Surah: Suratul Baqara

Ayah : 1

الٓمٓ

ALIF LAM MIM[1]


1- Allah () ya buxe wannan Sura da harufan Alif da Lam da Mim. Hakanan akwai surorin da dama da Allah ya buxe su da irin waxannan datsattsun haruffa. Allah ne kaxai ya san haqiqanin abin da yake nufi da su. Wasu malamai na cewa, Allah yana nuna mu’ujizar Alqurani ne da irin waxannan haruffa.


Surah: Suratul Baqara

Ayah : 2

ذَٰلِكَ ٱلۡكِتَٰبُ لَا رَيۡبَۛ فِيهِۛ هُدٗى لِّلۡمُتَّقِينَ

Wannan littafin babu wani kokwanto a cikinsa; shiriya ne ga masu taqawa[1]


1- Taqawa tana nufin aikata abin Allah ya wajabta da nisantar abin da ya haramta.


Surah: Suratul Baqara

Ayah : 3

ٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡغَيۡبِ وَيُقِيمُونَ ٱلصَّلَوٰةَ وَمِمَّا رَزَقۡنَٰهُمۡ يُنفِقُونَ

Waxanda suke yin imani da gaibi kuma suke tsayar da salla kuma suke ciyarwa daga abin da Muka arzuta su da shi



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 4

وَٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِمَآ أُنزِلَ إِلَيۡكَ وَمَآ أُنزِلَ مِن قَبۡلِكَ وَبِٱلۡأٓخِرَةِ هُمۡ يُوقِنُونَ

Waxanda suke yin imani da abin da aka saukar maka da abin da aka saukar a gabaninka, kuma suke sakankancewa da ranar lahira



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 5

أُوْلَـٰٓئِكَ عَلَىٰ هُدٗى مِّن رَّبِّهِمۡۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

Waxannan suna kan (babbar) shiriya daga Ubangijinsu, kuma waxannan su ne masu samun babban rabo



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 6

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ سَوَآءٌ عَلَيۡهِمۡ ءَأَنذَرۡتَهُمۡ أَمۡ لَمۡ تُنذِرۡهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Lalle waxanda suka kafirta, duk xaya ne a gare su, ka yi musu gargaxi ko ba ka yi musu ba, ba za su yi imani ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 7

خَتَمَ ٱللَّهُ عَلَىٰ قُلُوبِهِمۡ وَعَلَىٰ سَمۡعِهِمۡۖ وَعَلَىٰٓ أَبۡصَٰرِهِمۡ غِشَٰوَةٞۖ وَلَهُمۡ عَذَابٌ عَظِيمٞ

Allah Ya toshe zukatansu da jinsu, kuma akwai wani lulluvi a kan idanunsu, kuma suna da azaba mai girma



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 8

وَمِنَ ٱلنَّاسِ مَن يَقُولُ ءَامَنَّا بِٱللَّهِ وَبِٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَمَا هُم بِمُؤۡمِنِينَ

A cikin mutane kuma akwai waxanda suke cewa: “Mun yi imani da Allah kuma mun yi imani da ranar lahira,” alhalin su ba muminai ne ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 9

يُخَٰدِعُونَ ٱللَّهَ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَمَا يَخۡدَعُونَ إِلَّآ أَنفُسَهُمۡ وَمَا يَشۡعُرُونَ

Suna ganin suna yaudarar Allah ne da waxanda suka yi imani, amma kuwa ba kowa suke yaudara ba sai kawunansu, kuma su ba sa jin hakan



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 10

فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ فَزَادَهُمُ ٱللَّهُ مَرَضٗاۖ وَلَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمُۢ بِمَا كَانُواْ يَكۡذِبُونَ

Akwai wata cuta (ta munafunci) a cikin zukatansu, sai Allah Ya qara musu wata cutar, kuma suna da wata azaba mai raxaxi saboda qaryar da suke yi



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 11

وَإِذَا قِيلَ لَهُمۡ لَا تُفۡسِدُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ قَالُوٓاْ إِنَّمَا نَحۡنُ مُصۡلِحُونَ

Idan kuma aka ce musu: “Kada ku yi varna a bayan qasa”, sai su ce: “Mu fa masu gyara ne kawai.”



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 12

أَلَآ إِنَّهُمۡ هُمُ ٱلۡمُفۡسِدُونَ وَلَٰكِن لَّا يَشۡعُرُونَ

Saurara, lalle su su ne mavarnata, amma ba sa jin hakan



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 13

وَإِذَا قِيلَ لَهُمۡ ءَامِنُواْ كَمَآ ءَامَنَ ٱلنَّاسُ قَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ كَمَآ ءَامَنَ ٱلسُّفَهَآءُۗ أَلَآ إِنَّهُمۡ هُمُ ٱلسُّفَهَآءُ وَلَٰكِن لَّا يَعۡلَمُونَ

Idan kuma aka ce da su: “Ku yi imani kamar yadda mutane suka yi imani”, sai su ce: “Shin za mu yi imani ne kamar yadda wawaye suka yi imani?” Saurara, lalle su ne wawayen, sai dai ba sa sanin (hakan)



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 14

وَإِذَا لَقُواْ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ قَالُوٓاْ ءَامَنَّا وَإِذَا خَلَوۡاْ إِلَىٰ شَيَٰطِينِهِمۡ قَالُوٓاْ إِنَّا مَعَكُمۡ إِنَّمَا نَحۡنُ مُسۡتَهۡزِءُونَ

Idan kuma suka haxu da waxanda suka yi imani sai su ce: “Mun yi imani.” To amma idan suka kevanta da shaixanunsu (iyayen gidansu)[1] sai su ce: “Mu fa lalle muna nan tare da ku, mu kawai izgili ne muke yi.”


1- Shexanunsu, su ne manyan kafirai da Yahudawa.


Surah: Suratul Baqara

Ayah : 15

ٱللَّهُ يَسۡتَهۡزِئُ بِهِمۡ وَيَمُدُّهُمۡ فِي طُغۡيَٰنِهِمۡ يَعۡمَهُونَ

Allah Yana yi musu izgili, kuma Yana yi musu talala cikin shisshiginsu suna masu ximuwa



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 16

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ ٱشۡتَرَوُاْ ٱلضَّلَٰلَةَ بِٱلۡهُدَىٰ فَمَا رَبِحَت تِّجَٰرَتُهُمۡ وَمَا كَانُواْ مُهۡتَدِينَ

Waxannan su ne suka musanya shiriya da vata, don haka kasuwancinsu bai yi riba ba, kuma ba su zamo shiryayyu ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 17

مَثَلُهُمۡ كَمَثَلِ ٱلَّذِي ٱسۡتَوۡقَدَ نَارٗا فَلَمَّآ أَضَآءَتۡ مَا حَوۡلَهُۥ ذَهَبَ ٱللَّهُ بِنُورِهِمۡ وَتَرَكَهُمۡ فِي ظُلُمَٰتٖ لَّا يُبۡصِرُونَ

Misalinsu kamar misalin wanda ya wahala har ya kunna wuta ne, yayin da ta haskaka abin da yake daura da shi, sai Allah Ya tafiyar da haskensu Ya bar su cikin duffai ba sa gani



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 18

صُمُّۢ بُكۡمٌ عُمۡيٞ فَهُمۡ لَا يَرۡجِعُونَ

( Su ) kurame ne, bebaye ne, makafi ne, don haka ba za su tava dawowa (kan gaskiya) ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 19

أَوۡ كَصَيِّبٖ مِّنَ ٱلسَّمَآءِ فِيهِ ظُلُمَٰتٞ وَرَعۡدٞ وَبَرۡقٞ يَجۡعَلُونَ أَصَٰبِعَهُمۡ فِيٓ ءَاذَانِهِم مِّنَ ٱلصَّوَٰعِقِ حَذَرَ ٱلۡمَوۡتِۚ وَٱللَّهُ مُحِيطُۢ بِٱلۡكَٰفِرِينَ

Ko kuma (misalinsu) kamar wani mamakon ruwan sama ne, wanda yake xauke da duffai da tsawa da walqiya, har ta kai suna sanya ‘yan yatsunsu cikin kunnuwansu don tsananin tsawarwaki saboda tsoron mutuwa. Allah Kuma Yana kewaye da kafirai (da iliminsa)



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 20

يَكَادُ ٱلۡبَرۡقُ يَخۡطَفُ أَبۡصَٰرَهُمۡۖ كُلَّمَآ أَضَآءَ لَهُم مَّشَوۡاْ فِيهِ وَإِذَآ أَظۡلَمَ عَلَيۡهِمۡ قَامُواْۚ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَذَهَبَ بِسَمۡعِهِمۡ وَأَبۡصَٰرِهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Walqiyar ta kusa ta fauce idanuwansu. Duk sa›adda ta haska musu sai su ci gaba da tafiya cikin (haskenta); idan kuma ta rufe su da duhu sai su tsaya cak. Da kuwa Allah Ya ga dama da sai Ya tafiyar da jinsu da ganinsu. Lalle Allah Mai iko ne a kan komai



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 21

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱعۡبُدُواْ رَبَّكُمُ ٱلَّذِي خَلَقَكُمۡ وَٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تَتَّقُونَ

Ya ku mutane, ku bauta wa Ubangijinku Wanda Ya halicce ku, da waxanda suka gabace ku, don ku samu taqawa



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 22

ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلۡأَرۡضَ فِرَٰشٗا وَٱلسَّمَآءَ بِنَآءٗ وَأَنزَلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَأَخۡرَجَ بِهِۦ مِنَ ٱلثَّمَرَٰتِ رِزۡقٗا لَّكُمۡۖ فَلَا تَجۡعَلُواْ لِلَّهِ أَندَادٗا وَأَنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Shi ne Wanda Ya sanya muku qasa ta zama shimfixa kuma Ya sanya muku sama ta zama gini kuma Ya saukar da ruwa daga sama Ya fitar muku da arziqi na ‘ya’yan itatuwa, don haka kada ku sanya wa Allah kishiyoyi alhalin kuna sane



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 23

وَإِن كُنتُمۡ فِي رَيۡبٖ مِّمَّا نَزَّلۡنَا عَلَىٰ عَبۡدِنَا فَأۡتُواْ بِسُورَةٖ مِّن مِّثۡلِهِۦ وَٱدۡعُواْ شُهَدَآءَكُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Kuma idan kun kasance cikin kokwanto game da abin da Muka saukar wa bawanmu, to ku zo da kwatankwacin sura xaya kamarsa, kuma ku kirawo masu taimakonku ba Allah ba in kun kasance masu gaskiya



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 24

فَإِن لَّمۡ تَفۡعَلُواْ وَلَن تَفۡعَلُواْ فَٱتَّقُواْ ٱلنَّارَ ٱلَّتِي وَقُودُهَا ٱلنَّاسُ وَٱلۡحِجَارَةُۖ أُعِدَّتۡ لِلۡكَٰفِرِينَ

To idan har ba ku aikata hakan ba, kuma ba za ku tava iyawa ba, to ku kiyayi wata wuta wadda mutane ne da duwatsu makamashinta; an kuwa tanade ta domin kafirai



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 25

وَبَشِّرِ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أَنَّ لَهُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۖ كُلَّمَا رُزِقُواْ مِنۡهَا مِن ثَمَرَةٖ رِّزۡقٗا قَالُواْ هَٰذَا ٱلَّذِي رُزِقۡنَا مِن قَبۡلُۖ وَأُتُواْ بِهِۦ مُتَشَٰبِهٗاۖ وَلَهُمۡ فِيهَآ أَزۡوَٰجٞ مُّطَهَّرَةٞۖ وَهُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Kuma ka yi albishir ga waxanda suka yi imani kuma suka aikata ayyuka na qwarai cewa suna da wasu gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. Duk sa’adda aka arzuta su da ’ya’yan itatuwa daga gare su sai su ce: “Wannan shi ne irin abin da aka arzuta mu da shi xazu.” An kawo musu shi yana mai kama da juna, kuma suna da wasu mata tsarkaka a cikinsu, kuma su masu zama ne a cikinsu dindindin



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 26

۞إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَسۡتَحۡيِۦٓ أَن يَضۡرِبَ مَثَلٗا مَّا بَعُوضَةٗ فَمَا فَوۡقَهَاۚ فَأَمَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ فَيَعۡلَمُونَ أَنَّهُ ٱلۡحَقُّ مِن رَّبِّهِمۡۖ وَأَمَّا ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَيَقُولُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۘ يُضِلُّ بِهِۦ كَثِيرٗا وَيَهۡدِي بِهِۦ كَثِيرٗاۚ وَمَا يُضِلُّ بِهِۦٓ إِلَّا ٱلۡفَٰسِقِينَ

Lalle Allah ba Ya jin kunyar buga kowanne irin misali komai qanqantarsa, sauro da abin da ya fi shi. To amma waxanda suka yi imani suna sanin cewa, lalle shi (wannan misali) gaskiya ne daga Ubangijinsu. Amma waxanda suka kafirta sai su riqa cewa: “Me Allah Yake nufi da wannan misalin?” Yana kuwa vatar da mutane da yawa da shi, kuma Ya shiryar da mutane da yawa da shi, kuma ba kowa Yake vatarwa da shi ba sai fasiqai



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 27

ٱلَّذِينَ يَنقُضُونَ عَهۡدَ ٱللَّهِ مِنۢ بَعۡدِ مِيثَٰقِهِۦ وَيَقۡطَعُونَ مَآ أَمَرَ ٱللَّهُ بِهِۦٓ أَن يُوصَلَ وَيُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Waxanda suke warware alqawarin Allah bayan qulla shi, kuma suke yanke abin da Allah Ya yi umarni a sadar da shi, kuma suke varna a bayan qasa. Waxannan su ne cikakkun hasararru



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 28

كَيۡفَ تَكۡفُرُونَ بِٱللَّهِ وَكُنتُمۡ أَمۡوَٰتٗا فَأَحۡيَٰكُمۡۖ ثُمَّ يُمِيتُكُمۡ ثُمَّ يُحۡيِيكُمۡ ثُمَّ إِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Ta yaya kuke kafirce wa Allah alhalin a da kun kasance matattu, sannan Ya raya ku, sannan zai kuma mayar da ku matattu sannan Ya raya ku (a karo na biyu) sannan zuwa gare Shi ake mayar da ku?



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 29

هُوَ ٱلَّذِي خَلَقَ لَكُم مَّا فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰٓ إِلَى ٱلسَّمَآءِ فَسَوَّىٰهُنَّ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖۚ وَهُوَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Shi ne wanda Ya halitta muku abin da yake cikin qasa gaba xaya, sannan Ya nufi sama Ya daidaita su sammai bakwai, kuma Shi Masanin komai ne



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 30

وَإِذۡ قَالَ رَبُّكَ لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ إِنِّي جَاعِلٞ فِي ٱلۡأَرۡضِ خَلِيفَةٗۖ قَالُوٓاْ أَتَجۡعَلُ فِيهَا مَن يُفۡسِدُ فِيهَا وَيَسۡفِكُ ٱلدِّمَآءَ وَنَحۡنُ نُسَبِّحُ بِحَمۡدِكَ وَنُقَدِّسُ لَكَۖ قَالَ إِنِّيٓ أَعۡلَمُ مَا لَا تَعۡلَمُونَ

Kuma ka tuna sa’adda Ubangijinka Ya ce da mala’iku: “Lalle ni zan sanya wani halifa[1] a bayan qasa.” Suka ce: “Yanzu za Ka sanya mata wanda zai yi varna a cikinta kuma ya zubar da jini, alhali ga mu muna tasbihi tare da gode Maka, kuma muna tsarkake Ka?” (Allah) Ya ce: “Ni fa tabbas Na san abin da ku ba ku sani ba.”


1- Halifa, shi ne Annabi Adamu () da zuriyarsa, waxanda za su riqa maye gurbin juna a bayan qasa.