Surah: Suratus Shams

Ayah : 1

وَٱلشَّمۡسِ وَضُحَىٰهَا

Na rantse da rana da walaharta



Surah: Suratus Shams

Ayah : 2

وَٱلۡقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا

Da kuma wata idan ya bi ta (wato ranar)[1]


1- Watau ya biyo bayan faxuwar rana.


Surah: Suratus Shams

Ayah : 3

وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا

Da kuma wuni idan ya bayyana ta



Surah: Suratus Shams

Ayah : 4

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰهَا

Da kuma dare idan ya lulluve ta



Surah: Suratus Shams

Ayah : 5

وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا

Da kuma sama da gininta



Surah: Suratus Shams

Ayah : 6

وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا طَحَىٰهَا

Da kuma qasa da shimfixarta



Surah: Suratus Shams

Ayah : 7

وَنَفۡسٖ وَمَا سَوَّىٰهَا

Da kuma rai da daidaitarsa



Surah: Suratus Shams

Ayah : 8

فَأَلۡهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقۡوَىٰهَا

Sai Ya kimsa masa (gane) lalacewarsa da taqawarsa



Surah: Suratus Shams

Ayah : 9

قَدۡ أَفۡلَحَ مَن زَكَّىٰهَا

Haqiqa wanda ya tsarkake shi (ran) ya rabauta



Surah: Suratus Shams

Ayah : 10

وَقَدۡ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا

Haqiqa kuma wanda ya binne shi da savo ya tave



Surah: Suratus Shams

Ayah : 11

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِطَغۡوَىٰهَآ

Samudawa sun qaryata saboda xagawarsu



Surah: Suratus Shams

Ayah : 12

إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشۡقَىٰهَا

Yayin da mafi tsagerancinsu ya zabura



Surah: Suratus Shams

Ayah : 13

فَقَالَ لَهُمۡ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقۡيَٰهَا

Sai Manzon Allah[1] ya ce da su: “Ku bar taguwar Allah da (ranar) shanta.”


1- Watau Annabi Salihu ().


Surah: Suratus Shams

Ayah : 14

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمۡدَمَ عَلَيۡهِمۡ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمۡ فَسَوَّىٰهَا

Sai suka qaryata shi sannan suka soke ta, sai Ubangijinsu Ya kama su da azaba saboda zunubinsu, sai Ya daidaita ta (watau qabilar wajen azaba)



Surah: Suratus Shams

Ayah : 15

وَلَا يَخَافُ عُقۡبَٰهَا

Kuma ba Ya tsoron abin da zai biyo bayanta[1]


1- Watau ba ya jin tsoron wani abu da hallaka su za ta haifar nan gaba.