Surah: Suratun Najm

Ayah : 42

وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلۡمُنتَهَىٰ

“Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makoma



Surah: Suratun Najm

Ayah : 43

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَضۡحَكَ وَأَبۡكَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ya sa a yi dariya, kuma Ya sa a yi kuka



Surah: Suratun Najm

Ayah : 44

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَمَاتَ وَأَحۡيَا

“Kuma lalle Shi ne Ya kashe kuma Ya raya



Surah: Suratun Najm

Ayah : 45

وَأَنَّهُۥ خَلَقَ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ya halicci dangi biyu namiji da mace



Surah: Suratun Najm

Ayah : 46

مِن نُّطۡفَةٍ إِذَا تُمۡنَىٰ

“Daga maniyyi yayin da ake zuba shi



Surah: Suratun Najm

Ayah : 47

وَأَنَّ عَلَيۡهِ ٱلنَّشۡأَةَ ٱلۡأُخۡرَىٰ

“Kuma lalle Ya xora wa kansa sake tashin matattu



Surah: Suratun Najm

Ayah : 48

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَغۡنَىٰ وَأَقۡنَىٰ

“Lalle kuma Shi ne Ya wadata, Ya kuma yalwata



Surah: Suratun Najm

Ayah : 49

وَأَنَّهُۥ هُوَ رَبُّ ٱلشِّعۡرَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ubangijin tauraron nan Shi’ira



Surah: Suratun Najm

Ayah : 50

وَأَنَّهُۥٓ أَهۡلَكَ عَادًا ٱلۡأُولَىٰ

“Lalle kuma Ya hallakar da Adawa na farko



Surah: Suratun Najm

Ayah : 51

وَثَمُودَاْ فَمَآ أَبۡقَىٰ

“Da kuma Samudawa, don haka bai bar saura ba



Surah: Suratun Najm

Ayah : 52

وَقَوۡمَ نُوحٖ مِّن قَبۡلُۖ إِنَّهُمۡ كَانُواْ هُمۡ أَظۡلَمَ وَأَطۡغَىٰ

“Da mutanen Nuhu tun kafin su; lalle su sun kasance su ne mafiya zalunci kuma mafiya xagawa



Surah: Suratun Najm

Ayah : 53

وَٱلۡمُؤۡتَفِكَةَ أَهۡوَىٰ

“Da waxanda aka kife (mutanen Luxu, Allah) ya qasqanta su



Surah: Suratun Najm

Ayah : 54

فَغَشَّىٰهَا مَا غَشَّىٰ

“Sannan abin da ya lulluve su (na azaba) ya lulluve su.”



Surah: Suratun Najm

Ayah : 55

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ

To (kai xan’adam) da waxanne ni’imomin Ubangijinka kake jayayya?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 56

هَٰذَا نَذِيرٞ مِّنَ ٱلنُّذُرِ ٱلۡأُولَىٰٓ

Wannan mai gargaxi ne daga irin masu gargaxin farko



Surah: Suratun Najm

Ayah : 57

أَزِفَتِ ٱلۡأٓزِفَةُ

Mai kusantowa ta kusanto (watau alqiyama)



Surah: Suratun Najm

Ayah : 58

لَيۡسَ لَهَا مِن دُونِ ٱللَّهِ كَاشِفَةٌ

Ba wani mai bayyana lokacinta in ban da Allah



Surah: Suratun Najm

Ayah : 59

أَفَمِنۡ هَٰذَا ٱلۡحَدِيثِ تَعۡجَبُونَ

Yanzu game da wannan zancen ne[1] kuke mamaki?


1- Watau Alqur’ani mai girma.


Surah: Suratun Najm

Ayah : 60

وَتَضۡحَكُونَ وَلَا تَبۡكُونَ

Kuke kuma dariya ba kwa yin kuka?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 61

وَأَنتُمۡ سَٰمِدُونَ

Alhali kuna cikin gafala?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 62

فَٱسۡجُدُواْۤ لِلَّهِۤ وَٱعۡبُدُواْ۩

To ku yi sujjada ga Allah ku kuma bauta (masa)



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 1

ٱقۡتَرَبَتِ ٱلسَّاعَةُ وَٱنشَقَّ ٱلۡقَمَرُ

Alqiyama ta kusanto, wata kuma ya tsage[1]


1- Watau a zamanin Manzon Allah () wanda mushirikan Quraishawa suka gani da idonsu, bayan sun nemi ya nuna musu mu’ujiza.


Surah: Suratul Qamar

Ayah : 2

وَإِن يَرَوۡاْ ءَايَةٗ يُعۡرِضُواْ وَيَقُولُواْ سِحۡرٞ مُّسۡتَمِرّٞ

Idan kuma suka ga wata aya sai su kau da kai kuma su ce: “Wannan sihiri ne qaqqarfa.”



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 3

وَكَذَّبُواْ وَٱتَّبَعُوٓاْ أَهۡوَآءَهُمۡۚ وَكُلُّ أَمۡرٖ مُّسۡتَقِرّٞ

Suka kuma qaryata, suka bi soye-soyen zukatansu. Kowane al’amari kuwa (na alheri ko na sharri) mai tabbata ne



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 4

وَلَقَدۡ جَآءَهُم مِّنَ ٱلۡأَنۢبَآءِ مَا فِيهِ مُزۡدَجَرٌ

Haqiqa kuma wasu labarai waxanda tsawatarwa take cikinsu sun zo musu



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 5

حِكۡمَةُۢ بَٰلِغَةٞۖ فَمَا تُغۡنِ ٱلنُّذُرُ

Hikima ce mai kaiwa matuqa, sai dai kuma gargaxin ba ya amfanarwa



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 6

فَتَوَلَّ عَنۡهُمۡۘ يَوۡمَ يَدۡعُ ٱلدَّاعِ إِلَىٰ شَيۡءٖ نُّكُرٍ

Saboda haka ka rabu da su. A ranar da mai kira[1] zai yi kira zuwa ga wani abu na qi a rai[2]


1- Shi ne Mala’ika Israfilu () mai busa a qaho.


2- Watau lokacin fitowa daga qaburbura.


Surah: Suratul Qamar

Ayah : 7

خُشَّعًا أَبۡصَٰرُهُمۡ يَخۡرُجُونَ مِنَ ٱلۡأَجۡدَاثِ كَأَنَّهُمۡ جَرَادٞ مُّنتَشِرٞ

Idanuwansu suna a qasqance suna fitowa daga qaburbura, kai ka ce su farin xango ne masu bazuwa



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 8

مُّهۡطِعِينَ إِلَى ٱلدَّاعِۖ يَقُولُ ٱلۡكَٰفِرُونَ هَٰذَا يَوۡمٌ عَسِرٞ

Suna gaggawa zuwa ga mai kiran; kafirai za su riqa cewa: “Wannan rana ce mai tsanani.”



Surah: Suratul Qamar

Ayah : 9

۞كَذَّبَتۡ قَبۡلَهُمۡ قَوۡمُ نُوحٖ فَكَذَّبُواْ عَبۡدَنَا وَقَالُواْ مَجۡنُونٞ وَٱزۡدُجِرَ

Mutanen Nuhu sun qaryata kafin su (Quraishawa), sai suka qaryata Bawanmu suka kuma ce, mahaukaci ne, aka kuma kyare (shi)