Surah: Suratun Najm

Ayah : 31

وَلِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ لِيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ أَسَـٰٓـُٔواْ بِمَا عَمِلُواْ وَيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ أَحۡسَنُواْ بِٱلۡحُسۡنَى

Kuma abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa na Allah ne, don Ya saka wa waxanda suka munana da irin abin da suka aikata, Ya kuma saka wa waxanda suka kyautata da mafi kyan sakamako



Surah: Suratun Najm

Ayah : 32

ٱلَّذِينَ يَجۡتَنِبُونَ كَبَـٰٓئِرَ ٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡفَوَٰحِشَ إِلَّا ٱللَّمَمَۚ إِنَّ رَبَّكَ وَٰسِعُ ٱلۡمَغۡفِرَةِۚ هُوَ أَعۡلَمُ بِكُمۡ إِذۡ أَنشَأَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ وَإِذۡ أَنتُمۡ أَجِنَّةٞ فِي بُطُونِ أُمَّهَٰتِكُمۡۖ فَلَا تُزَكُّوٓاْ أَنفُسَكُمۡۖ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَنِ ٱتَّقَىٰٓ

(Su ne) waxanda suke nisantar manya-manyan zunubai da munanan ayyukan savo, sai dai ‘yan qananan zunubai. Lalle Ubangijinka Mayalwacin gafara ne. Shi ne Ya fi sanin ku, tun sanda Ya halicce ku daga qasa, sai ga ku kun zama ‘yan tayi a cikin cikin iyayenku mata; to kada ku tsarkake kanku; Shi ne Ya fi sanin wanda ya fi taqawa



Surah: Suratun Najm

Ayah : 33

أَفَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي تَوَلَّىٰ

Ka ba ni labarin wanda ya ba da baya



Surah: Suratun Najm

Ayah : 34

وَأَعۡطَىٰ قَلِيلٗا وَأَكۡدَىٰٓ

Ya kuma bayar da dukiya kaxan kuma ya yi rowa



Surah: Suratun Najm

Ayah : 35

أَعِندَهُۥ عِلۡمُ ٱلۡغَيۡبِ فَهُوَ يَرَىٰٓ

Shin yana da ilimin gaibu ne don haka yana ganin (komai)?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 36

أَمۡ لَمۡ يُنَبَّأۡ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىٰ

Ko ba a ba shi labarin abin da yake cikin takardun Musa ba ne?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 37

وَإِبۡرَٰهِيمَ ٱلَّذِي وَفَّىٰٓ

Da kuma Ibrahimu wanda ya cika alqawari?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 38

أَلَّا تَزِرُ وَازِرَةٞ وِزۡرَ أُخۡرَىٰ

Cewa: “Wani rai ba ya xaukar nauyin laifin wani



Surah: Suratun Najm

Ayah : 39

وَأَن لَّيۡسَ لِلۡإِنسَٰنِ إِلَّا مَا سَعَىٰ

“Kuma mutum bai mallaki wani sakamako ba sai na abin da ya aikata



Surah: Suratun Najm

Ayah : 40

وَأَنَّ سَعۡيَهُۥ سَوۡفَ يُرَىٰ

“Kuma lalle aikin nasa ba da daxewa ba za a gan shi



Surah: Suratun Najm

Ayah : 41

ثُمَّ يُجۡزَىٰهُ ٱلۡجَزَآءَ ٱلۡأَوۡفَىٰ

“Sannan a saka masa da cikakken sakamako



Surah: Suratun Najm

Ayah : 42

وَأَنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلۡمُنتَهَىٰ

“Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makoma



Surah: Suratun Najm

Ayah : 43

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَضۡحَكَ وَأَبۡكَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ya sa a yi dariya, kuma Ya sa a yi kuka



Surah: Suratun Najm

Ayah : 44

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَمَاتَ وَأَحۡيَا

“Kuma lalle Shi ne Ya kashe kuma Ya raya



Surah: Suratun Najm

Ayah : 45

وَأَنَّهُۥ خَلَقَ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ya halicci dangi biyu namiji da mace



Surah: Suratun Najm

Ayah : 46

مِن نُّطۡفَةٍ إِذَا تُمۡنَىٰ

“Daga maniyyi yayin da ake zuba shi



Surah: Suratun Najm

Ayah : 47

وَأَنَّ عَلَيۡهِ ٱلنَّشۡأَةَ ٱلۡأُخۡرَىٰ

“Kuma lalle Ya xora wa kansa sake tashin matattu



Surah: Suratun Najm

Ayah : 48

وَأَنَّهُۥ هُوَ أَغۡنَىٰ وَأَقۡنَىٰ

“Lalle kuma Shi ne Ya wadata, Ya kuma yalwata



Surah: Suratun Najm

Ayah : 49

وَأَنَّهُۥ هُوَ رَبُّ ٱلشِّعۡرَىٰ

“Kuma lalle Shi ne Ubangijin tauraron nan Shi’ira



Surah: Suratun Najm

Ayah : 50

وَأَنَّهُۥٓ أَهۡلَكَ عَادًا ٱلۡأُولَىٰ

“Lalle kuma Ya hallakar da Adawa na farko



Surah: Suratun Najm

Ayah : 51

وَثَمُودَاْ فَمَآ أَبۡقَىٰ

“Da kuma Samudawa, don haka bai bar saura ba



Surah: Suratun Najm

Ayah : 52

وَقَوۡمَ نُوحٖ مِّن قَبۡلُۖ إِنَّهُمۡ كَانُواْ هُمۡ أَظۡلَمَ وَأَطۡغَىٰ

“Da mutanen Nuhu tun kafin su; lalle su sun kasance su ne mafiya zalunci kuma mafiya xagawa



Surah: Suratun Najm

Ayah : 53

وَٱلۡمُؤۡتَفِكَةَ أَهۡوَىٰ

“Da waxanda aka kife (mutanen Luxu, Allah) ya qasqanta su



Surah: Suratun Najm

Ayah : 54

فَغَشَّىٰهَا مَا غَشَّىٰ

“Sannan abin da ya lulluve su (na azaba) ya lulluve su.”



Surah: Suratun Najm

Ayah : 55

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىٰ

To (kai xan’adam) da waxanne ni’imomin Ubangijinka kake jayayya?



Surah: Suratun Najm

Ayah : 56

هَٰذَا نَذِيرٞ مِّنَ ٱلنُّذُرِ ٱلۡأُولَىٰٓ

Wannan mai gargaxi ne daga irin masu gargaxin farko



Surah: Suratun Najm

Ayah : 57

أَزِفَتِ ٱلۡأٓزِفَةُ

Mai kusantowa ta kusanto (watau alqiyama)



Surah: Suratun Najm

Ayah : 58

لَيۡسَ لَهَا مِن دُونِ ٱللَّهِ كَاشِفَةٌ

Ba wani mai bayyana lokacinta in ban da Allah



Surah: Suratun Najm

Ayah : 59

أَفَمِنۡ هَٰذَا ٱلۡحَدِيثِ تَعۡجَبُونَ

Yanzu game da wannan zancen ne[1] kuke mamaki?


1- Watau Alqur’ani mai girma.


Surah: Suratun Najm

Ayah : 60

وَتَضۡحَكُونَ وَلَا تَبۡكُونَ

Kuke kuma dariya ba kwa yin kuka?