musu kashedi da ita idan sun qi imani. Duba Suratul Anfal, aya ta 32. Mai tambayar kuwa shi ne Nadhru xan Haris.


Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 2

لِّلۡكَٰفِرِينَ لَيۡسَ لَهُۥ دَافِعٞ

Ga kafirai (wadda) ba ta da wani mai kaxe ta



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 3

مِّنَ ٱللَّهِ ذِي ٱلۡمَعَارِجِ

Daga Allah Mai matattakalai



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 4

تَعۡرُجُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيۡهِ فِي يَوۡمٖ كَانَ مِقۡدَارُهُۥ خَمۡسِينَ أَلۡفَ سَنَةٖ

Mala’iku tare da Jibrilu suna hawa zuwa gare Shi a cikin wata rana (wadda) gwargwadonta yake daidai da shekara dubu hamsin



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 5

فَٱصۡبِرۡ صَبۡرٗا جَمِيلًا

Sai ka yi haquri kyakkyawan haquri



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 6

إِنَّهُمۡ يَرَوۡنَهُۥ بَعِيدٗا

Lalle su suna ganin ta mai nisa ce



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 7

وَنَرَىٰهُ قَرِيبٗا

Mu kuma Muna ganin ta kusa-kusa



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 8

يَوۡمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلۡمُهۡلِ

A ranar da sama za ta kasance kamar narkakkiyar dalma



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 9

وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ

Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga (ta gashin tumaki)



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 10

وَلَا يَسۡـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمٗا

Kuma aboki ba ya tambayar aboki



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 11

يُبَصَّرُونَهُمۡۚ يَوَدُّ ٱلۡمُجۡرِمُ لَوۡ يَفۡتَدِي مِنۡ عَذَابِ يَوۡمِئِذِۭ بِبَنِيهِ

(Alhali kuma) ana nuna musu junansu. Mai laifi ya riqa burin ina ma zai fanshi kansa daga azabar wannan rana da ‘ya’yansa



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 12

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ

Da matarsa da xan’uwansa



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 13

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِي تُـٔۡوِيهِ

Da danginsa waxanda suke kare shi



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 14

وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ يُنجِيهِ

Da ma duk wanda yake a bayan qasa baki xaya, sannan (fansar) ta tserar da shi



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 15

كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Faufau! Lalle ita (wutar) Laza ce



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 16

نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ

Mai xaxxaye fatar kai