Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 54

فَٱسۡتَخَفَّ قَوۡمَهُۥ فَأَطَاعُوهُۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمٗا فَٰسِقِينَ

Sai ya yi wasa da hankalin mutanensa sai suka bi shi. Lalle su sun kasance mutane ne fasiqai



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 55

فَلَمَّآ ءَاسَفُونَا ٱنتَقَمۡنَا مِنۡهُمۡ فَأَغۡرَقۡنَٰهُمۡ أَجۡمَعِينَ

To lokacin da suka fusata Mu sai Muka saukar musu da uquba, Muka nutsar da su ga baki xaya



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 56

فَجَعَلۡنَٰهُمۡ سَلَفٗا وَمَثَلٗا لِّلۡأٓخِرِينَ

Sai Muka sanya su ja-gaba (wajen hallakarwa), kuma wa’azi ga na baya



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 57

۞وَلَمَّا ضُرِبَ ٱبۡنُ مَرۡيَمَ مَثَلًا إِذَا قَوۡمُكَ مِنۡهُ يَصِدُّونَ

Lokacin da kuwa aka buga misali da (Isa) xan Maryamu, sai ga mutanenka suna ta annashawa game da shi[1]


1- Watau lokacin da Abdullahi xan Az-Ziba’ara ya ji faxar Allah cewa, waxanda aka bautawa ba Allah ba za su shiga wuta tare da masu bautarsu, sai ya ce, to idan haka ne Annabi Isa ma zai shiga wuta, wannan magana tasa ta faranta wa mushirikai rai sosai.


Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 58

وَقَالُوٓاْ ءَأَٰلِهَتُنَا خَيۡرٌ أَمۡ هُوَۚ مَا ضَرَبُوهُ لَكَ إِلَّا جَدَلَۢاۚ بَلۡ هُمۡ قَوۡمٌ خَصِمُونَ

Suka kuma ce: “Yanzu ababen bautar mu ne suka fi ko kuwa shi (Isa)?” Ba su buga maka misali da shi ba sai don son jayayya. Ba shakka su dai mutane ne masu tsananin jayayya



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 59

إِنۡ هُوَ إِلَّا عَبۡدٌ أَنۡعَمۡنَا عَلَيۡهِ وَجَعَلۡنَٰهُ مَثَلٗا لِّبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Shi (Isa) ba wani ba ne face bawa ne da Muka yi masa ni’ima, Muka kuma sanya shi abin buga misali ga Bani-Isra’ila



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 60

وَلَوۡ نَشَآءُ لَجَعَلۡنَا مِنكُم مَّلَـٰٓئِكَةٗ فِي ٱلۡأَرۡضِ يَخۡلُفُونَ

Da kuma za Mu ga dama tabbas da Mun sanya mala’iku ne za su maye gurbinku a bayan qasa



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 61

وَإِنَّهُۥ لَعِلۡمٞ لِّلسَّاعَةِ فَلَا تَمۡتَرُنَّ بِهَا وَٱتَّبِعُونِۚ هَٰذَا صِرَٰطٞ مُّسۡتَقِيمٞ

Lalle kuma shi (Isa) alama ce ta zuwan alqiyama[1], kada ku yi shakka game da ita, kuma ku bi Ni. Wannan ita ce hanya madaidaiciya


1- Watau lokacin da zai sauko daga sama ta biyu a qarshen zamani, kamar yadda tarin hadisan Annabi () suka tabbatar.


Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 62

وَلَا يَصُدَّنَّكُمُ ٱلشَّيۡطَٰنُۖ إِنَّهُۥ لَكُمۡ عَدُوّٞ مُّبِينٞ

Kada kuma Shaixan ya kange ku; lalle shi maqiyi ne mai bayyana (qiyyaya) a gare ku



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 63

وَلَمَّا جَآءَ عِيسَىٰ بِٱلۡبَيِّنَٰتِ قَالَ قَدۡ جِئۡتُكُم بِٱلۡحِكۡمَةِ وَلِأُبَيِّنَ لَكُم بَعۡضَ ٱلَّذِي تَخۡتَلِفُونَ فِيهِۖ فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

Lokacin da kuma Isa ya zo da hujjoji bayyanannu ya ce: “Haqiqa na zo muku da hikima, don kuma in bayyana muku sashin da kuke sassavawa cikinsa; to ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku bi ni



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 64

إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ رَبِّي وَرَبُّكُمۡ فَٱعۡبُدُوهُۚ هَٰذَا صِرَٰطٞ مُّسۡتَقِيمٞ

“Lalle Allah Shi ne Ubangijina kuma Ubangijinku, sai ku bauta masa. Wannan ita ce hanya madaidaiciya.”



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 65

فَٱخۡتَلَفَ ٱلۡأَحۡزَابُ مِنۢ بَيۡنِهِمۡۖ فَوَيۡلٞ لِّلَّذِينَ ظَلَمُواْ مِنۡ عَذَابِ يَوۡمٍ أَلِيمٍ

Sai qungiyoyi suka sassava a tsakaninsu[1]; don haka tsananin azabar yini mai raxaxi ya tabbata ga waxanda suka yi zalunci


1- Wasu suka ce shi Allah ne; wasu kuma suka ce xan Allah ne; wasu kuma suka ce shi da mahaifiyarsa duka alloli ne.


Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 66

هَلۡ يَنظُرُونَ إِلَّا ٱلسَّاعَةَ أَن تَأۡتِيَهُم بَغۡتَةٗ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

Ba abin da suke jira sai alqiyama kawai ta zo musu kwatsam, alhali ba tare da sun sani ba



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 67

ٱلۡأَخِلَّآءُ يَوۡمَئِذِۭ بَعۡضُهُمۡ لِبَعۡضٍ عَدُوٌّ إِلَّا ٱلۡمُتَّقِينَ

Masoya a wannan ranar maqiyan juna ne sai masu taqawa kaxai



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 68

يَٰعِبَادِ لَا خَوۡفٌ عَلَيۡكُمُ ٱلۡيَوۡمَ وَلَآ أَنتُمۡ تَحۡزَنُونَ

Ya ku bayina, babu wani tsoro gare ku a yau, kuma ba za ku yi baqin ciki ba



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 69

ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِـَٔايَٰتِنَا وَكَانُواْ مُسۡلِمِينَ

(Su ne) waxanda suka yi imani da ayoyinmu, suka kuma kasance Musulmi



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 70

ٱدۡخُلُواْ ٱلۡجَنَّةَ أَنتُمۡ وَأَزۡوَٰجُكُمۡ تُحۡبَرُونَ

(Za a ce da su): “Ku shiga Aljanna ku da matanku, za a faranta muku rai.”



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 71

يُطَافُ عَلَيۡهِم بِصِحَافٖ مِّن ذَهَبٖ وَأَكۡوَابٖۖ وَفِيهَا مَا تَشۡتَهِيهِ ٱلۡأَنفُسُ وَتَلَذُّ ٱلۡأَعۡيُنُۖ وَأَنتُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Ana zagayawa tsakaninsu da akusa na zinari da kofuna; a cikinta kuma akwai (duk) abin da rayuka suke sha’awa, idanuwa kuma suke jin daxin (ganinsu); ku kuma a cikinta madawwama ne



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 72

وَتِلۡكَ ٱلۡجَنَّةُ ٱلَّتِيٓ أُورِثۡتُمُوهَا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Waccan kuma ita ce Aljannar da aka gadar muku ita saboda abin da kuka kasance kuma aikatawa



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 73

لَكُمۡ فِيهَا فَٰكِهَةٞ كَثِيرَةٞ مِّنۡهَا تَأۡكُلُونَ

A cikinta kuna da `ya`yan itatuwa na marmari masu yawa, daga gare su kuma za ku riqa ci



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 74

إِنَّ ٱلۡمُجۡرِمِينَ فِي عَذَابِ جَهَنَّمَ خَٰلِدُونَ

Lalle masu manyan laifuka suna cikin azabar (wutar) Jahannama suna masu dawwama



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 75

لَا يُفَتَّرُ عَنۡهُمۡ وَهُمۡ فِيهِ مُبۡلِسُونَ

Ba a yanke musu ita (azabar), su kuwa masu yanke qaunar (fita) ne daga cikinta



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 76

وَمَا ظَلَمۡنَٰهُمۡ وَلَٰكِن كَانُواْ هُمُ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Ba Mu kuwa zalunce su ba, sai dai su ne suka kasance azzalumai



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 77

وَنَادَوۡاْ يَٰمَٰلِكُ لِيَقۡضِ عَلَيۡنَا رَبُّكَۖ قَالَ إِنَّكُم مَّـٰكِثُونَ

Suka kuma yi kiran: “Ya (kai mai tsaron wuta) Maliku, Ubangijinka Ya kashe mu mana!” Ya ce: “Lalle ku masu dawwama ne.”



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 78

لَقَدۡ جِئۡنَٰكُم بِٱلۡحَقِّ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَكُمۡ لِلۡحَقِّ كَٰرِهُونَ

Haqiqa Mun zo muku da gaskiya sai dai kuma mafiya yawanku masu qin gaskiya ne



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 79

أَمۡ أَبۡرَمُوٓاْ أَمۡرٗا فَإِنَّا مُبۡرِمُونَ

A’a, sun dai shirya wani makirci ne, Mu ma lalle Masu yin namu shirin ne



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 80

أَمۡ يَحۡسَبُونَ أَنَّا لَا نَسۡمَعُ سِرَّهُمۡ وَنَجۡوَىٰهُمۚ بَلَىٰ وَرُسُلُنَا لَدَيۡهِمۡ يَكۡتُبُونَ

Ko suna tsammanin cewa Mu ba Ma jin asirinsu da ganawarsu ne? Ba haka ba ne, manzanninmu suna tare da su suna rubutawa



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 81

قُلۡ إِن كَانَ لِلرَّحۡمَٰنِ وَلَدٞ فَأَنَا۠ أَوَّلُ ٱلۡعَٰبِدِينَ

Ka ce: “Idan da (Allah) Mai rahama zai zamanto Yana da xa, to ni ne farkon masu bauta[1].”


1- Watau shi ne farkon masu bauta wa wannan xan, domin kuwa ya zama wani sashi ne na Allah.


Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 82

سُبۡحَٰنَ رَبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ رَبِّ ٱلۡعَرۡشِ عَمَّا يَصِفُونَ

Tsarki ya tabbata ga Ubangijin sammai da qasa, Ubangiijn Al’arshi game da abin da suke siffantawa



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 83

فَذَرۡهُمۡ يَخُوضُواْ وَيَلۡعَبُواْ حَتَّىٰ يُلَٰقُواْ يَوۡمَهُمُ ٱلَّذِي يُوعَدُونَ

Sai ka bar su su yi ta kutse suna wasanni, har su haxu da ranar da ake alqawarta musu