Surah: Suratus Saffat

Ayah : 61

لِمِثۡلِ هَٰذَا فَلۡيَعۡمَلِ ٱلۡعَٰمِلُونَ

Don samun irin wannan lalle masu (kyakkyawan) aiki su yi aiki



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 62

أَذَٰلِكَ خَيۡرٞ نُّزُلًا أَمۡ شَجَرَةُ ٱلزَّقُّومِ

Shin wannan liyafa ita ce ta fi alheri ko kuwa bishiyar Zaqqum?



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 63

إِنَّا جَعَلۡنَٰهَا فِتۡنَةٗ لِّلظَّـٰلِمِينَ

Lalle Mu Mun sanya ta don ta zama fitina ga azzalumai



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 64

إِنَّهَا شَجَرَةٞ تَخۡرُجُ فِيٓ أَصۡلِ ٱلۡجَحِيمِ

Lalle ita wata bishiya ce da take fitowa a tsakiyar wutar Jahima



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 65

طَلۡعُهَا كَأَنَّهُۥ رُءُوسُ ٱلشَّيَٰطِينِ

‘Ya’yanta kai ka ce kawunan shaixanu ne



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 66

فَإِنَّهُمۡ لَأٓكِلُونَ مِنۡهَا فَمَالِـُٔونَ مِنۡهَا ٱلۡبُطُونَ

To su lalle za su ci daga gare ta, za su kuma cika cikkuna da ita



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 67

ثُمَّ إِنَّ لَهُمۡ عَلَيۡهَا لَشَوۡبٗا مِّنۡ حَمِيمٖ

Sannan kuma suna da wani gauraye na tafasasshen ruwa a kanta



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 68

ثُمَّ إِنَّ مَرۡجِعَهُمۡ لَإِلَى ٱلۡجَحِيمِ

Sannan kuma lalle makomarsu wutar Jahima ce



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 69

إِنَّهُمۡ أَلۡفَوۡاْ ءَابَآءَهُمۡ ضَآلِّينَ

Lalle su sun sami iyayensu vatattu



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 70

فَهُمۡ عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِمۡ يُهۡرَعُونَ

Sai suka riqa gaggawar bin sawunsu



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 71

وَلَقَدۡ ضَلَّ قَبۡلَهُمۡ أَكۡثَرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Haqiqa kafin su mafi yawan mutanen farko sun vata



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 72

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ

Kuma haqiqa Mun aiko masu gargaxi a cikinsu



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 73

فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُنذَرِينَ

To ka dubi yadda qarshen waxanda aka yi wa gargaxi ya kasance



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 74

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Sai dai bayin Allah waxanda aka tsarkake



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 75

وَلَقَدۡ نَادَىٰنَا نُوحٞ فَلَنِعۡمَ ٱلۡمُجِيبُونَ

Kuma haqiqa Nuhu ya roqe Mu, to madalla da Masu amsawa



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 76

وَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ

Muka kuma tserar da shi tare da iyalinsa daga baqin ciki mai girma



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 77

وَجَعَلۡنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلۡبَاقِينَ

Muka kuma sanya zuriyarsa su ne suka wanzu



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 78

وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

Muka kuma bar (kyakkyawan yabo) a gare shi ga ‘yan baya



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 79

سَلَٰمٌ عَلَىٰ نُوحٖ فِي ٱلۡعَٰلَمِينَ

Aminci ya tabbata ga Nuhu a cikin talikai



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 80

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 81

إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle shi yana daga bayinmu muminai



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 82

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka nutsar da sauran



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 83

۞وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِۦ لَإِبۡرَٰهِيمَ

Lalle kuma Ibrahimu yana daga mabiya addininsa



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 84

إِذۡ جَآءَ رَبَّهُۥ بِقَلۡبٖ سَلِيمٍ

A yayin da ya zo wa Ubangijinsa da lafiyayyar zuciya



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 85

إِذۡ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦ مَاذَا تَعۡبُدُونَ

Lokacin da ya ce da babansa da kuma mutanensa: “Me kuke bauta wa ne?



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 86

أَئِفۡكًا ءَالِهَةٗ دُونَ ٱللَّهِ تُرِيدُونَ

“Yanzu iyayen giji na qarya ba Allah ba kuke nufi?



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 87

فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“To mene ne tsammaninku game da Ubangijin talikai?”



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 88

فَنَظَرَ نَظۡرَةٗ فِي ٱلنُّجُومِ

Sai ya yi duba a cikin taurari, duba na tunani



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 89

فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٞ

Sannan ya ce: “Lalle ni fa ba ni da lafiya.”



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 90

فَتَوَلَّوۡاْ عَنۡهُ مُدۡبِرِينَ

Sai suka juya daga wurinsa suna masu ba da baya