ٱلۡحَآقَّةُ
Mai tabbata (watau alqiyama)
مَا ٱلۡحَآقَّةُ
Mece ce mai tabbata?
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡحَآقَّةُ
Me ya sanar da kai abin da ake kira mai tabbata?
كَذَّبَتۡ ثَمُودُ وَعَادُۢ بِٱلۡقَارِعَةِ
Samudawa da Adawa sun qaryata mai qwanqwasa (zukata da tsoro)
فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهۡلِكُواْ بِٱلطَّاغِيَةِ
To amma Samudawa sai aka halaka su da tsawa mai tsanani
وَأَمَّا عَادٞ فَأُهۡلِكُواْ بِرِيحٖ صَرۡصَرٍ عَاتِيَةٖ
Adawa kuma sai aka hallaka su da iska mai tsananin sanyi mai qarfi
سَخَّرَهَا عَلَيۡهِمۡ سَبۡعَ لَيَالٖ وَثَمَٰنِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومٗاۖ فَتَرَى ٱلۡقَوۡمَ فِيهَا صَرۡعَىٰ كَأَنَّهُمۡ أَعۡجَازُ نَخۡلٍ خَاوِيَةٖ
Ya aiko musu da ita dare bakwai da wuni takwas a jere, sai ka riqa ganin mutane a cikinta matattu a yashe, kai ka ce rarakakkun kututturan dabinai ne (a zube)
فَهَلۡ تَرَىٰ لَهُم مِّنۢ بَاقِيَةٖ
To shin za ka iya ganin sauran vurvushinsu?
وَجَآءَ فِرۡعَوۡنُ وَمَن قَبۡلَهُۥ وَٱلۡمُؤۡتَفِكَٰتُ بِٱلۡخَاطِئَةِ
Fir’auna kuma da waxanda suke gabaninsa da (alqaryar) da aka kifar[1], sun zo da manyan laifuka
1- Watau alqaryun Annabi Lux () waxanda Allah () ya kifar da su saboda miyagun laifuffukansu.
فَعَصَوۡاْ رَسُولَ رَبِّهِمۡ فَأَخَذَهُمۡ أَخۡذَةٗ رَّابِيَةً
Sai suka sava wa Manzon Ubangijinsu, sai Muka kama su kamawa mai qaruwa
إِنَّا لَمَّا طَغَا ٱلۡمَآءُ حَمَلۡنَٰكُمۡ فِي ٱلۡجَارِيَةِ
Mu lalle yayin da ruwa ya mamaye komai Mun xauke ku a cikin jirgin ruwa[1]
1- Watau ya xauki iyayensu waxanda suke cikin tsatsonsu a cikin jirgin ruwan Annabi Nuhu ().
لِنَجۡعَلَهَا لَكُمۡ تَذۡكِرَةٗ وَتَعِيَهَآ أُذُنٞ وَٰعِيَةٞ
Don Mu sanya shi wa’azi a gare ku, kuma kunne mai kiyayewa ya kiyaye shi
فَإِذَا نُفِخَ فِي ٱلصُّورِ نَفۡخَةٞ وَٰحِدَةٞ
To idan aka busa qaho busa xaya
وَحُمِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ وَٱلۡجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةٗ وَٰحِدَةٗ
Aka kuma xaga qasa da duwatsu sai aka dandaqe su dandaqewa baki xaya
فَيَوۡمَئِذٖ وَقَعَتِ ٱلۡوَاقِعَةُ
To a wannan rana ce mai afkuwa ta afku (watau alqiyama)
وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِيَ يَوۡمَئِذٖ وَاهِيَةٞ
Sama kuma ta kekkece, don kuwa a wannan ranar ita mai rauni ce
وَٱلۡمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرۡجَآئِهَاۚ وَيَحۡمِلُ عَرۡشَ رَبِّكَ فَوۡقَهُمۡ يَوۡمَئِذٖ ثَمَٰنِيَةٞ
Mala’iku kuma suna a sasanninta. A wannan ranar kuma (mala’iku) takwas za su xauki Al’arshin Ubangijinka a samansu
يَوۡمَئِذٖ تُعۡرَضُونَ لَا تَخۡفَىٰ مِنكُمۡ خَافِيَةٞ
A wannan ranar ne kuma za a bujuro da ku, ba wani abu naku mai vuya
فَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقۡرَءُواْ كِتَٰبِيَهۡ
To duk wanda aka bai wa littafinsa a hannunsa na dama zai ce: “Ku karvi littafina ku karanta
إِنِّي ظَنَنتُ أَنِّي مُلَٰقٍ حِسَابِيَهۡ
“Lalle ni na tabbata haka zan haxu da sakamakona.”
فَهُوَ فِي عِيشَةٖ رَّاضِيَةٖ
To shi zai zama cikin rayuwa abar yarda
فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٖ
Cikin Aljanna maxaukakiya
قُطُوفُهَا دَانِيَةٞ
‘Ya’yan itatuwanta dab da dab suke
كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ هَنِيٓـَٔۢا بِمَآ أَسۡلَفۡتُمۡ فِي ٱلۡأَيَّامِ ٱلۡخَالِيَةِ
(A ce da su): “Ku ci ku sha kuna masu farin ciki saboda abin da kuka gabatar a kwanakinku da suka shuxe (na duniya).”
وَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي لَمۡ أُوتَ كِتَٰبِيَهۡ
Amma kuma wanda aka bai wa littafinsa a hannunsa na hagun sai ya ce: “Kaicona, ina ma da ba a ba ni littafina ba!
وَلَمۡ أَدۡرِ مَا حِسَابِيَهۡ
“Kuma ban san mene ne sakamakona ba
يَٰلَيۡتَهَا كَانَتِ ٱلۡقَاضِيَةَ
“Kaiconta (watau mutuwa), ina ma da ta zama ita ce qarshe!
مَآ أَغۡنَىٰ عَنِّي مَالِيَهۡۜ
“Dukiyata ba ta wadata min komai ba
هَلَكَ عَنِّي سُلۡطَٰنِيَهۡ
“Mulkina ya vace min da gani.”
خُذُوهُ فَغُلُّوهُ
(Sai a ce da mala’iku): Ku kama shi ku ququnce shi!