Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 171

إِلَّا عَجُوزٗا فِي ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai fa wata tsohuwa (watau matarsa) da ta (kasance tana) cikin hallakakku



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 172

ثُمَّ دَمَّرۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka hallaka sauran



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 173

وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِم مَّطَرٗاۖ فَسَآءَ مَطَرُ ٱلۡمُنذَرِينَ

Muka kuma saukar musu da ruwa na azaba; to ruwan azabar waxanda aka yi wa gargaxi ya munana



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 174

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; yawancinsu kuwa ba su zamanto muminai ba



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 175

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangiijnka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 176

كَذَّبَ أَصۡحَٰبُ لۡـَٔيۡكَةِ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Mutanen kurmi sun qaryata manzanni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 177

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ شُعَيۡبٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da Shu’aibu ya ce da su: “Yanzu ba kwa kiyaye dokokin (Allah) ba?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 178

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce gare ku



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 179

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 180

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 181

۞أَوۡفُواْ ٱلۡكَيۡلَ وَلَا تَكُونُواْ مِنَ ٱلۡمُخۡسِرِينَ

“Ku cika mudu kada kuma ku zamanto daga masu tauye (shi)



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 182

وَزِنُواْ بِٱلۡقِسۡطَاسِ ٱلۡمُسۡتَقِيمِ

“Kuma ku riqa yin awon nauyi da ma’auni na adalci



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 183

وَلَا تَبۡخَسُواْ ٱلنَّاسَ أَشۡيَآءَهُمۡ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

“Kada kuma ku tauye wa mutane kayayyakinsu, kuma kada ku yawaita varna a bayan qasa



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 184

وَٱتَّقُواْ ٱلَّذِي خَلَقَكُمۡ وَٱلۡجِبِلَّةَ ٱلۡأَوَّلِينَ

“Kuma ku kiyaye dokokin (Allah) wanda Ya halicce ku da kuma al’ummu na farko.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 185

قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ

Suka ce: “Kai dai kana daga waxanda aka sihirce ne kawai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 186

وَمَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ ٱلۡكَٰذِبِينَ

“Kuma kai ba kowa ba ne sai mutum kamarmu, kuma ma lalle muna zaton kana daga maqaryata!



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 187

فَأَسۡقِطۡ عَلَيۡنَا كِسَفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

“Sai ka jeho mana da yankuna (na azaba) daga sama in ka kasance daga masu gaskiya!”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 188

قَالَ رَبِّيٓ أَعۡلَمُ بِمَا تَعۡمَلُونَ

(Shu’aibu) Ya ce: “Ubangijina Ya fi kowa sanin abin da kuke aikatawa.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 189

فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمۡ عَذَابُ يَوۡمِ ٱلظُّلَّةِۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٍ

Sai suka qaryata shi, sannan sai azabar yinin girgije (na wuta) ta kama su. Lalle ta kasance azabar wani yini ne mai girma



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 190

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; sai dai kuma yawancinsu ba su kasance muminai ba



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 191

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai rahama



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 192

وَإِنَّهُۥ لَتَنزِيلُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Kuma lalle shi (Alqur’ani) saukarwa ce ta Ubangijin talikai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 193

نَزَلَ بِهِ ٱلرُّوحُ ٱلۡأَمِينُ

Ruhi amintacce (watau Jibrilu) ne ya sauko da shi



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 194

عَلَىٰ قَلۡبِكَ لِتَكُونَ مِنَ ٱلۡمُنذِرِينَ

A bisa zuciyarka don ka zamanto daga masu gargaxi



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 195

بِلِسَانٍ عَرَبِيّٖ مُّبِينٖ

(Ya saukar da shi) da harshen Larabci mabayyani



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 196

وَإِنَّهُۥ لَفِي زُبُرِ ٱلۡأَوَّلِينَ

Kuma lalle shi yana daga cikin littattafan farko



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 197

أَوَلَمۡ يَكُن لَّهُمۡ ءَايَةً أَن يَعۡلَمَهُۥ عُلَمَـٰٓؤُاْ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Yanzu bai ishe su aya ba cewa, malaman Banu- Isra’ila sun san shi?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 198

وَلَوۡ نَزَّلۡنَٰهُ عَلَىٰ بَعۡضِ ٱلۡأَعۡجَمِينَ

Da kuwa Mun saukar da shi ga wani wanda ba Balarabe ba



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 199

فَقَرَأَهُۥ عَلَيۡهِم مَّا كَانُواْ بِهِۦ مُؤۡمِنِينَ

Sannan ya karanta musu shi, to da ba za su yi imani da shi ba



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 200

كَذَٰلِكَ سَلَكۡنَٰهُ فِي قُلُوبِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Kamar haka ne Muka shigar da shi (qaryata Annabi) cikin zukatan manyan masu laifi