Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 1

سَأَلَ سَآئِلُۢ بِعَذَابٖ وَاقِعٖ

Mai tambaya ya yi tambaya game da wata azaba mai aukuwa[1]


1- Watau wadda Annabi () yake musu kashedi da ita idan sun qi imani. Duba Suratul Anfal, aya ta 32. Mai tambayar kuwa shi ne Nadhru xan Haris.


Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 2

لِّلۡكَٰفِرِينَ لَيۡسَ لَهُۥ دَافِعٞ

Ga kafirai (wadda) ba ta da wani mai kaxe ta



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 3

مِّنَ ٱللَّهِ ذِي ٱلۡمَعَارِجِ

Daga Allah Mai matattakalai



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 4

تَعۡرُجُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيۡهِ فِي يَوۡمٖ كَانَ مِقۡدَارُهُۥ خَمۡسِينَ أَلۡفَ سَنَةٖ

Mala’iku tare da Jibrilu suna hawa zuwa gare Shi a cikin wata rana (wadda) gwargwadonta yake daidai da shekara dubu hamsin



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 5

فَٱصۡبِرۡ صَبۡرٗا جَمِيلًا

Sai ka yi haquri kyakkyawan haquri



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 6

إِنَّهُمۡ يَرَوۡنَهُۥ بَعِيدٗا

Lalle su suna ganin ta mai nisa ce



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 7

وَنَرَىٰهُ قَرِيبٗا

Mu kuma Muna ganin ta kusa-kusa



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 8

يَوۡمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلۡمُهۡلِ

A ranar da sama za ta kasance kamar narkakkiyar dalma



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 9

وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ

Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga (ta gashin tumaki)



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 10

وَلَا يَسۡـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمٗا

Kuma aboki ba ya tambayar aboki



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 11

يُبَصَّرُونَهُمۡۚ يَوَدُّ ٱلۡمُجۡرِمُ لَوۡ يَفۡتَدِي مِنۡ عَذَابِ يَوۡمِئِذِۭ بِبَنِيهِ

(Alhali kuma) ana nuna musu junansu. Mai laifi ya riqa burin ina ma zai fanshi kansa daga azabar wannan rana da ‘ya’yansa



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 12

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ

Da matarsa da xan’uwansa



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 13

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِي تُـٔۡوِيهِ

Da danginsa waxanda suke kare shi



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 14

وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ يُنجِيهِ

Da ma duk wanda yake a bayan qasa baki xaya, sannan (fansar) ta tserar da shi



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 15

كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Faufau! Lalle ita (wutar) Laza ce



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 16

نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ

Mai xaxxaye fatar kai



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 17

تَدۡعُواْ مَنۡ أَدۡبَرَ وَتَوَلَّىٰ

Tana kiran wanda ya juya ya ba da baya



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 18

وَجَمَعَ فَأَوۡعَىٰٓ

Ya kuma tara (dukiya) sai ya voye (ta)



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 19

۞إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا

Lalle mutum an halicce shi mai rashin nutsuwa ne



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 20

إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعٗا

(Watau) idan sharri ya same shi ya zama mai raki



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 21

وَإِذَا مَسَّهُ ٱلۡخَيۡرُ مَنُوعًا

Idan kuma alheri ya same shi ya zama mai maqo



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 22

إِلَّا ٱلۡمُصَلِّينَ

Sai dai masallata



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 23

ٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ دَآئِمُونَ

Waxanda suke masu dawwama a kan sallarsu



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 24

وَٱلَّذِينَ فِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ مَّعۡلُومٞ

Waxanda kuma suke akwai haqqi sananne a cikin dukiyoyinsu



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 25

لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ

Ga mai roqo da wanda ake hana wa (saboda ba ya roqo)



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 26

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

Waxanda kuma suke gaskata ranar sakamako



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 27

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنۡ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشۡفِقُونَ

Waxanda kuma suke tsoron azabar Ubangijinsu



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 28

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمۡ غَيۡرُ مَأۡمُونٖ

Lalle azabar Ubangijinsu ba abar amincewa ba ce



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 29

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِفُرُوجِهِمۡ حَٰفِظُونَ

Waxanda kuma suke kiyaye al’aurarsu (daga yin zina)



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 30

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ

Sai a wajan matayensu ko kuma qwarqarorinsu; to su a nan ba ababen zargi ba ne