Surah: Suratu Sad

Ayah : 53

هَٰذَا مَا تُوعَدُونَ لِيَوۡمِ ٱلۡحِسَابِ

Wannan shi ne ake yi muku alqawari da shi a ranar hisabi



Surah: Suratu Sad

Ayah : 54

إِنَّ هَٰذَا لَرِزۡقُنَا مَا لَهُۥ مِن نَّفَادٍ

Lalle wannan tabbas arzikinmu ne ba mai qarewa ba



Surah: Suratu Sad

Ayah : 55

هَٰذَاۚ وَإِنَّ لِلطَّـٰغِينَ لَشَرَّ مَـَٔابٖ

Wannan (shi ne sakamakon masu taqawa). Kuma lalle masu xagawa tabbas suna da mummunar makoma



Surah: Suratu Sad

Ayah : 56

جَهَنَّمَ يَصۡلَوۡنَهَا فَبِئۡسَ ٱلۡمِهَادُ

(Wato) Jahannama wadda za su shige ta, to wannan shimfixar zama ta munana



Surah: Suratu Sad

Ayah : 57

هَٰذَا فَلۡيَذُوقُوهُ حَمِيمٞ وَغَسَّاقٞ

Wannan (sakamako ne), sai su xanxane shi na tafasasshen ruwa da mugunya



Surah: Suratu Sad

Ayah : 58

وَءَاخَرُ مِن شَكۡلِهِۦٓ أَزۡوَٰجٌ

Da kuma wani mai kama da shi iri daban-daban



Surah: Suratu Sad

Ayah : 59

هَٰذَا فَوۡجٞ مُّقۡتَحِمٞ مَّعَكُمۡ لَا مَرۡحَبَۢا بِهِمۡۚ إِنَّهُمۡ صَالُواْ ٱلنَّارِ

(Za a ce da su): “Wannan ma wani gungun ne (na mabiya) mai afkawa tare da ku;” (sai shugabannin su ce): “Ba ma yin maraba da su.” Lalle (su duka) wuta za su shiga



Surah: Suratu Sad

Ayah : 60

قَالُواْ بَلۡ أَنتُمۡ لَا مَرۡحَبَۢا بِكُمۡۖ أَنتُمۡ قَدَّمۡتُمُوهُ لَنَاۖ فَبِئۡسَ ٱلۡقَرَارُ

(Mabiyan kuma sai) su ce: “A’a, ku dai ne ba ma maraba da ku; ku ne kuka kawo mana shi (wannan mummunan sakamako);” to wannan matabbata ta munana



Surah: Suratu Sad

Ayah : 61

قَالُواْ رَبَّنَا مَن قَدَّمَ لَنَا هَٰذَا فَزِدۡهُ عَذَابٗا ضِعۡفٗا فِي ٱلنَّارِ

Sai suka ce: “Ya Ubangijinmu, duk wanda ya kawo mana wannan (sakamakon) to Ka qara masa ninkin azaba a cikin wuta.”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 62

وَقَالُواْ مَا لَنَا لَا نَرَىٰ رِجَالٗا كُنَّا نَعُدُّهُم مِّنَ ٱلۡأَشۡرَارِ

Suka kuma ce: “Me ya sa ne ba ma ganin wasu mazaje[1] da muka kasance muna lissafa su cikin ashararai?


1- Suna nufin muminai waxanda suka riqa yi wa izgili a duniya, suna musu kallon vatattu.


Surah: Suratu Sad

Ayah : 63

أَتَّخَذۡنَٰهُمۡ سِخۡرِيًّا أَمۡ زَاغَتۡ عَنۡهُمُ ٱلۡأَبۡصَٰرُ

“Shin mun xauke su ne ababen yi wa ba’a (a duniya), ko kuwa idanuwanmu ne suka bauxe ba sa hango su?”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 64

إِنَّ ذَٰلِكَ لَحَقّٞ تَخَاصُمُ أَهۡلِ ٱلنَّارِ

“Shin mun xauke su ne ababen yi wa ba’a (a duniya), ko kuwa idanuwanmu ne suka bauxe ba sa hango su?”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 65

قُلۡ إِنَّمَآ أَنَا۠ مُنذِرٞۖ وَمَا مِنۡ إِلَٰهٍ إِلَّا ٱللَّهُ ٱلۡوَٰحِدُ ٱلۡقَهَّارُ

Ka ce: “Ni dai mai gargaxi ne kawai; kuma babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Allah Xaya, Mai rinjaye



Surah: Suratu Sad

Ayah : 66

رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡغَفَّـٰرُ

“Ubangijin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu, Mabuwayi, Mai gafara.”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 67

قُلۡ هُوَ نَبَؤٌاْ عَظِيمٌ

Ka ce: “Shi (wannan Alqur’ani) labari ne mai girma



Surah: Suratu Sad

Ayah : 68

أَنتُمۡ عَنۡهُ مُعۡرِضُونَ

“Da kuke bijire masa



Surah: Suratu Sad

Ayah : 69

مَا كَانَ لِيَ مِنۡ عِلۡمِۭ بِٱلۡمَلَإِ ٱلۡأَعۡلَىٰٓ إِذۡ يَخۡتَصِمُونَ

“Ban zama na san wani abu ba dangane da mala’iku masu daraja lokacin da suke yin muhawara (game da halittar Adamu)



Surah: Suratu Sad

Ayah : 70

إِن يُوحَىٰٓ إِلَيَّ إِلَّآ أَنَّمَآ أَنَا۠ نَذِيرٞ مُّبِينٌ

“Ba wani wahayi da aka yiwo min sai kawai cewa ni mai gargaxi ne mai bayyanawa.”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 71

إِذۡ قَالَ رَبُّكَ لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ إِنِّي خَٰلِقُۢ بَشَرٗا مِّن طِينٖ

(Ka tuna) lokacin da Ubangijinka Ya ce da mala’iku: “Lalle Ni zan halicci wani mutum daga tavo



Surah: Suratu Sad

Ayah : 72

فَإِذَا سَوَّيۡتُهُۥ وَنَفَخۡتُ فِيهِ مِن رُّوحِي فَقَعُواْ لَهُۥ سَٰجِدِينَ

“To idan Na daidaita shi Na kuma busa masa ruhina, sai ku faxi kuna masu yi masa sujjada.”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 73

فَسَجَدَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ كُلُّهُمۡ أَجۡمَعُونَ

Sai mala’iku dukkaninsu gaba xaya suka yi sujjada



Surah: Suratu Sad

Ayah : 74

إِلَّآ إِبۡلِيسَ ٱسۡتَكۡبَرَ وَكَانَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Sai Iblisa da ya yi girman kai ya kuma zama cikin kafirai



Surah: Suratu Sad

Ayah : 75

قَالَ يَـٰٓإِبۡلِيسُ مَا مَنَعَكَ أَن تَسۡجُدَ لِمَا خَلَقۡتُ بِيَدَيَّۖ أَسۡتَكۡبَرۡتَ أَمۡ كُنتَ مِنَ ٱلۡعَالِينَ

(Allah) Ya ce: “Ya kai Iblisa, me ya hana ka yin sujjada ga abin da Na halitta da hannayena biyu? Ka yi girman kai ne, ko kuwa da man can ka kasance daga masu nuna isa?”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 76

قَالَ أَنَا۠ خَيۡرٞ مِّنۡهُ خَلَقۡتَنِي مِن نَّارٖ وَخَلَقۡتَهُۥ مِن طِينٖ

Sai ya ce: “Ni ai na fi shi; (domin) Ka halicce ni ne daga wuta, (shi) kuma Ka halicce shi daga tavo.”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 77

قَالَ فَٱخۡرُجۡ مِنۡهَا فَإِنَّكَ رَجِيمٞ

(Sai Allah) Ya ce (da shi): “To ka fice daga cikinta (wato Aljanna) saboda kai lalle korarre ne (daga rahama)



Surah: Suratu Sad

Ayah : 78

وَإِنَّ عَلَيۡكَ لَعۡنَتِيٓ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلدِّينِ

“Kuma lalle la’antata tabbas ta hau kanka har zuwa ranar alqiyama.”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 79

قَالَ رَبِّ فَأَنظِرۡنِيٓ إِلَىٰ يَوۡمِ يُبۡعَثُونَ

(Sai Iblisa) ya ce: “Ya Ubangijina, Ka saurara min har zuwa ranar da za a tashe su.”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 80

قَالَ فَإِنَّكَ مِنَ ٱلۡمُنظَرِينَ

(Sai Allah) Ya ce: “To lalle kana cikin waxanda za a saurara wa



Surah: Suratu Sad

Ayah : 81

إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡوَقۡتِ ٱلۡمَعۡلُومِ

“Har zuwa ranar lokaci sananne.”



Surah: Suratu Sad

Ayah : 82

قَالَ فَبِعِزَّتِكَ لَأُغۡوِيَنَّهُمۡ أَجۡمَعِينَ

Sai ya ce: “To na rantse da girmanka tabbas zan vatar da su baki xaya