Surah: Suratu Yusuf 

Ayah : 51

قَالَ مَا خَطۡبُكُنَّ إِذۡ رَٰوَدتُّنَّ يُوسُفَ عَن نَّفۡسِهِۦۚ قُلۡنَ حَٰشَ لِلَّهِ مَا عَلِمۡنَا عَلَيۡهِ مِن سُوٓءٖۚ قَالَتِ ٱمۡرَأَتُ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡـَٰٔنَ حَصۡحَصَ ٱلۡحَقُّ أَنَا۠ رَٰوَدتُّهُۥ عَن نَّفۡسِهِۦ وَإِنَّهُۥ لَمِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

(Sarki) ya ce: “Mene ne labarinku lokacin da kuka nemi Yusufu da lalata?” Suka ce: “Tsarki ya tabbata ga Allah; ba mu san wani mummunan abu game da shi ba.” Matar Azizu ta ce: “Yanzu kam gaskiya ta bayyana; ni ce da kaina na nemi lalata da shi; lalle kuma shi yana cikin masu gaskiya



Surah: Suratu Yusuf 

Ayah : 52

ذَٰلِكَ لِيَعۡلَمَ أَنِّي لَمۡ أَخُنۡهُ بِٱلۡغَيۡبِ وَأَنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي كَيۡدَ ٱلۡخَآئِنِينَ

“Wannan kuwa don ya san cewa ni ban ha’ince shi a bayan idonsa ba, kuma lalle Allah ba Ya shiryar da makircin masu ha’inci