Surah: Suratus Shura

Ayah : 31

وَمَآ أَنتُم بِمُعۡجِزِينَ فِي ٱلۡأَرۡضِۖ وَمَا لَكُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ مِن وَلِيّٖ وَلَا نَصِيرٖ

Kuma ku ba za ku gagara ba a bayan qasa; kuma ba ku da wani majivinci ko mataimaki in ba Allah ba



Surah: Suratus Shura

Ayah : 32

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِ ٱلۡجَوَارِ فِي ٱلۡبَحۡرِ كَٱلۡأَعۡلَٰمِ

Daga cikin ayoyinsa kuma akwai jiragen ruwa masu gudu a cikin kogi kamar duwatsu



Surah: Suratus Shura

Ayah : 33

إِن يَشَأۡ يُسۡكِنِ ٱلرِّيحَ فَيَظۡلَلۡنَ رَوَاكِدَ عَلَىٰ ظَهۡرِهِۦٓۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّكُلِّ صَبَّارٖ شَكُورٍ

Idan da Ya ga dama da sai Ya kwantar da iska sai (jiragen) su zama a tsaye cak a kan (kogin). Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga duk wani mai yawan haquri, mai yawan godiya



Surah: Suratus Shura

Ayah : 34

أَوۡ يُوبِقۡهُنَّ بِمَا كَسَبُواْ وَيَعۡفُ عَن كَثِيرٖ

Ko kuma Ya nutsar da su saboda (munanan ayyukan) da suka aikata. Ko kuma ya yi afuwa ga wasu (laifuka) masu yawa



Surah: Suratus Shura

Ayah : 35

وَيَعۡلَمَ ٱلَّذِينَ يُجَٰدِلُونَ فِيٓ ءَايَٰتِنَا مَا لَهُم مِّن مَّحِيصٖ

Kuma waxanda suke jayayya game da ayoyinmu sun san da cewa ba su da wata matsera



Surah: Suratus Shura

Ayah : 36

فَمَآ أُوتِيتُم مِّن شَيۡءٖ فَمَتَٰعُ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۚ وَمَا عِندَ ٱللَّهِ خَيۡرٞ وَأَبۡقَىٰ لِلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَلَىٰ رَبِّهِمۡ يَتَوَكَّلُونَ

Sannan duk wani abu da aka ba ku to jin daxin rayuwar duniya ne; kuma abin da yake wurin Allah shi ya fi alheri ya kuma fi wanzuwa ga waxanda suka yi imani suke kuma dogara ga Ubangijinsu



Surah: Suratus Shura

Ayah : 37

وَٱلَّذِينَ يَجۡتَنِبُونَ كَبَـٰٓئِرَ ٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡفَوَٰحِشَ وَإِذَا مَا غَضِبُواْ هُمۡ يَغۡفِرُونَ

Waxanda kuma suke nesantar manyan zunubai da munanansu, idan kuma sun yi fushi sukan yafe



Surah: Suratus Shura

Ayah : 38

وَٱلَّذِينَ ٱسۡتَجَابُواْ لِرَبِّهِمۡ وَأَقَامُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَأَمۡرُهُمۡ شُورَىٰ بَيۡنَهُمۡ وَمِمَّا رَزَقۡنَٰهُمۡ يُنفِقُونَ

(Su ne) kuma waxanda suka amsa kiran Ubangijinsu suka kuma tsai da salla, al’amarinsu kuwa (suna) shawara ne a tsakaninsu, suna kuma ciyarwa daga abin da Muka arzuta su



Surah: Suratus Shura

Ayah : 39

وَٱلَّذِينَ إِذَآ أَصَابَهُمُ ٱلۡبَغۡيُ هُمۡ يَنتَصِرُونَ

(Su ne) kuma waxanda idan wani zalunci ya shafe su sukan rama[1]


1- Yayin da azzalumin ya kasance ba wanda ya cancanci afuwa ba ne, kuma babu maslaha cikin yi masa afuwar.


Surah: Suratus Shura

Ayah : 40

وَجَزَـٰٓؤُاْ سَيِّئَةٖ سَيِّئَةٞ مِّثۡلُهَاۖ فَمَنۡ عَفَا وَأَصۡلَحَ فَأَجۡرُهُۥ عَلَى ٱللَّهِۚ إِنَّهُۥ لَا يُحِبُّ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma sakamakon mummunan (abu) shi ne mayar da mummuna kamarsa; to wanda ya yi afuwa ya kuma kyautata, to ladansa yana wurin Allah. Lalle Shi ba Ya son azzalumai



Surah: Suratus Shura

Ayah : 41

وَلَمَنِ ٱنتَصَرَ بَعۡدَ ظُلۡمِهِۦ فَأُوْلَـٰٓئِكَ مَا عَلَيۡهِم مِّن سَبِيلٍ

Tabbas kuma duk wanda ya rama bayan an zalunce shi, to waxannan ba wani laifi a kansu



Surah: Suratus Shura

Ayah : 42

إِنَّمَا ٱلسَّبِيلُ عَلَى ٱلَّذِينَ يَظۡلِمُونَ ٱلنَّاسَ وَيَبۡغُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ بِغَيۡرِ ٱلۡحَقِّۚ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Laifi kam yana kan waxanda suke zaluntar mutane ne suke kuma yin ta’adda a bayan qasa ba da wata hujja ba. Waxannan suna da azaba mai raxaxi



Surah: Suratus Shura

Ayah : 43

وَلَمَن صَبَرَ وَغَفَرَ إِنَّ ذَٰلِكَ لَمِنۡ عَزۡمِ ٱلۡأُمُورِ

Tabbas kuma wanda ya yi haquri ya yafe, to tabbas wannan yana daga muhimman al’amura[1]


1- Watau haqurinsa zai zame masa alheri, har ma da al’ummarsa gaba xaya.


Surah: Suratus Shura

Ayah : 44

وَمَن يُضۡلِلِ ٱللَّهُ فَمَا لَهُۥ مِن وَلِيّٖ مِّنۢ بَعۡدِهِۦۗ وَتَرَى ٱلظَّـٰلِمِينَ لَمَّا رَأَوُاْ ٱلۡعَذَابَ يَقُولُونَ هَلۡ إِلَىٰ مَرَدّٖ مِّن سَبِيلٖ

Wanda kuma Allah Ya vatar, to ba shi da wani majivinci bayanSa. Kuma za ka ga azzalumai lokacin da suka ga azabar suna cewa: “Ina ma da akwai wata damar komawa (duniya)?”



Surah: Suratus Shura

Ayah : 45

وَتَرَىٰهُمۡ يُعۡرَضُونَ عَلَيۡهَا خَٰشِعِينَ مِنَ ٱلذُّلِّ يَنظُرُونَ مِن طَرۡفٍ خَفِيّٖۗ وَقَالَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِنَّ ٱلۡخَٰسِرِينَ ٱلَّذِينَ خَسِرُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ وَأَهۡلِيهِمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۗ أَلَآ إِنَّ ٱلظَّـٰلِمِينَ فِي عَذَابٖ مُّقِيمٖ

Kuma za ka gan su ana bijiro su a kanta (wutar) suna masu qanqan da kai na wulaqanci, suna kallo a sace. Waxanda kuma suka yi imani suka ce: “Lalle asararru su ne waxanda suka yi asarar rayuwarsu da ta iyalinsu a ranar alqiyama.” Ku saurara, lalle azzalumai suna cikin azaba dawwamammiya



Surah: Suratus Shura

Ayah : 46

وَمَا كَانَ لَهُم مِّنۡ أَوۡلِيَآءَ يَنصُرُونَهُم مِّن دُونِ ٱللَّهِۗ وَمَن يُضۡلِلِ ٱللَّهُ فَمَا لَهُۥ مِن سَبِيلٍ

Kuma ba su da wasu majivinta da za su taimake su in ban da Allah. Duk wanda Allah Ya vatar, to ba shi da wata hanya daban (ta shiriya)



Surah: Suratus Shura

Ayah : 47

ٱسۡتَجِيبُواْ لِرَبِّكُم مِّن قَبۡلِ أَن يَأۡتِيَ يَوۡمٞ لَّا مَرَدَّ لَهُۥ مِنَ ٱللَّهِۚ مَا لَكُم مِّن مَّلۡجَإٖ يَوۡمَئِذٖ وَمَا لَكُم مِّن نَّكِيرٖ

Ku amsa kiran Ubangijinku tun kafin ranar da ba ta da wata makauta[1] ta zo daga Allah. Ba ku da wata mafaka a wannan ranar, kuma ba ku da damar yin musu[2]


1- Watau babu wanda ya isa ya hana zuwanta.


2- Watau ba su da damar musunta zunuban da suka aikata a duniya.


Surah: Suratus Shura

Ayah : 48

فَإِنۡ أَعۡرَضُواْ فَمَآ أَرۡسَلۡنَٰكَ عَلَيۡهِمۡ حَفِيظًاۖ إِنۡ عَلَيۡكَ إِلَّا ٱلۡبَلَٰغُۗ وَإِنَّآ إِذَآ أَذَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ مِنَّا رَحۡمَةٗ فَرِحَ بِهَاۖ وَإِن تُصِبۡهُمۡ سَيِّئَةُۢ بِمَا قَدَّمَتۡ أَيۡدِيهِمۡ فَإِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ كَفُورٞ

To idan sun bijire, to ba Mu aika ka don ka zama mai gadin su ba; ba abin da yake kanka sai isar da saqo. Lalle kuma Mu idan Muka xanxana wa mutum wata rahama daga gare Mu sai ya riqa tutiya da ita. Idan kuma wani mummunan abu ya same su saboda abin da hannayensu suka aikata, to lalle shi mutum butulu ne



Surah: Suratus Shura

Ayah : 49

لِّلَّهِ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ يَخۡلُقُ مَا يَشَآءُۚ يَهَبُ لِمَن يَشَآءُ إِنَٰثٗا وَيَهَبُ لِمَن يَشَآءُ ٱلذُّكُورَ

Mulkin sammai da qasa na Allah ne. Yana halittar abin da Ya ga dama. Yana ba da `ya`ya mata ga wanda Ya ga dama, Yana kuma ba da `ya`ya maza ga wanda Ya ga dama



Surah: Suratus Shura

Ayah : 50

أَوۡ يُزَوِّجُهُمۡ ذُكۡرَانٗا وَإِنَٰثٗاۖ وَيَجۡعَلُ مَن يَشَآءُ عَقِيمًاۚ إِنَّهُۥ عَلِيمٞ قَدِيرٞ

Ko kuma ya haxa musu maza da mata; Yakan kuma mayar da wanda ya ga dama bakarare. Lalle Shi Masani ne, Mai iko



Surah: Suratus Shura

Ayah : 51

۞وَمَا كَانَ لِبَشَرٍ أَن يُكَلِّمَهُ ٱللَّهُ إِلَّا وَحۡيًا أَوۡ مِن وَرَآيِٕ حِجَابٍ أَوۡ يُرۡسِلَ رَسُولٗا فَيُوحِيَ بِإِذۡنِهِۦ مَا يَشَآءُۚ إِنَّهُۥ عَلِيٌّ حَكِيمٞ

Kuma zai yiwu ga wani mutum a ce Allah Ya yi magana da shi ba (baki da baki), sai dai wahayi ko kuma ta bayan wani shamaki, ko kuwa Ya aiko wani manzo (mala’ika) sai ya yi masa wahayin abin da ya ga dama da yardarsa. Lalle Shi Maxaukaki ne, Mai hikima



Surah: Suratus Shura

Ayah : 52

وَكَذَٰلِكَ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ رُوحٗا مِّنۡ أَمۡرِنَاۚ مَا كُنتَ تَدۡرِي مَا ٱلۡكِتَٰبُ وَلَا ٱلۡإِيمَٰنُ وَلَٰكِن جَعَلۡنَٰهُ نُورٗا نَّهۡدِي بِهِۦ مَن نَّشَآءُ مِنۡ عِبَادِنَاۚ وَإِنَّكَ لَتَهۡدِيٓ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Kuma kamar haka ne Muka yiwo maka wahayin Ruhi (watau Alqur’ani) daga umarninmu. Ba ka zamanto ka san mene ne littafi ko kuma imani ba, sai dai kuma Mun sanya shi (Alqur’ani) haske ne da Muke shiryar da wanda Muka ga dama daga bayinmu da shi. Lalle kuma kai tabbas kana shiryarwa zuwa ga tafarki madaidaici



Surah: Suratus Shura

Ayah : 53

صِرَٰطِ ٱللَّهِ ٱلَّذِي لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۗ أَلَآ إِلَى ٱللَّهِ تَصِيرُ ٱلۡأُمُورُ

(Watau) tafarkin Allah wanda Yake da mulkin abin da yake cikin sammai da abin da yake qasa. Ku saurara, zuwa ga Allah ne kawai al’amura suke komawa