Surah: Suratul Jinn

Ayah : 1

قُلۡ أُوحِيَ إِلَيَّ أَنَّهُ ٱسۡتَمَعَ نَفَرٞ مِّنَ ٱلۡجِنِّ فَقَالُوٓاْ إِنَّا سَمِعۡنَا قُرۡءَانًا عَجَبٗا

Ka ce: “An yiwo min wahayi na cewa, wata jama’a ta aljannu[1] sun saurari (karatun Alqur’ani), sai suka ce: “Lalle mu mun ji Alqur’ani mai ban mamaki


1- Su ne wasu aljannu da suka saurari karatun Annabi () a wani wuri da ake kira Baxnu Nakhla, lokacin da yake yi wa sahabbansa sallar asuba.


Surah: Suratul Jinn

Ayah : 2

يَهۡدِيٓ إِلَى ٱلرُّشۡدِ فَـَٔامَنَّا بِهِۦۖ وَلَن نُّشۡرِكَ بِرَبِّنَآ أَحَدٗا

“Yana shiryarwa zuwa ga daidai, saboda haka muka yi imani da shi; ba kuwa za mu haxa wani da Ubangijinmu ba har abada



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 3

وَأَنَّهُۥ تَعَٰلَىٰ جَدُّ رَبِّنَا مَا ٱتَّخَذَ صَٰحِبَةٗ وَلَا وَلَدٗا

“Kuma lalle yadda lamarin yake, girman Ubangijinmu ya xaukaka, bai riqi wata mata ko wani xa ba



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 4

وَأَنَّهُۥ كَانَ يَقُولُ سَفِيهُنَا عَلَى ٱللَّهِ شَطَطٗا

“Kuma lalle yadda lamarin yake, wani wawa daga cikinmu ya kasance yana faxar mummunar qarya game da Allah



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 5

وَأَنَّا ظَنَنَّآ أَن لَّن تَقُولَ ٱلۡإِنسُ وَٱلۡجِنُّ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبٗا

“Lalle kuma mun yi tsammanin mutum da aljan ba za su tava faxar qarya game da Allah ba



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 6

وَأَنَّهُۥ كَانَ رِجَالٞ مِّنَ ٱلۡإِنسِ يَعُوذُونَ بِرِجَالٖ مِّنَ ٱلۡجِنِّ فَزَادُوهُمۡ رَهَقٗا

“Kuma lalle yadda lamarin yake, wasu mazaje daga mutane sun kasance suna neman tsari daga wasu mazaje na aljannu, saboda haka suka qara musu girman kai



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 7

وَأَنَّهُمۡ ظَنُّواْ كَمَا ظَنَنتُمۡ أَن لَّن يَبۡعَثَ ٱللَّهُ أَحَدٗا

“Kuma lalle su sun yi tsammanin-kamar yadda kuka yi tsammani-cewar Allah ba zai tashi kowa ba har abada



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 8

وَأَنَّا لَمَسۡنَا ٱلسَّمَآءَ فَوَجَدۡنَٰهَا مُلِئَتۡ حَرَسٗا شَدِيدٗا وَشُهُبٗا

“Kuma lalle mu mun nemi hawa sama, sai muka same ta an cika ta da matsanancin tsaro da taurari (masu jifa da garwashi)



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 9

وَأَنَّا كُنَّا نَقۡعُدُ مِنۡهَا مَقَٰعِدَ لِلسَّمۡعِۖ فَمَن يَسۡتَمِعِ ٱلۡأٓنَ يَجِدۡ لَهُۥ شِهَابٗا رَّصَدٗا

“Lalle kuma mun zamanto a da muna hawa wasu wurare nata don yin sauraro[1]; to duk wanda ya nemi yin sauraro a yanzu zai sama wa kansa wani tauraro wanda aka tanada (don jifan sa)


1- Watau a da can lokacin jahiliyya aljannu sun saba hawa sama domin sato bayanan sirri daga tattaunawar mala’iku, suna isar da su ga bokaye a qasa.


Surah: Suratul Jinn

Ayah : 10

وَأَنَّا لَا نَدۡرِيٓ أَشَرٌّ أُرِيدَ بِمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ أَمۡ أَرَادَ بِهِمۡ رَبُّهُمۡ رَشَدٗا

“Kuma lalle mu ba mu sani ba, shin wani sharri ake nufi da waxanda ke qasa, ko kuwa Ubangijinsu Yana nufin su da shiriya ne?



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 11

وَأَنَّا مِنَّا ٱلصَّـٰلِحُونَ وَمِنَّا دُونَ ذَٰلِكَۖ كُنَّا طَرَآئِقَ قِدَدٗا

“Lalle daga cikinmu akwai salihai, daga cikinmu kuma akwai waxanda ba haka suke ba; mun zamanto hanyoyi daban-daban



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 12

وَأَنَّا ظَنَنَّآ أَن لَّن نُّعۡجِزَ ٱللَّهَ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَن نُّعۡجِزَهُۥ هَرَبٗا

“Kuma lalle mu mun tabbatar cewa ba za mu gagari Allah ba a bayan qasa, ba kuma za mu gagare Shi ba a guje



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 13

وَأَنَّا لَمَّا سَمِعۡنَا ٱلۡهُدَىٰٓ ءَامَنَّا بِهِۦۖ فَمَن يُؤۡمِنۢ بِرَبِّهِۦ فَلَا يَخَافُ بَخۡسٗا وَلَا رَهَقٗا

“Lalle kuma mu lokacin da muka ji Alqur’ani, sai muka yi imani da shi, to duk wanda zai yi imani da Ubangijinsa, to ba zai ji tsoron qwara ko zalunci ba[1]


1- Watau ba za a tauye masa ladansa ba, kuma ba za a qara masa wani laifin da bai aikata ba.


Surah: Suratul Jinn

Ayah : 14

وَأَنَّا مِنَّا ٱلۡمُسۡلِمُونَ وَمِنَّا ٱلۡقَٰسِطُونَۖ فَمَنۡ أَسۡلَمَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ تَحَرَّوۡاْ رَشَدٗا

“Kuma lalle mu a cikinmu akwai Musulmi, a cikinmu kuma akwai karkatattu; saboda haka duk wanda ya musulunta, to waxannan sun nufi hanyar shiriya



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 15

وَأَمَّا ٱلۡقَٰسِطُونَ فَكَانُواْ لِجَهَنَّمَ حَطَبٗا

“Amma kuma karkatattu, to sun kasance makamashi ne ga (wutar) Jahannama.”



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 16

وَأَلَّوِ ٱسۡتَقَٰمُواْ عَلَى ٱلطَّرِيقَةِ لَأَسۡقَيۡنَٰهُم مَّآءً غَدَقٗا

Da kuwa (mutan Makka) sun daidaita a kan (Musulunci), to lalle da Mun shayar da su ruwa mai yawa



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 17

لِّنَفۡتِنَهُمۡ فِيهِۚ وَمَن يُعۡرِضۡ عَن ذِكۡرِ رَبِّهِۦ يَسۡلُكۡهُ عَذَابٗا صَعَدٗا

Don Mu jarrabe su game da shi. Duk kuwa wanda ya kau da kai daga ambaton Ubangijinsa[1] to zai saka shi cikin azaba mai wahala


1- Watau ya bijire wa Alqur’ani da wa’azuzzukan da ke cikinsa.


Surah: Suratul Jinn

Ayah : 18

وَأَنَّ ٱلۡمَسَٰجِدَ لِلَّهِ فَلَا تَدۡعُواْ مَعَ ٱللَّهِ أَحَدٗا

Kuma lalle masallatai na Allah ne, saboda haka kada ku bauta wa wani tare da Allah



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 19

وَأَنَّهُۥ لَمَّا قَامَ عَبۡدُ ٱللَّهِ يَدۡعُوهُ كَادُواْ يَكُونُونَ عَلَيۡهِ لِبَدٗا

Kuma lalle yadda lamarin yake, yayin da Bawan Allah (Annabi Muhammadu) ya tashi yana bauta masa, sai (aljannu) suka kusa su zamo wasu kan wasu don cincirindo a kansa[1]


1- Watau a Baxnu Nakhla lokacin da yake tsaye yana karatun Alqur’ani.


Surah: Suratul Jinn

Ayah : 20

قُلۡ إِنَّمَآ أَدۡعُواْ رَبِّي وَلَآ أُشۡرِكُ بِهِۦٓ أَحَدٗا

Ka ce: “Lalle ina bauta wa Ubangijina ne kawai, ba kuwa na tara wani da Shi.”



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 21

قُلۡ إِنِّي لَآ أَمۡلِكُ لَكُمۡ ضَرّٗا وَلَا رَشَدٗا

Kuma ka ce: “Lalle ni ban mallaki kare muku wata cuta ko janyo muku wani alhairi ba.”



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 22

قُلۡ إِنِّي لَن يُجِيرَنِي مِنَ ٱللَّهِ أَحَدٞ وَلَنۡ أَجِدَ مِن دُونِهِۦ مُلۡتَحَدًا

Ka ce: “Lalle ni ba wani mai kare ni daga (azabar) Allah, kuma ba zan tava samun wata mafaka in ba tasa ba



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 23

إِلَّا بَلَٰغٗا مِّنَ ٱللَّهِ وَرِسَٰلَٰتِهِۦۚ وَمَن يَعۡصِ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ فَإِنَّ لَهُۥ نَارَ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدًا

“Sai dai isar da aike daga Allah da kuma saqwanninsa. Duk kuwa waxanda suka sava wa Allah da Manzonsa, to lalle suna da wutar Jahannama, suna madawwama a cikinta har abada.”



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 24

حَتَّىٰٓ إِذَا رَأَوۡاْ مَا يُوعَدُونَ فَسَيَعۡلَمُونَ مَنۡ أَضۡعَفُ نَاصِرٗا وَأَقَلُّ عَدَدٗا

Har yayin da (kafirai) suka ga abin da ake yi musu alqawari da shi, to ba da daxewa ba za su san wa ya fi raunanan mataimaka da kuma qanqantar jama’a



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 25

قُلۡ إِنۡ أَدۡرِيٓ أَقَرِيبٞ مَّا تُوعَدُونَ أَمۡ يَجۡعَلُ لَهُۥ رَبِّيٓ أَمَدًا

Ka ce: “Ni ban sani ba, shin kusa yake abin da ake yi muku alqawarinsa ko kuwa Ubangijina zai sanya masa zamani mai tsawo?”



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 26

عَٰلِمُ ٱلۡغَيۡبِ فَلَا يُظۡهِرُ عَلَىٰ غَيۡبِهِۦٓ أَحَدًا

“(Shi ne) Masanin gaibu, sannan ba Ya bayyana gaibunsa ga wani



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 27

إِلَّا مَنِ ٱرۡتَضَىٰ مِن رَّسُولٖ فَإِنَّهُۥ يَسۡلُكُ مِنۢ بَيۡنِ يَدَيۡهِ وَمِنۡ خَلۡفِهِۦ رَصَدٗا

“Sai manzo da ya yarda da shi, shi kuma lalle Yakan sanya masa tsaro ta gabansa da ta bayansa[1]


1- Watau ta hanyar sa masa mala’iku masu tsaron sa domin kada shaixanu su samu kusantar sa.


Surah: Suratul Jinn

Ayah : 28

لِّيَعۡلَمَ أَن قَدۡ أَبۡلَغُواْ رِسَٰلَٰتِ رَبِّهِمۡ وَأَحَاطَ بِمَا لَدَيۡهِمۡ وَأَحۡصَىٰ كُلَّ شَيۡءٍ عَدَدَۢا

“Don Ya bayyanar da cewa, haqiqa sun isar da saqwannin Ubangijinsu, Ya kuma kewaye da (sanin) abin da yake tare da su, Ya kuma qididdige adadin kowane abu.”