Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 1

الٓرۚ كِتَٰبٌ أَنزَلۡنَٰهُ إِلَيۡكَ لِتُخۡرِجَ ٱلنَّاسَ مِنَ ٱلظُّلُمَٰتِ إِلَى ٱلنُّورِ بِإِذۡنِ رَبِّهِمۡ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

ALIF LAM RA[1]. Littafi ne da Muka saukar maka da shi, don ka fitar da mutane daga duffai zuwa ga haske, da izinin Ubangijinsu zuwa ga tafarkin (Allah) Mabuwayi, Abin godiya


1- Duba Suratul Baqara aya ta 1, hashiya ta 8.


Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 2

ٱللَّهِ ٱلَّذِي لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۗ وَوَيۡلٞ لِّلۡكَٰفِرِينَ مِنۡ عَذَابٖ شَدِيدٍ

(Watau) Allah, Wanda abin da yake cikin sammai da na cikin qasa duka nasa ne. Bone na wata azaba mai tsanani kuma ya tabbatta ga kafirai



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 3

ٱلَّذِينَ يَسۡتَحِبُّونَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا عَلَى ٱلۡأٓخِرَةِ وَيَصُدُّونَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ وَيَبۡغُونَهَا عِوَجًاۚ أُوْلَـٰٓئِكَ فِي ضَلَٰلِۭ بَعِيدٖ

Waxanda suke fifita son rayuwar duniya a kan lahira, suke kuma hanawa (a bi) hanyar Allah, kuma suke neman ta zama karkatacciya. To waxannan suna cikin vata mai nisa



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 4

وَمَآ أَرۡسَلۡنَا مِن رَّسُولٍ إِلَّا بِلِسَانِ قَوۡمِهِۦ لِيُبَيِّنَ لَهُمۡۖ فَيُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Ba Mu tava aiko wani manzo ba kuwa sai da harshen mutanensa don ya yi musu bayani; sannan Allah Yana vatar da wanda ya ga dama, ya kuma shiryar da wanda ya ga dama. Shi ne kuwa Mabuwayi, Mai hikima



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 5

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا مُوسَىٰ بِـَٔايَٰتِنَآ أَنۡ أَخۡرِجۡ قَوۡمَكَ مِنَ ٱلظُّلُمَٰتِ إِلَى ٱلنُّورِ وَذَكِّرۡهُم بِأَيَّىٰمِ ٱللَّهِۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّكُلِّ صَبَّارٖ شَكُورٖ

Haqiqa kuma Mun aiko Musa da ayoyinmu cewa: “Ka fitar da mutananka daga duffai zuwa ga haske, kuma ka tunatar da su ni’imomin Allah (da ya yi musu).” Lalle game da wannan da akwai ayoyi ga duk wani mai yawan haquri, mai yawan godiya



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 6

وَإِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَةَ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡ إِذۡ أَنجَىٰكُم مِّنۡ ءَالِ فِرۡعَوۡنَ يَسُومُونَكُمۡ سُوٓءَ ٱلۡعَذَابِ وَيُذَبِّحُونَ أَبۡنَآءَكُمۡ وَيَسۡتَحۡيُونَ نِسَآءَكُمۡۚ وَفِي ذَٰلِكُم بَلَآءٞ مِّن رَّبِّكُمۡ عَظِيمٞ

Kuma (ka tuna) lokacin da Musa ya ce da mutanensa: “Ku tuna ni’imar Allah a gare ku lokacin da Ya tserar da ku daga mutanen Fir’auna, suna gana muku azaba, suna kuma yanyanka ‘ya’yanku, kuma suna raya matayenku. A game da wannan da akwai bala’i mai girma daga Ubangijinku



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 7

وَإِذۡ تَأَذَّنَ رَبُّكُمۡ لَئِن شَكَرۡتُمۡ لَأَزِيدَنَّكُمۡۖ وَلَئِن كَفَرۡتُمۡ إِنَّ عَذَابِي لَشَدِيدٞ

“Kuma (ku tuna) lokacin da Ubangijinku ya sanar da ku: “Lalle idan kuka gode wa (ni’imata) tabbas zan qara muku; idan kuwa kuka butulce, to lalle azabata tabbas mai tsanani ce.”



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 8

وَقَالَ مُوسَىٰٓ إِن تَكۡفُرُوٓاْ أَنتُمۡ وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا فَإِنَّ ٱللَّهَ لَغَنِيٌّ حَمِيدٌ

Musa kuma ya ce: “Idan kuka kafirce, ku da waxanda suke a bayan qasa baki xaya, to lalle Allah tabbas Mawadaci ne, Sha-yabo.”



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 9

أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ نَبَؤُاْ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِكُمۡ قَوۡمِ نُوحٖ وَعَادٖ وَثَمُودَ وَٱلَّذِينَ مِنۢ بَعۡدِهِمۡ لَا يَعۡلَمُهُمۡ إِلَّا ٱللَّهُۚ جَآءَتۡهُمۡ رُسُلُهُم بِٱلۡبَيِّنَٰتِ فَرَدُّوٓاْ أَيۡدِيَهُمۡ فِيٓ أَفۡوَٰهِهِمۡ وَقَالُوٓاْ إِنَّا كَفَرۡنَا بِمَآ أُرۡسِلۡتُم بِهِۦ وَإِنَّا لَفِي شَكّٖ مِّمَّا تَدۡعُونَنَآ إِلَيۡهِ مُرِيبٖ

Wai yanzu labarin waxanda suka gabace ku bai zo muku ba na mutanen Nuhu da Adawa da Samudawa da waxanda (suka zo) daga bayansu? Ba wanda ya san iyakarsu sai Allah. Manzanninsu sun zo musu da hujjoji bayyanannu, amma sai suka riqa cizon hannayensu (saboda haushi), suka kuma ce: “Lalle mu kam mun kafirta da abin da aka aiko ku da shi, lalle kuma muna cikin matuqar shakka game abin da kuke kiran mu zuwa gare shi.”



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 10

۞قَالَتۡ رُسُلُهُمۡ أَفِي ٱللَّهِ شَكّٞ فَاطِرِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ يَدۡعُوكُمۡ لِيَغۡفِرَ لَكُم مِّن ذُنُوبِكُمۡ وَيُؤَخِّرَكُمۡ إِلَىٰٓ أَجَلٖ مُّسَمّٗىۚ قَالُوٓاْ إِنۡ أَنتُمۡ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا تُرِيدُونَ أَن تَصُدُّونَا عَمَّا كَانَ يَعۡبُدُ ءَابَآؤُنَا فَأۡتُونَا بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٖ

Mazanninsu suka ce: “Yanzu kuwa ashe akwai wata shakka game da Allah, Maqagin sammai da qasa? Yana kiran ku ne don ya gafarta muku zunubanku kuma ya saurara muku har zuwa wani lokaci qayyadajje.” Suka ce: “Ku ba wasu ba ne daban in ban da mutane kamar mu, kuna so ne ku hana mu bin abin da iyanenmu suka kasance suna bauta wa, to sai ku kawo mana hujjoji bayyanannu.”



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 11

قَالَتۡ لَهُمۡ رُسُلُهُمۡ إِن نَّحۡنُ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُكُمۡ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ يَمُنُّ عَلَىٰ مَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦۖ وَمَا كَانَ لَنَآ أَن نَّأۡتِيَكُم بِسُلۡطَٰنٍ إِلَّا بِإِذۡنِ ٱللَّهِۚ وَعَلَى ٱللَّهِ فَلۡيَتَوَكَّلِ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ

Manzanninsu suka ce: “Mu ba kowa ba ne in ban da mutane kamarku, sai dai Allah Yana yin baiwa ga wanda Ya ga dama ne daga bayinsa, kuma ba zai yiwu ba a gare mu mu zo muku da wata hujja sai dai da izinin Allah. Muminai kuwa lalle su dogara ga Allah kawai



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 12

وَمَا لَنَآ أَلَّا نَتَوَكَّلَ عَلَى ٱللَّهِ وَقَدۡ هَدَىٰنَا سُبُلَنَاۚ وَلَنَصۡبِرَنَّ عَلَىٰ مَآ ءَاذَيۡتُمُونَاۚ وَعَلَى ٱللَّهِ فَلۡيَتَوَكَّلِ ٱلۡمُتَوَكِّلُونَ

“Kuma me zai hana mu mu dogara ga Allah, alhali kuwa haqiqa Ya shiryar da mu hanyoyinmu? Lalle kuwa tabbas za mu yi haquri bisa irin cutar mu da kuka yi. Masu dogaro kuma sai su dogara ga Allah kaxai.”



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 13

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لِرُسُلِهِمۡ لَنُخۡرِجَنَّكُم مِّنۡ أَرۡضِنَآ أَوۡ لَتَعُودُنَّ فِي مِلَّتِنَاۖ فَأَوۡحَىٰٓ إِلَيۡهِمۡ رَبُّهُمۡ لَنُهۡلِكَنَّ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Waxanda suka kafirta kuma suka ce da manzanninsu: “Lalle ba makawa za mu fitar da ku daga qasarmu, ko kuwa lalle ku komo cikin addininmu. Sai Ubangijinsu ya aiko musu cewa: “Lalle za Mu hallaka azzalumai



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 14

وَلَنُسۡكِنَنَّكُمُ ٱلۡأَرۡضَ مِنۢ بَعۡدِهِمۡۚ ذَٰلِكَ لِمَنۡ خَافَ مَقَامِي وَخَافَ وَعِيدِ

“Kuma tabbas za mu zaunar da ku qasar (tasu) a bayansu. Wannan kuwa sai ga wanda ya ji tsoron tsayuwa a gabana ya kuma ji tsoron narkona.”



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 15

وَٱسۡتَفۡتَحُواْ وَخَابَ كُلُّ جَبَّارٍ عَنِيدٖ

Sai kuma (manzannin) suka nemi nasarar (Allah), kuma (a qarshenta) duk wani mai nuna isa mai taurin kai ya hallaka



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 16

مِّن وَرَآئِهِۦ جَهَنَّمُ وَيُسۡقَىٰ مِن مَّآءٖ صَدِيدٖ

A gabansa Jahannama ce (take jiran sa), za a kuma shayar da shi ruwan mugunya



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 17

يَتَجَرَّعُهُۥ وَلَا يَكَادُ يُسِيغُهُۥ وَيَأۡتِيهِ ٱلۡمَوۡتُ مِن كُلِّ مَكَانٖ وَمَا هُوَ بِمَيِّتٖۖ وَمِن وَرَآئِهِۦ عَذَابٌ غَلِيظٞ

Yana kwankwaxar sa, ba kuwa zai ji daxin haxiyarsa ba, mutuwa kuma za ta zo masa ko ta ina, ba kuwa zai mutu ba; kuma a gabansa ga azaba mai kauri



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 18

مَّثَلُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِرَبِّهِمۡۖ أَعۡمَٰلُهُمۡ كَرَمَادٍ ٱشۡتَدَّتۡ بِهِ ٱلرِّيحُ فِي يَوۡمٍ عَاصِفٖۖ لَّا يَقۡدِرُونَ مِمَّا كَسَبُواْ عَلَىٰ شَيۡءٖۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلضَّلَٰلُ ٱلۡبَعِيدُ

Misalin waxanda suka kafirce wa Ubangijnsu; ayyukansu sun yi kama da toka wadda iska mai tsananin qarfi ta kwasa a wata rana mai guguwa; ba za su sami iko a kan komai ba dangane da abin da suka aikata (na kirki). Wannan shi ne vata mai nisa



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 19

أَلَمۡ تَرَ أَنَّ ٱللَّهَ خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۚ إِن يَشَأۡ يُذۡهِبۡكُمۡ وَيَأۡتِ بِخَلۡقٖ جَدِيدٖ

Ashe ba ka ga cewa, lalle Allah Ya halicci sammai da qasa kan gaskiya ba? Idan Ya ga dama sai Ya hallakar da ku Ya kuma zo da wata halitta sabuwa



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 20

وَمَا ذَٰلِكَ عَلَى ٱللَّهِ بِعَزِيزٖ

Wannan kuwa ba abin da zai gagari Allah ba ne



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 21

وَبَرَزُواْ لِلَّهِ جَمِيعٗا فَقَالَ ٱلضُّعَفَـٰٓؤُاْ لِلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُوٓاْ إِنَّا كُنَّا لَكُمۡ تَبَعٗا فَهَلۡ أَنتُم مُّغۡنُونَ عَنَّا مِنۡ عَذَابِ ٱللَّهِ مِن شَيۡءٖۚ قَالُواْ لَوۡ هَدَىٰنَا ٱللَّهُ لَهَدَيۡنَٰكُمۡۖ سَوَآءٌ عَلَيۡنَآ أَجَزِعۡنَآ أَمۡ صَبَرۡنَا مَا لَنَا مِن مَّحِيصٖ

Suka kuma fito gaba xaya a gaban Allah (ranar alqiyama), sai raunanan suka ce da waxanda suka yi girman kai: “Lalle mu mun zamanto mabiya a gare ku, to ko za ku maganta mana wani abu daga azabar Allah?” Suka ce: “Da Allah Ya shirye mu da lalle mun shiryar da ku; duka xaya ne gare mu ko mun yi raki ko mun yi haquri (duka dai) ba mu da wata maguda.”



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 22

وَقَالَ ٱلشَّيۡطَٰنُ لَمَّا قُضِيَ ٱلۡأَمۡرُ إِنَّ ٱللَّهَ وَعَدَكُمۡ وَعۡدَ ٱلۡحَقِّ وَوَعَدتُّكُمۡ فَأَخۡلَفۡتُكُمۡۖ وَمَا كَانَ لِيَ عَلَيۡكُم مِّن سُلۡطَٰنٍ إِلَّآ أَن دَعَوۡتُكُمۡ فَٱسۡتَجَبۡتُمۡ لِيۖ فَلَا تَلُومُونِي وَلُومُوٓاْ أَنفُسَكُمۖ مَّآ أَنَا۠ بِمُصۡرِخِكُمۡ وَمَآ أَنتُم بِمُصۡرِخِيَّ إِنِّي كَفَرۡتُ بِمَآ أَشۡرَكۡتُمُونِ مِن قَبۡلُۗ إِنَّ ٱلظَّـٰلِمِينَ لَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Shaixan kuma lokacin da aka gama hukunci ya ce: “Lalle Allah Ya yi muku alqawari na gaskiya, ni kuma na yi muku alqawari sai na sava muku. To ba ni da wani qarfi da na nuna muku, sai dai na yi kiran ku ne sai kuka amsa mini; to kada ku zarge ni, ku zargi kanku; ni ba zan taimake ku ba, ku kuma ba za ku taimake ni ba. Lalle ni na riga na kafirta da abin da kuka yi tarayya da ni a kansa tun a da can. Lalle azzalumai suna da (sakamakon) azaba mai raxaxi.”



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 23

وَأُدۡخِلَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَا بِإِذۡنِ رَبِّهِمۡۖ تَحِيَّتُهُمۡ فِيهَا سَلَٰمٌ

Aka kuma shigar da waxanda suka yi imani, suka kuma yi aiki nagari gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, suna masu dawwama a cikinsu da izinin Ubangijinsu; gaisuwarsu a cikinsu ita ce: “Aminci (ya tabbata a gare ku).”



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 24

أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ ضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا كَلِمَةٗ طَيِّبَةٗ كَشَجَرَةٖ طَيِّبَةٍ أَصۡلُهَا ثَابِتٞ وَفَرۡعُهَا فِي ٱلسَّمَآءِ

Shin ba ka ga yadda Allah Ya ba da misali ba? Daddaxar kalma[1] kamar daddaxar bishiya ce[2] wadda tushenta kafaffe ne (a qasa) reshenta kuma yana sama


1- Daddaxar kalma ita ce kalmar shahada, watau shaidawa babu abin bauta da gaskiya sai Allah.


2- Daddaxar bishiya kuwa ita ce bishiyar dabino. A nan ana nufin mumini. Kalmar shahada tana kafa tushenta a ciki zuciyar mumini.


Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 25

تُؤۡتِيٓ أُكُلَهَا كُلَّ حِينِۭ بِإِذۡنِ رَبِّهَاۗ وَيَضۡرِبُ ٱللَّهُ ٱلۡأَمۡثَالَ لِلنَّاسِ لَعَلَّهُمۡ يَتَذَكَّرُونَ

Tana bayar da ‘ya’yanta ko da yaushe da izinin Ubangijinta. Allah kuwa Yana ba da misalai ne ga mutane don su wa’azantu



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 26

وَمَثَلُ كَلِمَةٍ خَبِيثَةٖ كَشَجَرَةٍ خَبِيثَةٍ ٱجۡتُثَّتۡ مِن فَوۡقِ ٱلۡأَرۡضِ مَا لَهَا مِن قَرَارٖ

Misalin kuma mummunar kalma kamar mummunar bishiya ce da aka tumvuke daga kan qasa, ba ta da wata matabbata



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 27

يُثَبِّتُ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱلۡقَوۡلِ ٱلثَّابِتِ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَفِي ٱلۡأٓخِرَةِۖ وَيُضِلُّ ٱللَّهُ ٱلظَّـٰلِمِينَۚ وَيَفۡعَلُ ٱللَّهُ مَا يَشَآءُ

Allah Yana tabbatar da waxanda suka yi imani a kan magana tabbatacciya a rayuwar duniya da kuma a lahira; Yana kuma vatar da azzalumai. Allah kuma Yana aikata abin da Ya ga dama



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 28

۞أَلَمۡ تَرَ إِلَى ٱلَّذِينَ بَدَّلُواْ نِعۡمَتَ ٱللَّهِ كُفۡرٗا وَأَحَلُّواْ قَوۡمَهُمۡ دَارَ ٱلۡبَوَارِ

Shin ba ka ga waxanda suka musanya ni’imar Allah da kafirci ba[1], suka kuma jefa mutanensu gidan hallaka?


1- Su ne kafiran Quraishawa.


Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 29

جَهَنَّمَ يَصۡلَوۡنَهَاۖ وَبِئۡسَ ٱلۡقَرَارُ

(Watau) Jahannama, za su shige ta; makoma kuwa ta munana



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 30

وَجَعَلُواْ لِلَّهِ أَندَادٗا لِّيُضِلُّواْ عَن سَبِيلِهِۦۗ قُلۡ تَمَتَّعُواْ فَإِنَّ مَصِيرَكُمۡ إِلَى ٱلنَّارِ

Sun sanya wa Allah abokan tarayya don su vatar (da mutane) daga hanyarsa. Ka ce: “Ku ji daxi (kaxan a duniya), to lalle makomarku wuta ce!”