Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 91

كَذَٰلِكَۖ وَقَدۡ أَحَطۡنَا بِمَا لَدَيۡهِ خُبۡرٗا

Kamar haka (ya yi hukunci watau irin yadda ya yi a mafaxar rana), haqiqa kuma Mun kewaye da sanin (duk) abin da ke tare da shi (Zulqarnaini)



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 92

ثُمَّ أَتۡبَعَ سَبَبًا

Sannan ya kama hanya



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 93

حَتَّىٰٓ إِذَا بَلَغَ بَيۡنَ ٱلسَّدَّيۡنِ وَجَدَ مِن دُونِهِمَا قَوۡمٗا لَّا يَكَادُونَ يَفۡقَهُونَ قَوۡلٗا

Har ya iso (wani gari) tsakanin duwatsu biyu, ya kuma sami wasu mutane a gabansu (watau duwatsun) waxanda ba sa fahimtar wata magana



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 94

قَالُواْ يَٰذَا ٱلۡقَرۡنَيۡنِ إِنَّ يَأۡجُوجَ وَمَأۡجُوجَ مُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَهَلۡ نَجۡعَلُ لَكَ خَرۡجًا عَلَىٰٓ أَن تَجۡعَلَ بَيۡنَنَا وَبَيۡنَهُمۡ سَدّٗا

Suka ce: “Ya Zulqarnaini, lalle Yajuju da Majuju (mutane ne) masu varna a bayan qasa, to ko za mu iya biyan ka wata jinga don ka sanya wani shamaki tsakaninmu da su?”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 95

قَالَ مَا مَكَّنِّي فِيهِ رَبِّي خَيۡرٞ فَأَعِينُونِي بِقُوَّةٍ أَجۡعَلۡ بَيۡنَكُمۡ وَبَيۡنَهُمۡ رَدۡمًا

Ya ce, “Abin da Ubangijina Ya ba ni ya fi (abin da za ku ba ni), sai dai ku taimake ni da qarfi (don) in sanya shamaki tsakaninku da su



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 96

ءَاتُونِي زُبَرَ ٱلۡحَدِيدِۖ حَتَّىٰٓ إِذَا سَاوَىٰ بَيۡنَ ٱلصَّدَفَيۡنِ قَالَ ٱنفُخُواْۖ حَتَّىٰٓ إِذَا جَعَلَهُۥ نَارٗا قَالَ ءَاتُونِيٓ أُفۡرِغۡ عَلَيۡهِ قِطۡرٗا

“Ku kawo mini guntattakin qarafa”; har dai lokacin da ya daidaita (ginin da) duwatsun nan biyu, sai ya ce: “Ku hura wuta da zugazuginku”; har dai yayin da ya mai da shi wuta, sai ya ce: “Ku kawo min narkakkiyar dalma in zuba a kansu.”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 97

فَمَا ٱسۡطَٰعُوٓاْ أَن يَظۡهَرُوهُ وَمَا ٱسۡتَطَٰعُواْ لَهُۥ نَقۡبٗا

Saboda haka ba su samu ikon su haura shi ba, ba su kuma sami ikon huda shi ba



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 98

قَالَ هَٰذَا رَحۡمَةٞ مِّن رَّبِّيۖ فَإِذَا جَآءَ وَعۡدُ رَبِّي جَعَلَهُۥ دَكَّآءَۖ وَكَانَ وَعۡدُ رَبِّي حَقّٗا

Ya ce, “Wannan rahama ce daga Ubangijina; sai dai idan alqawarin Ubangijina ya zo, (watau tashin alqiyama) to zai mai da shi daga-daga; alqawarin Ubangijina kuwa ya tabbata gaskiya ne.”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 99

۞وَتَرَكۡنَا بَعۡضَهُمۡ يَوۡمَئِذٖ يَمُوجُ فِي بَعۡضٖۖ وَنُفِخَ فِي ٱلصُّورِ فَجَمَعۡنَٰهُمۡ جَمۡعٗا

Kuma Muka bar sashinsu (mutane) a wannan rana yana cakuxa da wani sashi[1]; aka kuma busa qaho, sannan Muka tattara su gaba xaya


1- Wannan zai iya xaukar ma’anar cewa, ranar da Yajuju da Majuju za su fito da yawa suna gauraya da mutane suna masu varna. A wata ma’anar kuma ana nufin ranar alqiyama da mutane da aljannu za su gauraya da juna wuri xaya.


Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 100

وَعَرَضۡنَا جَهَنَّمَ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡكَٰفِرِينَ عَرۡضًا

Muka kuma bijiro da (wutar) Jahannama a wannan ranar ga kafirai (su gan ta) quru-quru



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 101

ٱلَّذِينَ كَانَتۡ أَعۡيُنُهُمۡ فِي غِطَآءٍ عَن ذِكۡرِي وَكَانُواْ لَا يَسۡتَطِيعُونَ سَمۡعًا

(Su ne) waxanda idanuwansu suka makance daga ambatona, suka kuma kasance ba sa iya jin (gaskiya)



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 102

أَفَحَسِبَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَن يَتَّخِذُواْ عِبَادِي مِن دُونِيٓ أَوۡلِيَآءَۚ إِنَّآ أَعۡتَدۡنَا جَهَنَّمَ لِلۡكَٰفِرِينَ نُزُلٗا

Yanzu waxanda suka kafirta suna tsammanin su riqi wasu bayina ababen bauta ba Ni ba? Lalle Mun tanadi Jahannama ta zama masauki ga kafirai



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 103

قُلۡ هَلۡ نُنَبِّئُكُم بِٱلۡأَخۡسَرِينَ أَعۡمَٰلًا

Ka ce (da su): “Ba na ba ku labarin waxanda suka fi asarar ayyukansu ba?



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 104

ٱلَّذِينَ ضَلَّ سَعۡيُهُمۡ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَهُمۡ يَحۡسَبُونَ أَنَّهُمۡ يُحۡسِنُونَ صُنۡعًا

“(Su ne) waxanda aikinsu ya vace a rayuwarsu ta duniya alhali kuwa su suna tsammanin suna kyautata aiki ne.”



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 105

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِ رَبِّهِمۡ وَلِقَآئِهِۦ فَحَبِطَتۡ أَعۡمَٰلُهُمۡ فَلَا نُقِيمُ لَهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ وَزۡنٗا

Waxannan (su ne) waxanda suka kafirce wa ayoyin Ubangijinsu da kuma gamuwa da shi, sai ayyukansu suka lalace, ba za Mu sanya musu wani ma’auni ba a ranar alqiyama



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 106

ذَٰلِكَ جَزَآؤُهُمۡ جَهَنَّمُ بِمَا كَفَرُواْ وَٱتَّخَذُوٓاْ ءَايَٰتِي وَرُسُلِي هُزُوًا

Wannan shi ne sakamakonsu, Jahannama, saboda kafircewa da suka yi suka kuma riqi ayoyina da manzannina abin yi wa izgili



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 107

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ كَانَتۡ لَهُمۡ جَنَّـٰتُ ٱلۡفِرۡدَوۡسِ نُزُلًا

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari to Aljannar Firdausi[1] ita ce ta kasance masaukinsu


1- Aljannar Firdausi ita ce qololuwar Aljanna mafi daraja.


Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 108

خَٰلِدِينَ فِيهَا لَا يَبۡغُونَ عَنۡهَا حِوَلٗا

Suna masu dawwama a cikinta, ba sa neman wani musaya da ita



Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 109

قُل لَّوۡ كَانَ ٱلۡبَحۡرُ مِدَادٗا لِّكَلِمَٰتِ رَبِّي لَنَفِدَ ٱلۡبَحۡرُ قَبۡلَ أَن تَنفَدَ كَلِمَٰتُ رَبِّي وَلَوۡ جِئۡنَا بِمِثۡلِهِۦ مَدَدٗا

Ka ce (da su): “Da kogi zai zamanto tawada don (rubuta) kalmomin Ubangijina[1], to lalle da kogin ya qare kafin kalmomin Ubangijina su qare, ko da kuwa Mun zo da qarin wasu (koguna) kamarsa


1- Kalmomin Allah su ne yalwar siffofinsa da iliminsa da qudurarsa.


Surah: Suratul Kahf 

Ayah : 110

قُلۡ إِنَّمَآ أَنَا۠ بَشَرٞ مِّثۡلُكُمۡ يُوحَىٰٓ إِلَيَّ أَنَّمَآ إِلَٰهُكُمۡ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞۖ فَمَن كَانَ يَرۡجُواْ لِقَآءَ رَبِّهِۦ فَلۡيَعۡمَلۡ عَمَلٗا صَٰلِحٗا وَلَا يُشۡرِكۡ بِعِبَادَةِ رَبِّهِۦٓ أَحَدَۢا

Ka ce: “Ni dai mutum ne kawai kamarku da ake yi mini wahayi cewa abin bautarku abin bauta ne Xaya; don haka wanda ya kasance yana tsoron gamuwa da Ubangijinsa, to sai ya yi aiki nagari, kada kuma ya tara wani cikin bautar Ubangijinsa.”