Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 141

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Samudawa sun qaryata manzanni[1]


1- Domin qaryata Annabi Salihu () daidai yake da qaryata duk manzannin Allah, saboda saqo iri xaya suke xauke da shi.


Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 142

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ صَٰلِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da xan’uwansu Salihu ya ce da su: “Yanzu ba kwa yi taqawa ba?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 143

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce gare ku



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 144

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 145

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 146

أَتُتۡرَكُونَ فِي مَا هَٰهُنَآ ءَامِنِينَ

“Yanzu (zatonku) za a bar ku ne cikin abin da yake a nan (duniya) cikin kwanciyar hankali?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 147

فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

“(Watau) a cikin gonaki da idandunan ruwa?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 148

وَزُرُوعٖ وَنَخۡلٖ طَلۡعُهَا هَضِيمٞ

“Da shuke-shuke da dabinai masu taushin ‘ya’ya?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 149

وَتَنۡحِتُونَ مِنَ ٱلۡجِبَالِ بُيُوتٗا فَٰرِهِينَ

“Kuma kuna fafe duwatsu kuna yin gidaje kuna masu nuna qwarewa?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 150

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 151

وَلَا تُطِيعُوٓاْ أَمۡرَ ٱلۡمُسۡرِفِينَ

“Kada kuma ku bi umarnin mavarnata



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 152

ٱلَّذِينَ يُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا يُصۡلِحُونَ

“Waxanda suke varna a bayan qasa, kuma ba sa gyara.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 153

قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ

Suka ce: “Lalle kai kana daga waxanda aka sihirce ne kawai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 154

مَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا فَأۡتِ بِـَٔايَةٍ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

“Kai ba kowa ba ne sai mutum kamarmu, to ka zo mana da aya idan ka kasance daga masu gaskiya.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 155

قَالَ هَٰذِهِۦ نَاقَةٞ لَّهَا شِرۡبٞ وَلَكُمۡ شِرۡبُ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ

(Salihu) ya ce: “Wannan taguwa ce[1], tana da (ranar) shanta ku ma kuna da rana sananniya ta shanku


1- Watau a matsayin mu’ujiza ga Annabi Salihu ().


Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 156

وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٖ فَيَأۡخُذَكُمۡ عَذَابُ يَوۡمٍ عَظِيمٖ

“Kada kuwa ku shafe ta da mugun abu, sai azabar wani yini mai girma ta kama ku.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 157

فَعَقَرُوهَا فَأَصۡبَحُواْ نَٰدِمِينَ

Sai suka soke ta, sai kuwa suka wayi gari suna masu nadama



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 158

فَأَخَذَهُمُ ٱلۡعَذَابُۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Sai azaba ta kama su. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 159

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 160

كَذَّبَتۡ قَوۡمُ لُوطٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Mutanen Luxu sun qaryata manzanni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 161

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da xan’uwansu Luxu ya ce da su: “Yanzu ba kwa kiyaye dokokin Allah ba?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 162

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce gare ku



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 163

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 164

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 165

أَتَأۡتُونَ ٱلذُّكۡرَانَ مِنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Yanzu kwa riqa zaike wa maza daga halittu?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 166

وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمۡ رَبُّكُم مِّنۡ أَزۡوَٰجِكُمۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٌ عَادُونَ

“Kuma ku bar abin da Ubangijinku Ya halitta na matanku dominku? A’a, ku dai mutane ne masu qetare iyaka.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 167

قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰلُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمُخۡرَجِينَ

Suka ce: “Tabbas Luxu idan ba ka bar (faxar abin da kake faxa ba) haqiqa za ka kasance daga korarru (daga garin nan).”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 168

قَالَ إِنِّي لِعَمَلِكُم مِّنَ ٱلۡقَالِينَ

(Luxu) ya ce: “Lalle ni ina cikin masu qyamar aikin nan naku



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 169

رَبِّ نَجِّنِي وَأَهۡلِي مِمَّا يَعۡمَلُونَ

“Ya Ubangijina, Ka tserar da ni da iyalina daga (sakamakon) abin da suke aikatawa.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 170

فَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

Sai Muka tserar da shi da iyalinsa gaba xaya