Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 211

وَمَا يَنۢبَغِي لَهُمۡ وَمَا يَسۡتَطِيعُونَ

Kuma bai kamace su ba, ba kuma za su iya ba



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 212

إِنَّهُمۡ عَنِ ٱلسَّمۡعِ لَمَعۡزُولُونَ

Lalle su ababen kangewa ne daga jin (wahayi)



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 213

فَلَا تَدۡعُ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ فَتَكُونَ مِنَ ٱلۡمُعَذَّبِينَ

To kada ka bauta wa wani tare da Allah, sai ka zamanto daga waxanda za a yi wa azaba



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 214

وَأَنذِرۡ عَشِيرَتَكَ ٱلۡأَقۡرَبِينَ

Kuma ka gargaxi danginka mafiya kusanci



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 215

وَٱخۡفِضۡ جَنَاحَكَ لِمَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Ka kuma tausasa ga wanda ya bi ka daga muminai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 216

فَإِنۡ عَصَوۡكَ فَقُلۡ إِنِّي بَرِيٓءٞ مِّمَّا تَعۡمَلُونَ

To idan suka sava maka sai ka ce: “Ni lalle ba ruwana da abin da kuke aikatawa.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 217

وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱلۡعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ

Ka kuma dogara ga Mabuwayi, Mai rahama



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 218

ٱلَّذِي يَرَىٰكَ حِينَ تَقُومُ

Wanda Yake ganin ka yayin da kake tashi (don yin salla)



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 219

وَتَقَلُّبَكَ فِي ٱلسَّـٰجِدِينَ

Da kuma (yayin) jujjuyawarka cikin masu sujjada[1]


1- Watau masallata a sallar jam’i.


Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 220

إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Haqiqa Shi Mai ji ne, Masani



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 221

هَلۡ أُنَبِّئُكُمۡ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ ٱلشَّيَٰطِينُ

Shin ba Na ba ku labari ba game da wanda shexanu suke saukar masa?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 222

تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٖ

Suna sauka ne a kan duk wani maqaryaci mai yawan laifi



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 223

يُلۡقُونَ ٱلسَّمۡعَ وَأَكۡثَرُهُمۡ كَٰذِبُونَ

Suna jefa wa (bokaye) abin da suka sato jinsa, yawancinsu kuwa maqaryata ne



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 224

وَٱلشُّعَرَآءُ يَتَّبِعُهُمُ ٱلۡغَاوُۥنَ

Mawaqa kuwa vatattu ne suke bin su



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 225

أَلَمۡ تَرَ أَنَّهُمۡ فِي كُلِّ وَادٖ يَهِيمُونَ

Ba ka ga cewa su kutsawa suke yi cikin kowanne kwari ba[1]?


1- Watau suna kutsawa cikin kowane saqo-saqo na waqe-waqe, wani lokaci ta hanyar yabo, wani lokaci kuma ya hanyar zambo ko alfahari, su faxi qarya da gaskiya.


Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 226

وَأَنَّهُمۡ يَقُولُونَ مَا لَا يَفۡعَلُونَ

Lalle kuma suna faxar abin da ba sa aikatawa



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 227

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَذَكَرُواْ ٱللَّهَ كَثِيرٗا وَٱنتَصَرُواْ مِنۢ بَعۡدِ مَا ظُلِمُواْۗ وَسَيَعۡلَمُ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ أَيَّ مُنقَلَبٖ يَنقَلِبُونَ

Sai dai waxanda suka yi imani kuma suka yi aiki nagari, kuma suka ambaci Allah da yawa, suka kuma yi sakayya bayan an zalunce su[1]. Waxanda suka yi zalunci kuwa ba da daxewa ba za su san kowace makomar za su koma


1- Watau mawaqan Musulmi waxanda suke mayar da martani a kan mawaqan kafirai masu sukan Musulunci.