Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 31

۞قَالَ فَمَا خَطۡبُكُمۡ أَيُّهَا ٱلۡمُرۡسَلُونَ

(Ibrahimu) ya ce: “To me yake tafe da ku, ya ku waxannan manzanni?”



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 32

قَالُوٓاْ إِنَّآ أُرۡسِلۡنَآ إِلَىٰ قَوۡمٖ مُّجۡرِمِينَ

Suka ce: “Lalle mu an aiko mu ne zuwa ga wasu mutane masu manyan laifuka[1]


1- Su ne mutanen Annabi Lux () masu neman maza da sha’awa.


Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 33

لِنُرۡسِلَ عَلَيۡهِمۡ حِجَارَةٗ مِّن طِينٖ

“Don mu zuba musu qonannun duwatsu na tavon (wuta)



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 34

مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلۡمُسۡرِفِينَ

“Waxanda aka yi wa alama daga wurin Ubangijinka saboda mavarnata.”



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 35

فَأَخۡرَجۡنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Sai Muka tserar da duk wanda ya kasance a cikinta (alqaryar) daga muminai



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 36

فَمَا وَجَدۡنَا فِيهَا غَيۡرَ بَيۡتٖ مِّنَ ٱلۡمُسۡلِمِينَ

Sai ba mu sami wani (gida) a cikinta ba in ban da gida xaya na Musulmi[1]


1- Shi ne gidan Annabi Lux (), in ban da matarsa, ita ba ta yi imani ba.


Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 37

وَتَرَكۡنَا فِيهَآ ءَايَةٗ لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَلِيمَ

Muka kuma bar aya ta wa’azi a cikinta ga waxanda suke tsoron azaba mai raxaxi



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 38

وَفِي مُوسَىٰٓ إِذۡ أَرۡسَلۡنَٰهُ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٖ

Game da Musa kuma (akwai aya), lokacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir’auna da hujjoji bayyanannu



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 39

فَتَوَلَّىٰ بِرُكۡنِهِۦ وَقَالَ سَٰحِرٌ أَوۡ مَجۡنُونٞ

Sai ya ba da baya shi da qarfin rundunarsa, ya kuma ce: “(Musa) mai sihiri ne ko mahaukaci.”



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 40

فَأَخَذۡنَٰهُ وَجُنُودَهُۥ فَنَبَذۡنَٰهُمۡ فِي ٱلۡيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٞ

Saboda haka Muka kama shi tare da rundunarsa, sai Muka watsa su a cikin kogi, alhali yana mai aikata abin Allah-wadai



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 41

وَفِي عَادٍ إِذۡ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمُ ٱلرِّيحَ ٱلۡعَقِيمَ

Kuma game da Adawa (akwai aya), lokacin da Muka aiko musu da iska marar alhairi



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 42

مَا تَذَرُ مِن شَيۡءٍ أَتَتۡ عَلَيۡهِ إِلَّا جَعَلَتۡهُ كَٱلرَّمِيمِ

Ba ta barin wani abu idan ta biyo ta kansa sai ta mayar da shi kamar daddagagge qashi



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 43

وَفِي ثَمُودَ إِذۡ قِيلَ لَهُمۡ تَمَتَّعُواْ حَتَّىٰ حِينٖ

Kuma game da Samudawa (akwai aya), lokacin da aka ce da su: “Ku ji daxi zuwa wani xan lokaci[1].”


1- Watau wa’adin kwana uku kacal.


Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 44

فَعَتَوۡاْ عَنۡ أَمۡرِ رَبِّهِمۡ فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّـٰعِقَةُ وَهُمۡ يَنظُرُونَ

Sai suka yi tsaurin kai game da umarnin Ubangijinsu, saboda haka tsawa ta faxa musu alhali kuwa suna kallo



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 45

فَمَا ٱسۡتَطَٰعُواْ مِن قِيَامٖ وَمَا كَانُواْ مُنتَصِرِينَ

To ba su sami damar tsayuwa ba, kuma ba su zamanto masu taimaka wa (junansu) ba



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 46

وَقَوۡمَ نُوحٖ مِّن قَبۡلُۖ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمٗا فَٰسِقِينَ

Kuma (Mun hallakar da) mutanen Nuhu a gabaninsu; don kuwa lalle sun kasance mutane ne fasiqai



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 47

وَٱلسَّمَآءَ بَنَيۡنَٰهَا بِأَيۡيْدٖ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ

Sama kuma Mun gina ta da qarfi, lalle kuma Mu tabbas Masu yalwatawa ne



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 48

وَٱلۡأَرۡضَ فَرَشۡنَٰهَا فَنِعۡمَ ٱلۡمَٰهِدُونَ

Qasa kuma Muka shimfixa ta, to madalla da Masu shimfixar



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 49

وَمِن كُلِّ شَيۡءٍ خَلَقۡنَا زَوۡجَيۡنِ لَعَلَّكُمۡ تَذَكَّرُونَ

Daga kowane abu kuma Mun halicci nau’i biyu, don ku wa’azantu



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 50

فَفِرُّوٓاْ إِلَى ٱللَّهِۖ إِنِّي لَكُم مِّنۡهُ نَذِيرٞ مُّبِينٞ

To ku gudo zuwa ga Allah[1], lalle ni mai gargaxi ne game da Shi, mai bayyana (gargaxi)


1- Watau su guje wa azabarsa zuwa kyakkyawan sakamakonsa ta hanyar yi masa biyayya.


Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 51

وَلَا تَجۡعَلُواْ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَۖ إِنِّي لَكُم مِّنۡهُ نَذِيرٞ مُّبِينٞ

Kada kuma ku sanya wani abin bauta tare da Allah; lalle ni mai gargaxi ne game da Shi, mai bayyana (gargaxi)



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 52

كَذَٰلِكَ مَآ أَتَى ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُواْ سَاحِرٌ أَوۡ مَجۡنُونٌ

Kamar haka abin yake, ba waxanda wani manzo ya zo musu a gabaninsu (mutan Makka) sai sun ce mai sihiri ne ko mahaukaci



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 53

أَتَوَاصَوۡاْ بِهِۦۚ بَلۡ هُمۡ قَوۡمٞ طَاغُونَ

Shin wasiyya suke yi wa junansu ne game da shi? A’a, su dai mutane ne masu qetare iyaka



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 54

فَتَوَلَّ عَنۡهُمۡ فَمَآ أَنتَ بِمَلُومٖ

Sai ka rabu da su, don kuwa kai ba abin zargi ba ne



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 55

وَذَكِّرۡ فَإِنَّ ٱلذِّكۡرَىٰ تَنفَعُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Kuma ka yi wa’azi, don ko lalle wa’azi yana amfanar muminai



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 56

وَمَا خَلَقۡتُ ٱلۡجِنَّ وَٱلۡإِنسَ إِلَّا لِيَعۡبُدُونِ

Ban halicci aljanu da mutane ba sai don su bauta min



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 57

مَآ أُرِيدُ مِنۡهُم مِّن رِّزۡقٖ وَمَآ أُرِيدُ أَن يُطۡعِمُونِ

Ba Na neman wani arziki a wurinsu, kuma ba Na neman su ciyar da Ni



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 58

إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلرَّزَّاقُ ذُو ٱلۡقُوَّةِ ٱلۡمَتِينُ

Lalle Allah Shi ne Mai arzutawa, Mai tsananin qarfi



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 59

فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُواْ ذَنُوبٗا مِّثۡلَ ذَنُوبِ أَصۡحَٰبِهِمۡ فَلَا يَسۡتَعۡجِلُونِ

To lalle waxanda suka zalunci (kansu) suna da wani kaso na azaba kamar kason abokansu[1], saboda haka kada su nemi gaggauto shi


1- Watau kafiran farko.


Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 60

فَوَيۡلٞ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ مِن يَوۡمِهِمُ ٱلَّذِي يُوعَدُونَ

To tsananin azaba ya tabbata ga waxanda suka kafirta a ranar da ake alqawarta musu