Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 31

مِن فِرۡعَوۡنَۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَالِيٗا مِّنَ ٱلۡمُسۡرِفِينَ

Daga Fir’auna. Lalle shi ya kasance mai girman kai daga mavarnata



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 32

وَلَقَدِ ٱخۡتَرۡنَٰهُمۡ عَلَىٰ عِلۡمٍ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Kuma haqiqa Mun fifita su (Banu Isra’ila) bisa saninmu a kan (sauran) talikai



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 33

وَءَاتَيۡنَٰهُم مِّنَ ٱلۡأٓيَٰتِ مَا فِيهِ بَلَـٰٓؤٞاْ مُّبِينٌ

Muka kuma ba su wasu ayoyinmu waxanda a cikinsa akwai jarrabawa mabayyaniya



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 34

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَيَقُولُونَ

Lalle waxannan (kafiran Makka) tabbas suna cewa:



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 35

إِنۡ هِيَ إِلَّا مَوۡتَتُنَا ٱلۡأُولَىٰ وَمَا نَحۡنُ بِمُنشَرِينَ

“Babu wata mutuwa da za mu yi sai mutuwarmu ta farko, kuma mu ba za a tashe mu ba



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 36

فَأۡتُواْ بِـَٔابَآئِنَآ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

“To ku zo mana da iyayenmu idan kun kasance masu gaskiya.”



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 37

أَهُمۡ خَيۡرٌ أَمۡ قَوۡمُ تُبَّعٖ وَٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ أَهۡلَكۡنَٰهُمۡۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ مُجۡرِمِينَ

Yanzu su ne suka fi ko kuwa mutanen Tubba’u[1] da waxanda suke a gabaninsu? Duk Mun hallakar da su. Lalle sun kasance masu manyan laifuka


1- Mutanen Makka sun yarda cewa qabilun Larabawan Himyar da Saba’u waxanda ake kira mutanen Tubba’u na qasar Yaman sun fi su qarfin Mulki da jin daxin duniya.


Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 38

وَمَا خَلَقۡنَا ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَا لَٰعِبِينَ

Ba Mu kuma halicci sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu don wasa ba



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 39

مَا خَلَقۡنَٰهُمَآ إِلَّا بِٱلۡحَقِّ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Ba Mu halicce su ba sai don gaskiya, sai dai kuma yawancinsu ba su san haka ba



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 40

إِنَّ يَوۡمَ ٱلۡفَصۡلِ مِيقَٰتُهُمۡ أَجۡمَعِينَ

Lalle ranar alqiyama ne lokacin da aka qayyade musu gaba xaya



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 41

يَوۡمَ لَا يُغۡنِي مَوۡلًى عَن مَّوۡلٗى شَيۡـٔٗا وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ

Ranar da wani masoyi ba zai amfana wa masoyinsa komai ba, su kuma ba za a taimaka musu ba



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 42

إِلَّا مَن رَّحِمَ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Sai fa wanda Allah Ya ji qan sa. Lalle Shi ne Mabuwayi, Mai rahama



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 43

إِنَّ شَجَرَتَ ٱلزَّقُّومِ

Lalle itaciyar Zaqqumu



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 44

طَعَامُ ٱلۡأَثِيمِ

Abincin mai babban zunubi ce



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 45

كَٱلۡمُهۡلِ يَغۡلِي فِي ٱلۡبُطُونِ

(Kuma) kamar narkakkiyar darma, tana tafarfasa a cikin ciki



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 46

كَغَلۡيِ ٱلۡحَمِيمِ

Kamar tafasar ruwan zafi



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 47

خُذُوهُ فَٱعۡتِلُوهُ إِلَىٰ سَوَآءِ ٱلۡجَحِيمِ

(Za a ce da mala’iku): “Ku kama shi sannan ku ja shi tsakiyar wutar Jahima



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 48

ثُمَّ صُبُّواْ فَوۡقَ رَأۡسِهِۦ مِنۡ عَذَابِ ٱلۡحَمِيمِ

“Sannan ku kwarara azabar ruwan zafi a tsakiyar kansa.”



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 49

ذُقۡ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡكَرِيمُ

(Sai a ce da shi): “Xanxana, lalle kai xin nan kai babban mutum ne mai daraja[1]


1- Watau kamar yadda yake xaukar kansa a duniya. Ana faxa masa haka cikin izgili da ba’a.


Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 50

إِنَّ هَٰذَا مَا كُنتُم بِهِۦ تَمۡتَرُونَ

(Za a ce da kafirai): “Lalle wannan ne abin da kuka kasance kuna shakkar sa.”



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 51

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي مَقَامٍ أَمِينٖ

Lalle masu taqawa suna cikin wani amintaccen wuri



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 52

فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

Cikin lambuna da idanuwan ruwa



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 53

يَلۡبَسُونَ مِن سُندُسٖ وَإِسۡتَبۡرَقٖ مُّتَقَٰبِلِينَ

Suna saye da tufafi na alharini mai shara-shara da mai kauri suna fuskantar juna



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 54

كَذَٰلِكَ وَزَوَّجۡنَٰهُم بِحُورٍ عِينٖ

Kamar haka ne, Muka kuma aura musu (‘yan matan) Hurul-Ini



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 55

يَدۡعُونَ فِيهَا بِكُلِّ فَٰكِهَةٍ ءَامِنِينَ

A cikinta (Aljannar) suna kiran a kawo musu duk wani kayan marmari, suna cikin aminci



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 56

لَا يَذُوقُونَ فِيهَا ٱلۡمَوۡتَ إِلَّا ٱلۡمَوۡتَةَ ٱلۡأُولَىٰۖ وَوَقَىٰهُمۡ عَذَابَ ٱلۡجَحِيمِ

Ba za su xanxani wata mutuwa a cikinta ba sai dai mutuwar farko; Ya kuma tserar da su daga azabar wutar Jahima



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 57

فَضۡلٗا مِّن رَّبِّكَۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

(Wannan) falala ce daga Ubangijinka. Wannan shi ne babban rabo



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 58

فَإِنَّمَا يَسَّرۡنَٰهُ بِلِسَانِكَ لَعَلَّهُمۡ يَتَذَكَّرُونَ

To kawai Mun sauqaqe shi ne (wato Alqur’ani) da harshenka, don su wa’azantu



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 59

فَٱرۡتَقِبۡ إِنَّهُم مُّرۡتَقِبُونَ

To ka saurara, lalle su ma masu sauraro ne