Surah: Suratul Infixar

Ayah : 1

إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنفَطَرَتۡ

Idan sama ta tsattsage



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 2

وَإِذَا ٱلۡكَوَاكِبُ ٱنتَثَرَتۡ

Idan kuma taurari suka farfaxo suka tarwatse



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 3

وَإِذَا ٱلۡبِحَارُ فُجِّرَتۡ

Idan kuma koguna aka harhaxe su



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 4

وَإِذَا ٱلۡقُبُورُ بُعۡثِرَتۡ

Idan kuma qaburbura aka fito da matattun da ke cikinsu



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 5

عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّا قَدَّمَتۡ وَأَخَّرَتۡ

Kowane rai ya san abin da ya gabatar da wanda ya jirkintar



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 6

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡإِنسَٰنُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ ٱلۡكَرِيمِ

Ya kai mutum, me ya ruxe ka ne game da Ubangijinka Mai karamci?



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 7

ٱلَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ

Wanda Ya halicce ka Ya kuma daidaita ka Ya miqar da kai[1]?


1- Watau ya lura da girman ni’imar da ya yi masa yayin da bai yi masa irin halittar jaki ba ko ta biri ko ta kare.


Surah: Suratul Infixar

Ayah : 8

فِيٓ أَيِّ صُورَةٖ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ

Ya harhaxa ka cikin irin surar da Ya ga dama?



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 9

كَلَّا بَلۡ تُكَذِّبُونَ بِٱلدِّينِ

A’a dai, kawai dai kuna qaryata ranar sakamako ne



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 10

وَإِنَّ عَلَيۡكُمۡ لَحَٰفِظِينَ

Kuma lalle akwai masu kula da ku[1]


1- Watau mala’iku.


Surah: Suratul Infixar

Ayah : 11

كِرَامٗا كَٰتِبِينَ

Masu daraja marubuta



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 12

يَعۡلَمُونَ مَا تَفۡعَلُونَ

Suna sane da abin da kuke aikatawa



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 13

إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٖ

Lalle mutanen kirki tabbas suna cikin ni’ima



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 14

وَإِنَّ ٱلۡفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٖ

Lalle kuma fajirai tabbas suna cikin (wutar) Jahima



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 15

يَصۡلَوۡنَهَا يَوۡمَ ٱلدِّينِ

Za su qonu da ita ranar sakamako



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 16

وَمَا هُمۡ عَنۡهَا بِغَآئِبِينَ

Kuma su ba masu rabuwa ne da ita ba



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 17

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Kuma kai me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 18

ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Sannan me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 19

يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ

(Ita ce) ranar da wani rai ba ya mallakar wani amfani ga wani rai; al’amari kuwa (gaba xayansa) a wannan ranar yana ga Allah