Surah: Suratul Buruj

Ayah : 1

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡبُرُوجِ

Na rantse da sama ma’abociyar manziloli[1]


1- Watau manziloli na rana da wata da taurari.


Surah: Suratul Buruj

Ayah : 2

وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡمَوۡعُودِ

Da ranar da aka yi alqawarin zuwanta[1]


1- Watau ranar alqiyama.


Surah: Suratul Buruj

Ayah : 3

وَشَاهِدٖ وَمَشۡهُودٖ

Da mai shaida[1] da kuma abin yi wa shaida


1- Watau kamar Annabi da zai ba da shaida game da al’ummarsa.


Surah: Suratul Buruj

Ayah : 4

قُتِلَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡأُخۡدُودِ

An la’anci ma’abota rami (na azabtar da muminai)[1]


1- Wani azzalumin sarki ne da aka yi a Najrana ta qasar Yaman kafin aiko Annabi () wanda aka haqa masa rami aka hura wuta, ya riqa jefa muminai a cikinsa yana qona su da ransu.


Surah: Suratul Buruj

Ayah : 5

ٱلنَّارِ ذَاتِ ٱلۡوَقُودِ

Na wuta mai ruruwa



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 6

إِذۡ هُمۡ عَلَيۡهَا قُعُودٞ

Yayin da suke zaune a gefenta



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 7

وَهُمۡ عَلَىٰ مَا يَفۡعَلُونَ بِٱلۡمُؤۡمِنِينَ شُهُودٞ

Alhali su suna kallon abin da suke aikata wa muminai



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 8

وَمَا نَقَمُواْ مِنۡهُمۡ إِلَّآ أَن يُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

Babu kuwa abin da suke tuhumar su da shi sai don kawai sun yi imani da Allah Mabuwayi, Sha-yabo



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 9

ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

Wanda Yake da mulkin sammai da qasa. Allah kuma Mai ganin komai ne



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُواْ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ ثُمَّ لَمۡ يَتُوبُواْ فَلَهُمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمۡ عَذَابُ ٱلۡحَرِيقِ

Lalle waxanda suka azabtar da muminai maza da muminai mata sannan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, suna kuma da azabar quna



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 11

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡكَبِيرُ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. Wannan kuwa shi ne babban rabo



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 12

إِنَّ بَطۡشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ

Lalle damqar Ubangijinka tabbas mai tsanani ce



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 13

إِنَّهُۥ هُوَ يُبۡدِئُ وَيُعِيدُ

Lalle Shi ne Yake farar (da komai) Yake kuma dawo (da shi)



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 14

وَهُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلۡوَدُودُ

Shi ne kuma Mai gafara, Mai qaunar (bayinsa na qwarai)



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 15

ذُو ٱلۡعَرۡشِ ٱلۡمَجِيدُ

Ma’abocin Al’arshi Mai girma



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 16

فَعَّالٞ لِّمَا يُرِيدُ

Mai aikata abin da Yake nufi



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 17

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلۡجُنُودِ

Shin labarin rundunoni ya zo maka?



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 18

فِرۡعَوۡنَ وَثَمُودَ

(Su ne) Fir’auna da Samudawa



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 19

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي تَكۡذِيبٖ

A’a, su dai waxanda suka kafirta suna cikin qaryatawa ne



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 20

وَٱللَّهُ مِن وَرَآئِهِم مُّحِيطُۢ

Allah kuwa Yana kewaye da su (da iliminsa)



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 21

بَلۡ هُوَ قُرۡءَانٞ مَّجِيدٞ

A’a, shi dai Alqur’ani ne mai girma



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 22

فِي لَوۡحٖ مَّحۡفُوظِۭ

A cikin Lauhul-Mahafuzu