Surah: Suratul Fatiha

Ayah : 1

بِسۡمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحۡمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin qai[1]


1- Bisimilla Alqur’ani ce, kuma aya ce a ‘Suratun Namli aya ta 30’; sannan ita aya ce a farkon ‘Suratul Fatiha’, sannan an saukar da ita a farkon kowace sura don bambance tsakanin qarshen sura da farkon wata sura. Amma ban da tsakanin ‘Suratul Anfal’ da ‘Taubah’.


Surah: Suratul Fatiha

Ayah : 2

ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai



Surah: Suratul Fatiha

Ayah : 3

ٱلرَّحۡمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

Mai rahama Mai jin qai[1]


1- Allah, suna ne na wanda ya cancanta a bauta masa shi kaxai. Ba a kiran wani da shi. Arrahman wanda yake nuna yalwatacciyar rahmar Allah wadda take shafar kowa da komai a nan duniya da kuma sunansa Arrahim, wanda yake nuna kevantacciyar rahamarsa a lahira ga muminai kawai masu tsoran sa.


Surah: Suratul Fatiha

Ayah : 4

مَٰلِكِ يَوۡمِ ٱلدِّينِ

Mamallakin ranar sakamako



Surah: Suratul Fatiha

Ayah : 5

إِيَّاكَ نَعۡبُدُ وَإِيَّاكَ نَسۡتَعِينُ

Kai kaxai muke bautata wa, kuma Kai kaxai muke neman taimakonka



Surah: Suratul Fatiha

Ayah : 6

ٱهۡدِنَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلۡمُسۡتَقِيمَ

Ka shiryar da mu tafarkin nan madaidaici



Surah: Suratul Fatiha

Ayah : 7

صِرَٰطَ ٱلَّذِينَ أَنۡعَمۡتَ عَلَيۡهِمۡ غَيۡرِ ٱلۡمَغۡضُوبِ عَلَيۡهِمۡ وَلَا ٱلضَّآلِّينَ

Tafarkin waxanda Ka yi wa ni’ima[1], ba waxanda aka yi fushi da su ba[2], ba kuma vatattu ba[3]


1- Su ne waxanda aka ambata a aya ta 69 a Suratun Nisa’i.


2- Watau waxanda suka san gaskiya suka take, kamar Yahudawa.


3- Watau waxanda suke bautar Allah da jahilci, kamar Nasara.