Surah: Suratus Saffat

Ayah : 121

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 122

إِنَّهُمَا مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle suna daga cikin bayinmu muminai



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 123

وَإِنَّ إِلۡيَاسَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Kuma lalle Ilyasu tabbas yana daga cikin manzanni



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 124

إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِۦٓ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da ya ce da mutanensa: “Yanzu ba za ku kiyaye dokokin (Allah) ba?



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 125

أَتَدۡعُونَ بَعۡلٗا وَتَذَرُونَ أَحۡسَنَ ٱلۡخَٰلِقِينَ

“Yanzu kwa riqa bauta wa (gunkin) Ba’alu ku riqa barin Mafi iya kyautata halitta?



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 126

ٱللَّهَ رَبَّكُمۡ وَرَبَّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ

“(Wato) Allah Ubangijinku kuma Ubangijin iyayenku na farko?”



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 127

فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمۡ لَمُحۡضَرُونَ

Sai suka qaryata shi, to don haka, lalle za a halarto da su (wuta)



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 128

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Sai dai bayin Allah waxanda aka tsarkake



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 129

وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

Muka kuma bar (kyakkyawan yabo) a gare shi ga ‘yan baya



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 130

سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِلۡ يَاسِينَ

Aminci ya tabbata ga Ilyasu



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 131

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 132

إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle shi yana daga bayinmu muminai



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 133

وَإِنَّ لُوطٗا لَّمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Lalle kuma Luxu tabbas yana daga cikin manzanni



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 134

إِذۡ نَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

(Ka tuna) sanda Muka tserar da shi tare da iyalinsa baki xaya



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 135

إِلَّا عَجُوزٗا فِي ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai dai wata tsohuwa (wato matarsa) da take cikin halakakku



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 136

ثُمَّ دَمَّرۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka hallakar da sauran



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 137

وَإِنَّكُمۡ لَتَمُرُّونَ عَلَيۡهِم مُّصۡبِحِينَ

Kuma lalle ku[1] tabbas kuna wucewa ta wajan (gidajensu) da asussuba


1- Watau ku mutanen Makka.


Surah: Suratus Saffat

Ayah : 138

وَبِٱلَّيۡلِۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Da kuma cikin dare. Yanzu ba kwa hankalta ba?



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 139

وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Kuma lalle Yunusa tabbas yana daga cikin manzanni



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 140

إِذۡ أَبَقَ إِلَى ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ

(Ka tuna) lokacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwan da yake maqare



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 141

فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ ٱلۡمُدۡحَضِينَ

Sannan ya shiga quri’a, sai ya zama cikin waxanda aka yi galaba a kansu



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 142

فَٱلۡتَقَمَهُ ٱلۡحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٞ

Sai kifi ya haxiye shi, alhali yana abin zargi[1]


1- Watau a kan guduwa ya bar mutanensa ba tare da izinin Allah ba.


Surah: Suratus Saffat

Ayah : 143

فَلَوۡلَآ أَنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلۡمُسَبِّحِينَ

Ba don dai shi ya zama daga masu tsarkake Allah (da yawan tasbihi) ba



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 144

لَلَبِثَ فِي بَطۡنِهِۦٓ إِلَىٰ يَوۡمِ يُبۡعَثُونَ

Tabbas da ya zauna a cikin cikinsa har zuwa ranar da za a tashe su[1]


1- Watau ranar alqiyama, domin zai zama shi ne qabarinsa.


Surah: Suratus Saffat

Ayah : 145

۞فَنَبَذۡنَٰهُ بِٱلۡعَرَآءِ وَهُوَ سَقِيمٞ

Sai Muka jefa shi a tudu, a halin yana cikin rashin lafiya



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 146

وَأَنۢبَتۡنَا عَلَيۡهِ شَجَرَةٗ مِّن يَقۡطِينٖ

Muka kuma tsirar masa wata bishiya ta kabewa[1]


1- Domin ya rufe tsiraicinsa da ganyenta, ya kuma ci ‘ya’yanta, ya kuma sha inuwarta.


Surah: Suratus Saffat

Ayah : 147

وَأَرۡسَلۡنَٰهُ إِلَىٰ مِاْئَةِ أَلۡفٍ أَوۡ يَزِيدُونَ

Muka kuma aika shi zuwa ga mutum dubu xari, ko kuma sama da haka



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 148

فَـَٔامَنُواْ فَمَتَّعۡنَٰهُمۡ إِلَىٰ حِينٖ

Sai suka yi imani, sai Muka jiyar da su daxi har zuwa wani lokaci



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 149

فَٱسۡتَفۡتِهِمۡ أَلِرَبِّكَ ٱلۡبَنَاتُ وَلَهُمُ ٱلۡبَنُونَ

Ka tambaye su: Yanzu Ubangijinka ne Yake da ‘ya’ya mata, su kuma suna da ‘ya’ya maza[1]?


1- Mushirikan Larabawa suna cewa mala’iku mata ne kuma ‘ya’yan Allah ne, yayin da sus uke fifita ‘ya’ya maza ga kawunansu.


Surah: Suratus Saffat

Ayah : 150

أَمۡ خَلَقۡنَا ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ إِنَٰثٗا وَهُمۡ شَٰهِدُونَ

Ko kuma Mun halicci mala’iku ne ‘ya’ya mata a gaban idonsu suna gani?