Surah: Suratun Nahl

Ayah : 91

وَأَوۡفُواْ بِعَهۡدِ ٱللَّهِ إِذَا عَٰهَدتُّمۡ وَلَا تَنقُضُواْ ٱلۡأَيۡمَٰنَ بَعۡدَ تَوۡكِيدِهَا وَقَدۡ جَعَلۡتُمُ ٱللَّهَ عَلَيۡكُمۡ كَفِيلًاۚ إِنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُ مَا تَفۡعَلُونَ

Ku kuma cika alqawarin Allah idan kuka xauki alqawari, kada kuma ku warware rantsuwa bayan kun qarfafa ta, alhali kuwa kun sanya Allah shaida a kanku. Lalle Allah Yana sane da abin da kuke aikatawa



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 92

وَلَا تَكُونُواْ كَٱلَّتِي نَقَضَتۡ غَزۡلَهَا مِنۢ بَعۡدِ قُوَّةٍ أَنكَٰثٗا تَتَّخِذُونَ أَيۡمَٰنَكُمۡ دَخَلَۢا بَيۡنَكُمۡ أَن تَكُونَ أُمَّةٌ هِيَ أَرۡبَىٰ مِنۡ أُمَّةٍۚ إِنَّمَا يَبۡلُوكُمُ ٱللَّهُ بِهِۦۚ وَلَيُبَيِّنَنَّ لَكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ مَا كُنتُمۡ فِيهِ تَخۡتَلِفُونَ

Kada kuma ku zamanto kamar (mace) wadda ta warware kaxinta wara-wara bayan qarfinsa, kuna xaukar rantse-rantsenku yaudara a tsakaninku, don ganin kasancewar wata al’umma ta fi wata yawa da qarfi. Allah dai Yana jarabtar ku da shi (cika alqawari) ne. Don kuma a ranar alqiyama Ya bayyana muku abin da kuka kasance kuna savani a game da shi



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 93

وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَجَعَلَكُمۡ أُمَّةٗ وَٰحِدَةٗ وَلَٰكِن يُضِلُّ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَلَتُسۡـَٔلُنَّ عَمَّا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Da kuwa Allah Ya ga dama da Ya sanya ku al’umma xaya (masu addini xaya), sai dai kuma Yana vatar da wanda Ya ga dama Yana kuma shiryar da wanda Ya ga dama. Kuma tabbas za a tambaye ku game da abin da kuka kasance kuna aikatawa



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 94

وَلَا تَتَّخِذُوٓاْ أَيۡمَٰنَكُمۡ دَخَلَۢا بَيۡنَكُمۡ فَتَزِلَّ قَدَمُۢ بَعۡدَ ثُبُوتِهَا وَتَذُوقُواْ ٱلسُّوٓءَ بِمَا صَدَدتُّمۡ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ وَلَكُمۡ عَذَابٌ عَظِيمٞ

Kuma kada ku xauki rantse-rantsenku yaudara a tsakaninku, sai qafafuwanku su zame bayan tabbatarsu, kuma ku xanxani azaba saboda toshe hanyar Allah da kuka yi; kuma (a lahira) kuna da azaba mai girma



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 95

وَلَا تَشۡتَرُواْ بِعَهۡدِ ٱللَّهِ ثَمَنٗا قَلِيلًاۚ إِنَّمَا عِندَ ٱللَّهِ هُوَ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Kada kuma ku sayar da alqawarin Allah da xan kuxi qanqani. Lalle abin da yake wurin Allah shi ya fi muku alheri in kun kasance kun san (haka)



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 96

مَا عِندَكُمۡ يَنفَدُ وَمَا عِندَ ٱللَّهِ بَاقٖۗ وَلَنَجۡزِيَنَّ ٱلَّذِينَ صَبَرُوٓاْ أَجۡرَهُم بِأَحۡسَنِ مَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Abin da yake wurinku yana qarewa; abin da kuwa yake wurin Allah wanzajje ne. Lalle kuwa tabbas za Mu saka wa waxanda suka yi haquri ladansu da mafi kyan abin da suka kasance suna aikatawa



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 97

مَنۡ عَمِلَ صَٰلِحٗا مِّن ذَكَرٍ أَوۡ أُنثَىٰ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَلَنُحۡيِيَنَّهُۥ حَيَوٰةٗ طَيِّبَةٗۖ وَلَنَجۡزِيَنَّهُمۡ أَجۡرَهُم بِأَحۡسَنِ مَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Wanda ya yi kyakkyawan aiki namiji ko mace alhali shi yana mumini, to lalle za Mu raya shi rayuwa mai daxi, kuma za Mu saka musu ladansu da mafi kyan abin da suka kasance suna aikatawa



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 98

فَإِذَا قَرَأۡتَ ٱلۡقُرۡءَانَ فَٱسۡتَعِذۡ بِٱللَّهِ مِنَ ٱلشَّيۡطَٰنِ ٱلرَّجِيمِ

To idan za ka karanta Alqur’ani sai ka nemi tsarin Allah daga Shaixan korarre (daga rahamar Allah)



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 99

إِنَّهُۥ لَيۡسَ لَهُۥ سُلۡطَٰنٌ عَلَى ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَلَىٰ رَبِّهِمۡ يَتَوَكَّلُونَ

Lalle shi (Shaixan) ba shi da iko a kan waxanda suka yi imani kuma suke dogara da Ubangijinsu



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 100

إِنَّمَا سُلۡطَٰنُهُۥ عَلَى ٱلَّذِينَ يَتَوَلَّوۡنَهُۥ وَٱلَّذِينَ هُم بِهِۦ مُشۡرِكُونَ

Ikonsa kawai yana kan waxanda suke jivintar sa da kuma waxanda suke yin tarayya da shi



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 101

وَإِذَا بَدَّلۡنَآ ءَايَةٗ مَّكَانَ ءَايَةٖ وَٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا يُنَزِّلُ قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مُفۡتَرِۭۚ بَلۡ أَكۡثَرُهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Idan kuma Muka musanya wata aya a madadin wata ayar, alhali kuwa Allah ne Mafi sanin abin da Yake saukarwa, sai su ce: “Kai dai mai qirqirar qarya ne kawai!” A’a, ba haka ba ne, yawancinsu ba su san (komai) ba ne



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 102

قُلۡ نَزَّلَهُۥ رُوحُ ٱلۡقُدُسِ مِن رَّبِّكَ بِٱلۡحَقِّ لِيُثَبِّتَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَهُدٗى وَبُشۡرَىٰ لِلۡمُسۡلِمِينَ

Ka ce: “Ruhul Qudusi (watau Mala’ika Jibrilu) ne ya saukar da shi daga Ubangijinka da gaskiya don ya tabbatar da waxanda suka yi imani (a kan dugadugansu), kuma shiriya ne da albishir ga Musulmai.”



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 103

وَلَقَدۡ نَعۡلَمُ أَنَّهُمۡ يَقُولُونَ إِنَّمَا يُعَلِّمُهُۥ بَشَرٞۗ لِّسَانُ ٱلَّذِي يُلۡحِدُونَ إِلَيۡهِ أَعۡجَمِيّٞ وَهَٰذَا لِسَانٌ عَرَبِيّٞ مُّبِينٌ

Kuma haqiqa Mun san lalle suna cewa,: “Wani mutun ne kawai yake koya masa shi[1].” Harshen wanda suke karkata zuwa gare shi ajami ne, wannan kuwa harshe ne na Larabci bayyananne


1- Quraishawa suka riqa tuhumar Manzon Allah () yayin da suka gan shi yana magana da wani bawa matashi ba’ajame, suna cewa wai shi ne yake koya masa karatun Alqur’ani.


Surah: Suratun Nahl

Ayah : 104

إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ لَا يَهۡدِيهِمُ ٱللَّهُ وَلَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٌ

Lalle waxanda ba sa yin imani da ayoyin Allah, to Allah ba zai shirye su ba, kuma suna da azaba mai raxaxi



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 105

إِنَّمَا يَفۡتَرِي ٱلۡكَذِبَ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَٰذِبُونَ

Waxanda ba sa yin imani da ayoyin Allah su ne kawai suke qirqirar qarya; kuma waxannan su ne maqaryata



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 106

مَن كَفَرَ بِٱللَّهِ مِنۢ بَعۡدِ إِيمَٰنِهِۦٓ إِلَّا مَنۡ أُكۡرِهَ وَقَلۡبُهُۥ مُطۡمَئِنُّۢ بِٱلۡإِيمَٰنِ وَلَٰكِن مَّن شَرَحَ بِٱلۡكُفۡرِ صَدۡرٗا فَعَلَيۡهِمۡ غَضَبٞ مِّنَ ٱللَّهِ وَلَهُمۡ عَذَابٌ عَظِيمٞ

Wanda ya kafirce wa Allah bayan imaninsa, sai dai wanda aka tilasta wa alhali kuwa zuciyarsa ta cika da imani, amma kuma wanda ya buxe wa kafirci qirjinsa, to (waxannan) fushin Allah ya tabbata a kansu kuma suna da azaba mai girma



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 107

ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمُ ٱسۡتَحَبُّواْ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا عَلَى ٱلۡأٓخِرَةِ وَأَنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Wannan kuwa (ya faru) saboda su sun fi son rayuwar duniya a kan ta lahira, kuma lalle Allah ba Ya shiryar da mutane kafirai



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 108

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ طَبَعَ ٱللَّهُ عَلَىٰ قُلُوبِهِمۡ وَسَمۡعِهِمۡ وَأَبۡصَٰرِهِمۡۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡغَٰفِلُونَ

Waxannan su ne waxanda Allah Ya doxe zukatansu da jinsu da ganinsu, kuma waxannan su ne gafalallu



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 109

لَا جَرَمَ أَنَّهُمۡ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Ba shakka lalle su a lahira su ne tavavvu



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 110

ثُمَّ إِنَّ رَبَّكَ لِلَّذِينَ هَاجَرُواْ مِنۢ بَعۡدِ مَا فُتِنُواْ ثُمَّ جَٰهَدُواْ وَصَبَرُوٓاْ إِنَّ رَبَّكَ مِنۢ بَعۡدِهَا لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Sannan lalle Ubangjinka (Mai gafara ne da jin qai) ga waxanda suka yi hijira bayan an fitine su, sannan suka yi jihadi suka kuma yi haquri, lalle Ubangijinka, bayansu (waxannan ayyuka) Mai gafara ne, Mai jin qai



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 111

۞يَوۡمَ تَأۡتِي كُلُّ نَفۡسٖ تُجَٰدِلُ عَن نَّفۡسِهَا وَتُوَفَّىٰ كُلُّ نَفۡسٖ مَّا عَمِلَتۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Ranar da kowanne rai zai zo yana kare kansa, kuma a cika wa kowanne rai (sakamakon) abin da ya aikata, kuma su ba za a zalunce su ba



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 112

وَضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا قَرۡيَةٗ كَانَتۡ ءَامِنَةٗ مُّطۡمَئِنَّةٗ يَأۡتِيهَا رِزۡقُهَا رَغَدٗا مِّن كُلِّ مَكَانٖ فَكَفَرَتۡ بِأَنۡعُمِ ٱللَّهِ فَأَذَٰقَهَا ٱللَّهُ لِبَاسَ ٱلۡجُوعِ وَٱلۡخَوۡفِ بِمَا كَانُواْ يَصۡنَعُونَ

Allah kuma Ya ba da misali da wata alqarya[1] wadda ta kasance cikin aminci da kwanciyar hankali, arzikinta yana zo mata a yalwace ta kowanne wuri, sai ta kafirce wa ni’imomin Allah, to sai Allah Ya xanxana mata masifar yunwa da tsoro saboda abin da suka kasance suna aikatawa


1- Watau garin Makka.


Surah: Suratun Nahl

Ayah : 113

وَلَقَدۡ جَآءَهُمۡ رَسُولٞ مِّنۡهُمۡ فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمُ ٱلۡعَذَابُ وَهُمۡ ظَٰلِمُونَ

Haqiqa kuma Manzo ya zo musu daga cikinsu, sai suka qaryata shi, to sai azaba ta afka musu alhali suna azzalumai



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 114

فَكُلُواْ مِمَّا رَزَقَكُمُ ٱللَّهُ حَلَٰلٗا طَيِّبٗا وَٱشۡكُرُواْ نِعۡمَتَ ٱللَّهِ إِن كُنتُمۡ إِيَّاهُ تَعۡبُدُونَ

To ku ci halal mai daxi daga abin da Allah Ya arzuta ku da shi, kuma ku gode ni’imomin Allah in kun kasance Shi kaxai kuke bauta wa



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 115

إِنَّمَا حَرَّمَ عَلَيۡكُمُ ٱلۡمَيۡتَةَ وَٱلدَّمَ وَلَحۡمَ ٱلۡخِنزِيرِ وَمَآ أُهِلَّ لِغَيۡرِ ٱللَّهِ بِهِۦۖ فَمَنِ ٱضۡطُرَّ غَيۡرَ بَاغٖ وَلَا عَادٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Abin da kawai Ya haramta muku (shi ne) mushe da jini (mai kwarara) da naman alade da kuma abin da aka yanka da (sunan) wanin Allah; amma wanda ya matsu (ya ci) ba yana mai zalunci ko qetare iyaka ba, to lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 116

وَلَا تَقُولُواْ لِمَا تَصِفُ أَلۡسِنَتُكُمُ ٱلۡكَذِبَ هَٰذَا حَلَٰلٞ وَهَٰذَا حَرَامٞ لِّتَفۡتَرُواْ عَلَى ٱللَّهِ ٱلۡكَذِبَۚ إِنَّ ٱلَّذِينَ يَفۡتَرُونَ عَلَى ٱللَّهِ ٱلۡكَذِبَ لَا يُفۡلِحُونَ

Kuma saboda abin da harsunanku suke bayyanawa na qarya kada ku riqa cewa, wannan halal ne, wannan kuma haram ne, don ku yi wa Allah qarya. Lalle waxanda suke qirqira wa Allah qarya ba sa rabauta



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 117

مَتَٰعٞ قَلِيلٞ وَلَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

(Wannan) jin daxi ne qanqani (a duniya), kuma suna da azaba mai raxaxi



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 118

وَعَلَى ٱلَّذِينَ هَادُواْ حَرَّمۡنَا مَا قَصَصۡنَا عَلَيۡكَ مِن قَبۡلُۖ وَمَا ظَلَمۡنَٰهُمۡ وَلَٰكِن كَانُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Kuma Mun haramta wa Yahudawa abin da Muka labarta maka tun tuni[1]; ba Mu kuwa zalunce su ba, sai dai kuma kansu suka zalunta


1- Shi ne abin da ya zo a ciki Suratul An’am, aya ta 146.


Surah: Suratun Nahl

Ayah : 119

ثُمَّ إِنَّ رَبَّكَ لِلَّذِينَ عَمِلُواْ ٱلسُّوٓءَ بِجَهَٰلَةٖ ثُمَّ تَابُواْ مِنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ وَأَصۡلَحُوٓاْ إِنَّ رَبَّكَ مِنۢ بَعۡدِهَا لَغَفُورٞ رَّحِيمٌ

Sannan lalle Ubangijinka (Mai gafara ne) ga waxanda suka aikata mummuna a cikin jahilci sannan suka tuba bayan haka suka kuma gyara, lalle Ubagijinka Mai gafara ne, Mai jin qai



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 120

إِنَّ إِبۡرَٰهِيمَ كَانَ أُمَّةٗ قَانِتٗا لِّلَّهِ حَنِيفٗا وَلَمۡ يَكُ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

Lalle Ibrahimu ya zama abin koyi ne mai biyayya ga Allah mai kauce wa varna, bai kuma zamanto daga masu shirka ba