Surah: Suratun Nahl

Ayah : 22

إِلَٰهُكُمۡ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞۚ فَٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ قُلُوبُهُم مُّنكِرَةٞ وَهُم مُّسۡتَكۡبِرُونَ

Abin bautarku Abin bauta ne Xaya, sai dai waxanda ba sa yin imani da ranar lahira zukatansu masu musun hakan ne, kuma su masu girman kai ne



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 23

لَا جَرَمَ أَنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُ مَا يُسِرُّونَ وَمَا يُعۡلِنُونَۚ إِنَّهُۥ لَا يُحِبُّ ٱلۡمُسۡتَكۡبِرِينَ

Ba shakka, lalle Allah Yana sane da abin da suke voyewa da abin da suke bayyanawa. Lalle Shi ba Ya son masu girman kai



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 24

وَإِذَا قِيلَ لَهُم مَّاذَآ أَنزَلَ رَبُّكُمۡ قَالُوٓاْ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Idan kuma aka ce da su: “Me Ubangijinku Ya saukar?” (Sai) su ce: “Tatsuniyoyin mutanen farko.”



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 25

لِيَحۡمِلُوٓاْ أَوۡزَارَهُمۡ كَامِلَةٗ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ وَمِنۡ أَوۡزَارِ ٱلَّذِينَ يُضِلُّونَهُم بِغَيۡرِ عِلۡمٍۗ أَلَا سَآءَ مَا يَزِرُونَ

(Wannan kuwa) don su xauki laifukansu cikakku ranar alqiyama, da kuma laifukan waxanda suke vatarwa ba da ilimi ba. Ku saurara, abin da suke xauka ya munana!



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 26

قَدۡ مَكَرَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ فَأَتَى ٱللَّهُ بُنۡيَٰنَهُم مِّنَ ٱلۡقَوَاعِدِ فَخَرَّ عَلَيۡهِمُ ٱلسَّقۡفُ مِن فَوۡقِهِمۡ وَأَتَىٰهُمُ ٱلۡعَذَابُ مِنۡ حَيۡثُ لَا يَشۡعُرُونَ

Haqiqa waxanda suka gabace su sun shirya makirci, sai Allah Ya tumvuke gininsu daga harsashi, sai rufin ya rifto a kansu daga samansu, azaba kuma ta zo musu ta inda ba sa tsammani



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 27

ثُمَّ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ يُخۡزِيهِمۡ وَيَقُولُ أَيۡنَ شُرَكَآءِيَ ٱلَّذِينَ كُنتُمۡ تُشَـٰٓقُّونَ فِيهِمۡۚ قَالَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡعِلۡمَ إِنَّ ٱلۡخِزۡيَ ٱلۡيَوۡمَ وَٱلسُّوٓءَ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ

Sannan kuma ranar alqiyama (Allah) zai kunyata su kuma zai ce: “Ina abokan tarayyar nawa da kuka zamanto kuna jayayya a game da su?” (Sai) waxanda aka bai wa ilimi su ce: “Lalle a yau wulaqanci da mummunar azaba sun tabbata a kan kafirai.”



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 28

ٱلَّذِينَ تَتَوَفَّىٰهُمُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ ظَالِمِيٓ أَنفُسِهِمۡۖ فَأَلۡقَوُاْ ٱلسَّلَمَ مَا كُنَّا نَعۡمَلُ مِن سُوٓءِۭۚ بَلَىٰٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمُۢ بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Waxanda mala’iku suke karvar ransu suna masu zaluntar kawunansu; sai suka ba da kai (suna cewa,): “Ba mu kasance muna yin wani mummunan aiki ba.” A’a, ba haka ba ne, lalle Allah Masanin abin da kuka zamanto kuna aikatawa ne



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 29

فَٱدۡخُلُوٓاْ أَبۡوَٰبَ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَاۖ فَلَبِئۡسَ مَثۡوَى ٱلۡمُتَكَبِّرِينَ

“Sai ku shiga qofofin Jahannama kuna masu dawwama a cikinta; lalle makomar masu girman kai ta munana.”



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 30

۞وَقِيلَ لِلَّذِينَ ٱتَّقَوۡاْ مَاذَآ أَنزَلَ رَبُّكُمۡۚ قَالُواْ خَيۡرٗاۗ لِّلَّذِينَ أَحۡسَنُواْ فِي هَٰذِهِ ٱلدُّنۡيَا حَسَنَةٞۚ وَلَدَارُ ٱلۡأٓخِرَةِ خَيۡرٞۚ وَلَنِعۡمَ دَارُ ٱلۡمُتَّقِينَ

Aka kuma ce da waxanda suka kiyaye dokokin (Allah): “Me Ubangijinku Ya sauqar?” Suka ce: “Alheri.” Waxanda suka kyautata a wannan duniya suna da kyakkyawar (rayuwa). Lalle kuma gidan lahira shi ya fi alheri. Madalla da gidan masu taqawa



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 31

جَنَّـٰتُ عَدۡنٖ يَدۡخُلُونَهَا تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۖ لَهُمۡ فِيهَا مَا يَشَآءُونَۚ كَذَٰلِكَ يَجۡزِي ٱللَّهُ ٱلۡمُتَّقِينَ

Aljannatai ne na jin daxi za su shige su, qoramu suna gudana ta qarqashinsu; suna da duk abin da suka ga dama cikinsu. Kamar haka Allah Yake saka wa masu taqawa



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 32

ٱلَّذِينَ تَتَوَفَّىٰهُمُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ طَيِّبِينَ يَقُولُونَ سَلَٰمٌ عَلَيۡكُمُ ٱدۡخُلُواْ ٱلۡجَنَّةَ بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Waxanda mala’iku suke xaukar ransu suna tsarkaka, suna cewa: “Aminci ya tabbata a gare ku, ku shiga Aljanna saboda abin da kuka zamanto kuna aikatawa (a duniya)



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 33

هَلۡ يَنظُرُونَ إِلَّآ أَن تَأۡتِيَهُمُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ أَوۡ يَأۡتِيَ أَمۡرُ رَبِّكَۚ كَذَٰلِكَ فَعَلَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡۚ وَمَا ظَلَمَهُمُ ٱللَّهُ وَلَٰكِن كَانُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Shin akwai abin da (mushrikai) suke sauraro in ban da mala’iku su zo musu, ko kuma umarnin Ubangijinka ya zo? Kamar haka waxanda ke gabaninsu suka aikata. Allah bai zalunce su ba, sai dai kuma kawunansu suka kasance suna zalunta



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 34

فَأَصَابَهُمۡ سَيِّـَٔاتُ مَا عَمِلُواْ وَحَاقَ بِهِم مَّا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ

Sai (sakamakon) mummunan abin da suka aikata ya same su, kuma abin da suke yi wa izgili ya rutsa da su



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 35

وَقَالَ ٱلَّذِينَ أَشۡرَكُواْ لَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ مَا عَبَدۡنَا مِن دُونِهِۦ مِن شَيۡءٖ نَّحۡنُ وَلَآ ءَابَآؤُنَا وَلَا حَرَّمۡنَا مِن دُونِهِۦ مِن شَيۡءٖۚ كَذَٰلِكَ فَعَلَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡۚ فَهَلۡ عَلَى ٱلرُّسُلِ إِلَّا ٱلۡبَلَٰغُ ٱلۡمُبِينُ

Waxanda kuma suka yi shirka suka ce: “Da Allah Ya ga dama da ba mu bauta wa komai ba sai Shi, daga mu har iyayenmu, da kuma ba mu haramta komai ba wanda bai haramta ba.” Kamar haka waxanda suka gabace su suka aikata. Shin akwai abin da yake a kan manzanni in ban da isar da aike a fili?



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 36

وَلَقَدۡ بَعَثۡنَا فِي كُلِّ أُمَّةٖ رَّسُولًا أَنِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ وَٱجۡتَنِبُواْ ٱلطَّـٰغُوتَۖ فَمِنۡهُم مَّنۡ هَدَى ٱللَّهُ وَمِنۡهُم مَّنۡ حَقَّتۡ عَلَيۡهِ ٱلضَّلَٰلَةُۚ فَسِيرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَٱنظُرُواْ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُكَذِّبِينَ

Haqiqa kuma Mun aiko manzo a kowacce al’umma cewa,: “Ku bauta wa Allah, kuma ku nisanci Xagutu[1].” To akwai daga cikinsu waxanda Allah Ya shiryar, akwai kuma daga cikinsu wanda vata ya tabbata a kansa. To ku yi tafiya a bayan qasa ku ga yadda qarshen masu qaryatawa ya kasance


1- Xagutu ana nufin duk wani abu da aka qetare iyakokin Allah saboda shi, ta hanyar bautar sa, mutum ne ko aljani ko dutse ko itace.


Surah: Suratun Nahl

Ayah : 37

إِن تَحۡرِصۡ عَلَىٰ هُدَىٰهُمۡ فَإِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي مَن يُضِلُّۖ وَمَا لَهُم مِّن نَّـٰصِرِينَ

Idan ma kana kwaxayin shiriyarsu ne, to lalle Allah fa ba Ya shiryar da wanda Ya vatar; ba su da kuma wasu mataimaka



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 38

وَأَقۡسَمُواْ بِٱللَّهِ جَهۡدَ أَيۡمَٰنِهِمۡ لَا يَبۡعَثُ ٱللَّهُ مَن يَمُوتُۚ بَلَىٰ وَعۡدًا عَلَيۡهِ حَقّٗا وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Suka kuma rantse da Allah iya rantsuwarsu, (cewa) Allah ba zai tashi wanda ya mutu ba. A’a, ba haka ba ne, alqawari ne a kansa na gaskiya, sai dai yawancin mutane ba sa sanin (haka)



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 39

لِيُبَيِّنَ لَهُمُ ٱلَّذِي يَخۡتَلِفُونَ فِيهِ وَلِيَعۡلَمَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَنَّهُمۡ كَانُواْ كَٰذِبِينَ

(Zai tashe su) don Ya bayyana musu abin da suke savani game da shi, don kuma kafirai su san cewa, su sun tabbata maqaryata



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 40

إِنَّمَا قَوۡلُنَا لِشَيۡءٍ إِذَآ أَرَدۡنَٰهُ أَن نَّقُولَ لَهُۥ كُن فَيَكُونُ

Abin da kawai Muke cewa da abu idan Mun nufe shi, sai Mu ce da shi: “Kasance”, sai kawai ya kasance



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 41

وَٱلَّذِينَ هَاجَرُواْ فِي ٱللَّهِ مِنۢ بَعۡدِ مَا ظُلِمُواْ لَنُبَوِّئَنَّهُمۡ فِي ٱلدُّنۡيَا حَسَنَةٗۖ وَلَأَجۡرُ ٱلۡأٓخِرَةِ أَكۡبَرُۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ

Waxanda kuma suka yi hijira saboda Allah bayan an zalunce su lalle za Mu shirya musu kyakkyawar (rayuwa) a duniya; ladan lahira kuma ya fi girma da a ce sun kasance suna sane da (haka)



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 42

ٱلَّذِينَ صَبَرُواْ وَعَلَىٰ رَبِّهِمۡ يَتَوَكَّلُونَ

Waxanda suka yi haquri kuma ga Ubangijinsu kawai suke dogaro



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 43

وَمَآ أَرۡسَلۡنَا مِن قَبۡلِكَ إِلَّا رِجَالٗا نُّوحِيٓ إِلَيۡهِمۡۖ فَسۡـَٔلُوٓاْ أَهۡلَ ٱلذِّكۡرِ إِن كُنتُمۡ لَا تَعۡلَمُونَ

Ba Mu tava aiko (wasu manzanni) ba a gabaninka sai mazaje waxanda Muke yi wa wahayi. Don haka ku tambayi ma’abota ilimi idan kun kasance ba ku sani ba



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 44

بِٱلۡبَيِّنَٰتِ وَٱلزُّبُرِۗ وَأَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلذِّكۡرَ لِتُبَيِّنَ لِلنَّاسِ مَا نُزِّلَ إِلَيۡهِمۡ وَلَعَلَّهُمۡ يَتَفَكَّرُونَ

(Mun aiko su) da hujjoji bayyanannu da littattafai. Mun kuma saukar maka da Alqur’ani don ka yi wa mutane bayanin abin da aka saukar musu ko sa yi tunani



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 45

أَفَأَمِنَ ٱلَّذِينَ مَكَرُواْ ٱلسَّيِّـَٔاتِ أَن يَخۡسِفَ ٱللَّهُ بِهِمُ ٱلۡأَرۡضَ أَوۡ يَأۡتِيَهُمُ ٱلۡعَذَابُ مِنۡ حَيۡثُ لَا يَشۡعُرُونَ

Yanzu waxanda suka shirya mummunan makirci ba sa gudun Allah Ya kife qasa da su, ko kuma azaba ta zo musu ta inda ba sa zato?



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 46

أَوۡ يَأۡخُذَهُمۡ فِي تَقَلُّبِهِمۡ فَمَا هُم بِمُعۡجِزِينَ

Ko kuwa Ya kama su a cikin kai-kawonsu, ba kuwa za su gagara ba?



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 47

أَوۡ يَأۡخُذَهُمۡ عَلَىٰ تَخَوُّفٖ فَإِنَّ رَبَّكُمۡ لَرَءُوفٞ رَّحِيمٌ

Ko kuma Ya kama su a lokacin da suke cike da tsoron (Sa)? To lalle Ubangijinka Mai tausayi ne, Mai jin qai



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 48

أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَىٰ مَا خَلَقَ ٱللَّهُ مِن شَيۡءٖ يَتَفَيَّؤُاْ ظِلَٰلُهُۥ عَنِ ٱلۡيَمِينِ وَٱلشَّمَآئِلِ سُجَّدٗا لِّلَّهِ وَهُمۡ دَٰخِرُونَ

Shin yanzu ba sa ganin abubuwan da Allah Ya halitta kowane iri ne, inuwowinsa suna bazuwa dama da hagu, suna masu sujjada ga Allah suna kuma masu qasqantar da kai[1]?


1- Malamai sun ce, idan rana ta gushe daga tsakiyar sama, to komai yana faxuwa ya yi sujjada ga Allah.


Surah: Suratun Nahl

Ayah : 49

وَلِلَّهِۤ يَسۡجُدُۤ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ مِن دَآبَّةٖ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَهُمۡ لَا يَسۡتَكۡبِرُونَ

Abin da yake cikin sammai da abin da yake bayan qasa na kowace dabba da mala’iku suna yin sujjada ne ga Allah, su kuma ba sa girman kai



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 50

يَخَافُونَ رَبَّهُم مِّن فَوۡقِهِمۡ وَيَفۡعَلُونَ مَا يُؤۡمَرُونَ۩

Suna tsoron Ubangijnsu daga samansu kuma suna aikata abin da ake umartar su da shi