Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 18

وَتَحۡسَبُهُمۡ أَيۡقَاظٗا وَهُمۡ رُقُودٞۚ وَنُقَلِّبُهُمۡ ذَاتَ ٱلۡيَمِينِ وَذَاتَ ٱلشِّمَالِۖ وَكَلۡبُهُم بَٰسِطٞ ذِرَاعَيۡهِ بِٱلۡوَصِيدِۚ لَوِ ٱطَّلَعۡتَ عَلَيۡهِمۡ لَوَلَّيۡتَ مِنۡهُمۡ فِرَارٗا وَلَمُلِئۡتَ مِنۡهُمۡ رُعۡبٗا

Za kuma ka zaci a farke suke alhali kuwa suna bacci ne. Muka kuma riqa juya su ta varin dama da kuma ta varin hagu; karensu kuwa ya shimfixa qafafunsa na gaba a mashigar kogon. Da abin ka leqa su ne to lalle da ka fita a guje, lalle kuma da ka cika da tsoron su



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 19

وَكَذَٰلِكَ بَعَثۡنَٰهُمۡ لِيَتَسَآءَلُواْ بَيۡنَهُمۡۚ قَالَ قَآئِلٞ مِّنۡهُمۡ كَمۡ لَبِثۡتُمۡۖ قَالُواْ لَبِثۡنَا يَوۡمًا أَوۡ بَعۡضَ يَوۡمٖۚ قَالُواْ رَبُّكُمۡ أَعۡلَمُ بِمَا لَبِثۡتُمۡ فَٱبۡعَثُوٓاْ أَحَدَكُم بِوَرِقِكُمۡ هَٰذِهِۦٓ إِلَى ٱلۡمَدِينَةِ فَلۡيَنظُرۡ أَيُّهَآ أَزۡكَىٰ طَعَامٗا فَلۡيَأۡتِكُم بِرِزۡقٖ مِّنۡهُ وَلۡيَتَلَطَّفۡ وَلَا يُشۡعِرَنَّ بِكُمۡ أَحَدًا

Kamar haka Muka tashe su don su riqa tambayar junansu. Wani mai tambaya daga cikinsu ya ce: “Mene ne tsawon zamanku (a nan)?” Suka ce: “Mun yi zaman yini xaya ne ko kuma rabin yini.” (Sannan kuma) suka ce: “Ubangijinku ne Ya fi sanin tsawon zaman da kuka yi, sai ku aiki xayanku da wannan kuxin naku cikin gari, sai ya duba ya ga wanne irin abinci ne ya fi tsarki, to sai ya zo muku da abin da za ku ci da shi (kuxin), kuma ya yi taka-tsantsan kada wani ya shaida ku



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 20

إِنَّهُمۡ إِن يَظۡهَرُواْ عَلَيۡكُمۡ يَرۡجُمُوكُمۡ أَوۡ يُعِيدُوكُمۡ فِي مِلَّتِهِمۡ وَلَن تُفۡلِحُوٓاْ إِذًا أَبَدٗا

“Lalle idan suka yi galaba a kanku to za su jefe ku ko kuma su mai da ku cikin addininsu, to shi ke nan ba za ku rabauta ba har abada.”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 21

وَكَذَٰلِكَ أَعۡثَرۡنَا عَلَيۡهِمۡ لِيَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٞ وَأَنَّ ٱلسَّاعَةَ لَا رَيۡبَ فِيهَآ إِذۡ يَتَنَٰزَعُونَ بَيۡنَهُمۡ أَمۡرَهُمۡۖ فَقَالُواْ ٱبۡنُواْ عَلَيۡهِم بُنۡيَٰنٗاۖ رَّبُّهُمۡ أَعۡلَمُ بِهِمۡۚ قَالَ ٱلَّذِينَ غَلَبُواْ عَلَىٰٓ أَمۡرِهِمۡ لَنَتَّخِذَنَّ عَلَيۡهِم مَّسۡجِدٗا

Kamar haka kuwa Muka nuna wa (mutanen nasu) su don su san cewa lalle alqawarin Allah gaskiya ne, kuma ita alqiyama babu kokwanto a cikinta, kuma ka tuna lokacin da su (mutanen) suke ta jayayya a tsakaninsu game da al’amarinsu (watau samarin); sai (wasu daga cikinsu) suka ce: “Ku tayar da gini a kansu (wanda zai toshe qofar kogon).” Ubangijinsu Shi Ya fi sanin lamarinsu. Waxanda suka yi rinjaye kan al’amarinsu suka ce: “Lalle tabbas za mu yi masallaci a kansu (watau a kan qabarinsu)[1].”


1- Wannan magana ce ta masu iko a garin, ba ta masu ilimi ba. Musulunci yah ana gina masallaci a maqabarta ko salla a kan qabari ko ana fuskantar sa.


Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 22

سَيَقُولُونَ ثَلَٰثَةٞ رَّابِعُهُمۡ كَلۡبُهُمۡ وَيَقُولُونَ خَمۡسَةٞ سَادِسُهُمۡ كَلۡبُهُمۡ رَجۡمَۢا بِٱلۡغَيۡبِۖ وَيَقُولُونَ سَبۡعَةٞ وَثَامِنُهُمۡ كَلۡبُهُمۡۚ قُل رَّبِّيٓ أَعۡلَمُ بِعِدَّتِهِم مَّا يَعۡلَمُهُمۡ إِلَّا قَلِيلٞۗ فَلَا تُمَارِ فِيهِمۡ إِلَّا مِرَآءٗ ظَٰهِرٗا وَلَا تَسۡتَفۡتِ فِيهِم مِّنۡهُمۡ أَحَدٗا

(Wasu) suka riqa cewa su uku ne na huxunsu shi ne karensu; (wasu) kuma suna cewa biyar ne na shidansu ne karensu don lalube cikin duhu; (wasu) kuma suna cewa su bakwai ne na takwas xinsu kuma karensu ne. Ka ce (da su): “Ubangiji Shi Ya fi sanin yawansu, ba wanda ya san lamarinsu sai ‘yan kaxan.” To kada ka yi jayayya game da (al’amarinsu) sai dai a kan abin da yake a fili, kada kuma ka nemi fatawar xaya daga cikinsu game da su (samarin)



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 23

وَلَا تَقُولَنَّ لِشَاْيۡءٍ إِنِّي فَاعِلٞ ذَٰلِكَ غَدًا

Kada kuma ka ce da kowane abu: “Lalle zan aikata wannan gobe.”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 24

إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ وَٱذۡكُر رَّبَّكَ إِذَا نَسِيتَ وَقُلۡ عَسَىٰٓ أَن يَهۡدِيَنِ رَبِّي لِأَقۡرَبَ مِنۡ هَٰذَا رَشَدٗا

Sai dai (tare da cewa): ‘In sha Allah’; ka kuma ambaci Ubangijinka idan ka manta, kuma ka ce: “Ina fatan Ubangijina Ya nuna mini abin da ya fi wannan zama shiriya.”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 25

وَلَبِثُواْ فِي كَهۡفِهِمۡ ثَلَٰثَ مِاْئَةٖ سِنِينَ وَٱزۡدَادُواْ تِسۡعٗا

Sun kuwa zauna cikin kogonsu shekara xari uku, suka kuma qara tara[1]


1- A lissafin shekarar shamsiyya, watau lissafi da fitowar rana da faxuwarta shi ne 300. A lissafin qamariyya kuwa, watau lissafin ganin wata shi ne 309.


Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 26

قُلِ ٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا لَبِثُواْۖ لَهُۥ غَيۡبُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ أَبۡصِرۡ بِهِۦ وَأَسۡمِعۡۚ مَا لَهُم مِّن دُونِهِۦ مِن وَلِيّٖ وَلَا يُشۡرِكُ فِي حُكۡمِهِۦٓ أَحَدٗا

Ka ce: “Allah ne Mafi sanin tsawon zaman da suka yi.” Gaibun da yake sammai da qasa nasa ne. Wa ya yi gani irin nasa, wa kuma ya yi ji irin nasa (watau Allah). Ba su da wani majivinci in ban da Shi; ba Ya kuma tarayya da wani a cikin hukuncinsa



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 27

وَٱتۡلُ مَآ أُوحِيَ إِلَيۡكَ مِن كِتَابِ رَبِّكَۖ لَا مُبَدِّلَ لِكَلِمَٰتِهِۦ وَلَن تَجِدَ مِن دُونِهِۦ مُلۡتَحَدٗا

Kuma ka karanta abin da aka yiwo maka wahayi da shi daga littafin Ubangijinka: Ba mai canja kalmominsa; ba kuma za ka sami wata mafaka ba in ba ta wurinsa ba



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 28

وَٱصۡبِرۡ نَفۡسَكَ مَعَ ٱلَّذِينَ يَدۡعُونَ رَبَّهُم بِٱلۡغَدَوٰةِ وَٱلۡعَشِيِّ يُرِيدُونَ وَجۡهَهُۥۖ وَلَا تَعۡدُ عَيۡنَاكَ عَنۡهُمۡ تُرِيدُ زِينَةَ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۖ وَلَا تُطِعۡ مَنۡ أَغۡفَلۡنَا قَلۡبَهُۥ عَن ذِكۡرِنَا وَٱتَّبَعَ هَوَىٰهُ وَكَانَ أَمۡرُهُۥ فُرُطٗا

Ka kuma haqurqurtar da kanka (da zama) tare da waxanda suke bauta wa Ubangijinsu safe da yamma suna neman yardarsa; kar kuma ka kawar da idanuwanka daga gare su kana neman adon rayuwar duniya; kada kuma ka bi wanda Muka shagaltar da zuciyarsa daga ambatonmu ya kuma bi son ransa, wanda kuma al’amarinsa ya zama a sukurkuce



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 29

وَقُلِ ٱلۡحَقُّ مِن رَّبِّكُمۡۖ فَمَن شَآءَ فَلۡيُؤۡمِن وَمَن شَآءَ فَلۡيَكۡفُرۡۚ إِنَّآ أَعۡتَدۡنَا لِلظَّـٰلِمِينَ نَارًا أَحَاطَ بِهِمۡ سُرَادِقُهَاۚ وَإِن يَسۡتَغِيثُواْ يُغَاثُواْ بِمَآءٖ كَٱلۡمُهۡلِ يَشۡوِي ٱلۡوُجُوهَۚ بِئۡسَ ٱلشَّرَابُ وَسَآءَتۡ مُرۡتَفَقًا

Kuma ka ce: “Gaskiya daga Ubangijinku take;” to wanda ya ga dama ya yi imani, wanda kuma ya ga dama sai ya kafirta. Lalle kam Mun tanadar wa azzalumai wata wuta wadda katangarta ta kewaye su. Idan kuma suka nemi taimako to za a taimake su ne da ruwa kamar tafasasshen mai da zai riqa toye fuskoki. Tir da wannan abin shan, makoma kuma ta munana



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 30

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ إِنَّا لَا نُضِيعُ أَجۡرَ مَنۡ أَحۡسَنَ عَمَلًا

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki nagari tabbas Mu ba ma tozarta ladan wanda ya kyautata aiki



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 31

أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ جَنَّـٰتُ عَدۡنٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهِمُ ٱلۡأَنۡهَٰرُ يُحَلَّوۡنَ فِيهَا مِنۡ أَسَاوِرَ مِن ذَهَبٖ وَيَلۡبَسُونَ ثِيَابًا خُضۡرٗا مِّن سُندُسٖ وَإِسۡتَبۡرَقٖ مُّتَّكِـِٔينَ فِيهَا عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِۚ نِعۡمَ ٱلثَّوَابُ وَحَسُنَتۡ مُرۡتَفَقٗا

Waxannan suna da gidajen Aljanna na dawwama waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, ana yi musu ado a cikinsu (watau gidajen) da awarwaro na zinare, suna kuma sanya tufafi koraye na alharini mai shara-shara da mai kauri, suna kwance a kan gadaje. Madalla (da wannan) lada, wurin hutu kuma ya kyautata



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 32

۞وَٱضۡرِبۡ لَهُم مَّثَلٗا رَّجُلَيۡنِ جَعَلۡنَا لِأَحَدِهِمَا جَنَّتَيۡنِ مِنۡ أَعۡنَٰبٖ وَحَفَفۡنَٰهُمَا بِنَخۡلٖ وَجَعَلۡنَا بَيۡنَهُمَا زَرۡعٗا

Ka kuma ba su misali da wasu mutane su biyu da Muka tanadar wa xayansu gonakai biyu na inabi, Muka kuma kewaye su da dabinai, Muka kuma sanya wasu shukoki tsakaninsu



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 33

كِلۡتَا ٱلۡجَنَّتَيۡنِ ءَاتَتۡ أُكُلَهَا وَلَمۡ تَظۡلِم مِّنۡهُ شَيۡـٔٗاۚ وَفَجَّرۡنَا خِلَٰلَهُمَا نَهَرٗا

Kowace xaya daga gonakin ta ba da ‘ya’yanta kuma ba ta rage komai daga gare su ba. Muka kuma vuvvugo da qorama ta tsakiyarsu



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 34

وَكَانَ لَهُۥ ثَمَرٞ فَقَالَ لِصَٰحِبِهِۦ وَهُوَ يُحَاوِرُهُۥٓ أَنَا۠ أَكۡثَرُ مِنكَ مَالٗا وَأَعَزُّ نَفَرٗا

Ya zamanto yana da ‘ya’yan itace, sai ya ce da abokinsa yayin da yake mahawara da shi: “Ni na fi ka yawan dukiya da qarfin jama’a.”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 35

وَدَخَلَ جَنَّتَهُۥ وَهُوَ ظَالِمٞ لِّنَفۡسِهِۦ قَالَ مَآ أَظُنُّ أَن تَبِيدَ هَٰذِهِۦٓ أَبَدٗا

Ya kuma shiga gonarsa yana kuwa mai zaluntar kansa[1], ya ce: “Ba na tsammanin cewa wannan za ta qare har abada.”


1- Yana alfahari da rashin nuna godiya ga Allah.


Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 36

وَمَآ أَظُنُّ ٱلسَّاعَةَ قَآئِمَةٗ وَلَئِن رُّدِدتُّ إِلَىٰ رَبِّي لَأَجِدَنَّ خَيۡرٗا مِّنۡهَا مُنقَلَبٗا

“Kuma ba na tsammanin alqiyama za ta tashi, kuma ko da an mayar da ni wurin Ubangijina to lalle zan sami canji fiye ma da ita.”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 37

قَالَ لَهُۥ صَاحِبُهُۥ وَهُوَ يُحَاوِرُهُۥٓ أَكَفَرۡتَ بِٱلَّذِي خَلَقَكَ مِن تُرَابٖ ثُمَّ مِن نُّطۡفَةٖ ثُمَّ سَوَّىٰكَ رَجُلٗا

Abokinsa ya ce da shi yana mai mahawara da shi: “Yanzu ka kafirce wa Wanda Ya halicce ka daga qasa, sannan (kuma) daga maniyyi, sannan Ya daidaita ka (ka zama) mutum?



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 38

لَّـٰكِنَّا۠ هُوَ ٱللَّهُ رَبِّي وَلَآ أُشۡرِكُ بِرَبِّيٓ أَحَدٗا

“Sai dai ni kam Allah Shi ne Ubangijina, ba kuwa zan haxa wani da Ubangijina ba



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 39

وَلَوۡلَآ إِذۡ دَخَلۡتَ جَنَّتَكَ قُلۡتَ مَا شَآءَ ٱللَّهُ لَا قُوَّةَ إِلَّا بِٱللَّهِۚ إِن تَرَنِ أَنَا۠ أَقَلَّ مِنكَ مَالٗا وَوَلَدٗا

“Kuma mai ya hana ka lokacin da ka shiga gonarka ka ce: ‘Abin da Allah Ya ga dama (shi zai kasance). Babu wani qarfi kuma babu dabara sai da Allah.’ Idan kana gani na na fi ka qarancin dukiya da ‘ya’ya



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 40

فَعَسَىٰ رَبِّيٓ أَن يُؤۡتِيَنِ خَيۡرٗا مِّن جَنَّتِكَ وَيُرۡسِلَ عَلَيۡهَا حُسۡبَانٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ فَتُصۡبِحَ صَعِيدٗا زَلَقًا

“To ina fatan Ubangijina Ya ba ni fiye da gonarka, Ya kuma aiko mata (gonarka) da wani bala’i daga sama, sannan ta wayi gari ta zama qeqasasshiyar qasa mai santsi



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 41

أَوۡ يُصۡبِحَ مَآؤُهَا غَوۡرٗا فَلَن تَسۡتَطِيعَ لَهُۥ طَلَبٗا

“Ko kuma ruwanta ya zama ya qafe qarqaf, ba ko za ka sami hanyar samo shi ba.”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 42

وَأُحِيطَ بِثَمَرِهِۦ فَأَصۡبَحَ يُقَلِّبُ كَفَّيۡهِ عَلَىٰ مَآ أَنفَقَ فِيهَا وَهِيَ خَاوِيَةٌ عَلَىٰ عُرُوشِهَا وَيَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي لَمۡ أُشۡرِكۡ بِرَبِّيٓ أَحَدٗا

Aka kuwa hallaka ‘ya’yan itacen nasa, sannan ya wayi gari yana tafa hannayensa kan irin abin da ya vatar a kanta, ita kuwa ga ta ta zubo a kan dirkokinta, yana kuma cewa: “Kaicona, ina ma ban haxa wani da Ubangijina ba!”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 43

وَلَمۡ تَكُن لَّهُۥ فِئَةٞ يَنصُرُونَهُۥ مِن دُونِ ٱللَّهِ وَمَا كَانَ مُنتَصِرًا

Ba shi kuwa da wata qungiya da za ta taimake shi ban da Allah, kuma bai zamo mai taimaka wa (kansa) ba



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 44

هُنَالِكَ ٱلۡوَلَٰيَةُ لِلَّهِ ٱلۡحَقِّۚ هُوَ خَيۡرٞ ثَوَابٗا وَخَيۡرٌ عُقۡبٗا

A wannan lokacin ne (ya bayyana) cewa taimako na Allah ne Tabbataccen (Sarki). Shi ne Fiyayyen Mai ba da lada kuma Fiyayyen Mai kyautata qarshe



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 45

وَٱضۡرِبۡ لَهُم مَّثَلَ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا كَمَآءٍ أَنزَلۡنَٰهُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ فَٱخۡتَلَطَ بِهِۦ نَبَاتُ ٱلۡأَرۡضِ فَأَصۡبَحَ هَشِيمٗا تَذۡرُوهُ ٱلرِّيَٰحُۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ مُّقۡتَدِرًا

Kuma ka ba su misalin rayuwar duniya (wadda take) kamar ruwa ne da Muka saukar da shi daga sama, sai tsirran qasa suka cakuxa da shi, sannan ya zama busasshe, iska tana xaixaita shi. Allah kuwa Ya kasance Mai iko ne a kan komai



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 46

ٱلۡمَالُ وَٱلۡبَنُونَ زِينَةُ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۖ وَٱلۡبَٰقِيَٰتُ ٱلصَّـٰلِحَٰتُ خَيۡرٌ عِندَ رَبِّكَ ثَوَابٗا وَخَيۡرٌ أَمَلٗا

Dukiya da ‘ya’ya adon rayuwar duniya ne; wanzazzun ayyuka nagari kuwa su suka fi lada a wurin Ubangijinka kuma su ne buri mafi alheri



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 47

وَيَوۡمَ نُسَيِّرُ ٱلۡجِبَالَ وَتَرَى ٱلۡأَرۡضَ بَارِزَةٗ وَحَشَرۡنَٰهُمۡ فَلَمۡ نُغَادِرۡ مِنۡهُمۡ أَحَدٗا

Kuma ka tuna ranar da za Mu tafiyar da duwatsu kuma ka ga qasa a baje (ba tudu ba rafi), Mu kuma tattara su (gaba xaya), ba Mu bar xaya daga cikinsu ba