Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 61

عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ أَمۡثَٰلَكُمۡ وَنُنشِئَكُمۡ فِي مَا لَا تَعۡلَمُونَ

A kan Mu musanya irinku Mu kuma halitta ku cikin abin da ba ku sani ba



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 62

وَلَقَدۡ عَلِمۡتُمُ ٱلنَّشۡأَةَ ٱلۡأُولَىٰ فَلَوۡلَا تَذَكَّرُونَ

Haqiqa kuma ku kun san halitta ta farko, don me ba kwa wa’azantuwa?



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 63

أَفَرَءَيۡتُم مَّا تَحۡرُثُونَ

Ku ba Ni labarin abin da kuke nomawa?



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 64

ءَأَنتُمۡ تَزۡرَعُونَهُۥٓ أَمۡ نَحۡنُ ٱلزَّـٰرِعُونَ

Shin ku ne kuke tsiro da shi, ko Mu ne Masu tsirarwar?



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 65

لَوۡ نَشَآءُ لَجَعَلۡنَٰهُ حُطَٰمٗا فَظَلۡتُمۡ تَفَكَّهُونَ

Idan da Mun ga dama tabbas da Mun mayar da shi karmami, sai ku wayi gari kuna mamaki



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 66

إِنَّا لَمُغۡرَمُونَ

(Kuna cewa): “Lalle mu an xora mana asara.”



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 67

بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ

“A’a, mu dai an hana mu ne.”



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 68

أَفَرَءَيۡتُمُ ٱلۡمَآءَ ٱلَّذِي تَشۡرَبُونَ

Ku ba Ni labarin ruwa wanda kuke sha



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 69

ءَأَنتُمۡ أَنزَلۡتُمُوهُ مِنَ ٱلۡمُزۡنِ أَمۡ نَحۡنُ ٱلۡمُنزِلُونَ

Yanzu ku ne kuke sauko da shi daga girgije, ko kuwa Mu ne masu saukarwar?



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 70

لَوۡ نَشَآءُ جَعَلۡنَٰهُ أُجَاجٗا فَلَوۡلَا تَشۡكُرُونَ

Da Mun ga dama da Mun mayar da shi (ruwa) mai zartsi, to don me ba kwa godewa?



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 71

أَفَرَءَيۡتُمُ ٱلنَّارَ ٱلَّتِي تُورُونَ

Ku ba Ni labarin wutar da kuke kunnawa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 72

ءَأَنتُمۡ أَنشَأۡتُمۡ شَجَرَتَهَآ أَمۡ نَحۡنُ ٱلۡمُنشِـُٔونَ

Yanzu ku ne kuka halicci bishiyarta, ko kuwa Mu ne Masu halittar?



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 73

نَحۡنُ جَعَلۡنَٰهَا تَذۡكِرَةٗ وَمَتَٰعٗا لِّلۡمُقۡوِينَ

Mu ne Muka sanya ta wa’azi da kuma abin amfani ga matafiya



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 74

فَسَبِّحۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلۡعَظِيمِ

Saboda haka sai ka tsarkake Sunan Ubangijinka Mai girma



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 75

۞فَلَآ أُقۡسِمُ بِمَوَٰقِعِ ٱلنُّجُومِ

To ina yin rantsuwa da mafaxar taurari



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 76

وَإِنَّهُۥ لَقَسَمٞ لَّوۡ تَعۡلَمُونَ عَظِيمٌ

Lalle ita kuwa rantsuwa ce mai girma, da kuna ganewa.[1]


1- Domin taurari da tafiyarsu a sararin sama abu ne mai cike da ayoyi da darussa masu ximbin yawa.


Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 77

إِنَّهُۥ لَقُرۡءَانٞ كَرِيمٞ

Lalle shi Alqur’ani ne mai girma



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 78

فِي كِتَٰبٖ مَّكۡنُونٖ

A cikin littafi abin kiyayewa (daga wani sauyi).[1]


1- Shi ne Lauhul Mahfuz.


Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 79

لَّا يَمَسُّهُۥٓ إِلَّا ٱلۡمُطَهَّرُونَ

Babu mai tava shi sai tsarkakakku



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 80

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Saukakke ne daga Ubangijin talikai



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 81

أَفَبِهَٰذَا ٱلۡحَدِيثِ أَنتُم مُّدۡهِنُونَ

Yanzu wannan zance kuke qaryatawa?



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 82

وَتَجۡعَلُونَ رِزۡقَكُمۡ أَنَّكُمۡ تُكَذِّبُونَ

Kuke kuma sanya (godiyar) arzikinku shi ne ku riqa qaryatawa?



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 83

فَلَوۡلَآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلۡحُلۡقُومَ

Me ya hana idan (rai) ya isa maqogwaro



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 84

وَأَنتُمۡ حِينَئِذٖ تَنظُرُونَ

Ku kuma a lokacin kuna kallo



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 85

وَنَحۡنُ أَقۡرَبُ إِلَيۡهِ مِنكُمۡ وَلَٰكِن لَّا تُبۡصِرُونَ

Mu ne kuwa Muka fi ku kusanci da shi, sai dai kuma ba kwa gani



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 86

فَلَوۡلَآ إِن كُنتُمۡ غَيۡرَ مَدِينِينَ

Me ya hana idan da kun zamanto ba waxanda za a tasa ba ne



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 87

تَرۡجِعُونَهَآ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Ku dawo da shi (ran) mana idan kun kasance masu gaskiya



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 88

فَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلۡمُقَرَّبِينَ

Amma kuma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 89

فَرَوۡحٞ وَرَيۡحَانٞ وَجَنَّتُ نَعِيمٖ

To (sakamakonsa) hutu ne da arziki mai daxi, da kuma Aljannar ni’ima



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 90

وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنۡ أَصۡحَٰبِ ٱلۡيَمِينِ

Idan kuma ya kasance daga ma’abota hannun dama ne