Surah: Suratul Qalam

Ayah : 1

نٓۚ وَٱلۡقَلَمِ وَمَا يَسۡطُرُونَ

NUN[1]. (Allah ya ce): Na rantse da alqalami da abin da (mala’iku) suke rubutawa


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Surah: Suratul Qalam

Ayah : 2

مَآ أَنتَ بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ بِمَجۡنُونٖ

Kai ba mahaukaci ba ne saboda ni’imar Ubangijinka



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 3

وَإِنَّ لَكَ لَأَجۡرًا غَيۡرَ مَمۡنُونٖ

Kuma lalle tabbas kana da lada marar yankewa



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 4

وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٖ

Lalle kuma kai kana kan halaye masu girma



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 5

فَسَتُبۡصِرُ وَيُبۡصِرُونَ

To ba da daxewa ba za ka gani, su ma kuma su gani



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 6

بِأَييِّكُمُ ٱلۡمَفۡتُونُ

Wane ne daga cikinku mahaukaci?



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 7

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ

Lalle Ubangijinka Shi Ya fi sanin wanda ya kauce wa hanyarsa kuma Shi Ya fi sanin shiryayyu



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 8

فَلَا تُطِعِ ٱلۡمُكَذِّبِينَ

Saboda haka kada ka bi masu qaryatawa



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 9

وَدُّواْ لَوۡ تُدۡهِنُ فَيُدۡهِنُونَ

Sun yi burin da za ka sassauto, sai su ma su sassauto[1]


1- Watau ya daina aibata gumakansu da bautarsu, sai su ma su daina sukan sa da addininsa.


Surah: Suratul Qalam

Ayah : 10

وَلَا تُطِعۡ كُلَّ حَلَّافٖ مَّهِينٍ

Kada kuma ka bi duk wani mai yawan rantsuwa, wulaqantacce



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 11

هَمَّازٖ مَّشَّآءِۭ بِنَمِيمٖ

Mai yawan yin zunxe, mai yawan yawo da annamimanci



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 12

مَّنَّاعٖ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ

Mai yawan hana alheri, mai ta’addanci, mai yawan savo



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 13

عُتُلِّۭ بَعۡدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ

Mai busasshiyar zuciya, bayan wannan kuma marar asali ne



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 14

أَن كَانَ ذَا مَالٖ وَبَنِينَ

Don ya kasance mai dukiya da ‘ya’ya



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 15

إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Idan ana karanta masa ayoyinmu sai ya ce: “Tatsuniyoyin mutanen farko ne.”



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 16

سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلۡخُرۡطُومِ

Ba da daxewa ba za Mu yi masa alama a kan hancinsa



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 17

إِنَّا بَلَوۡنَٰهُمۡ كَمَا بَلَوۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡجَنَّةِ إِذۡ أَقۡسَمُواْ لَيَصۡرِمُنَّهَا مُصۡبِحِينَ

Lalle Mu Mun jarrabe su (wato mutanen Makka) kamar yadda Muka jarrabi ma’abota gona, lokacin da suka rantse cewa, lalle tabbas za su girbe ta da asussuba



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 18

وَلَا يَسۡتَثۡنُونَ

Ba sa kuma togaciya (da faxar insha Allah)



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 19

فَطَافَ عَلَيۡهَا طَآئِفٞ مِّن رَّبِّكَ وَهُمۡ نَآئِمُونَ

Sai wani bala’i daga Ubangijinka ya kewaye ta alhali su suna bacci



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 20

فَأَصۡبَحَتۡ كَٱلصَّرِيمِ

Sai ta wayi gari (baqi qirin) kamar duhun dare



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 21

فَتَنَادَوۡاْ مُصۡبِحِينَ

Sai suka kirawo junansu da asussuba



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 22

أَنِ ٱغۡدُواْ عَلَىٰ حَرۡثِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰرِمِينَ

Cewa: “Ku yi sammako ga amfanin gonarku idan kun kasance masu yin girbi.”



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 23

فَٱنطَلَقُواْ وَهُمۡ يَتَخَٰفَتُونَ

Sai suka tafi alhali suna yi wa junansu raxa



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 24

أَن لَّا يَدۡخُلَنَّهَا ٱلۡيَوۡمَ عَلَيۡكُم مِّسۡكِينٞ

Cewa: “Lalle a yau kada wani miskini ya shigar muku cikinta.”



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 25

وَغَدَوۡاْ عَلَىٰ حَرۡدٖ قَٰدِرِينَ

Suka kuwa yi sammako suna masu zaton su masu iko ne a kan hana (mabuqata)



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 26

فَلَمَّا رَأَوۡهَا قَالُوٓاْ إِنَّا لَضَآلُّونَ

To lokacin da suka gan ta sai suka ce: “Lalle mu tabbas mun yi vatan kai



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 27

بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ

“A’a, mu dai an hana mu ne kawai.”



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 28

قَالَ أَوۡسَطُهُمۡ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ لَوۡلَا تُسَبِّحُونَ

Sai wanda ya fi su kirki ya ce: “Ban gaya muku ya kamata ku tsarkake Allah ba?”



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 29

قَالُواْ سُبۡحَٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ

Suka ce, “Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu, lalle mu mun kasance azzalumai.”



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 30

فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَلَٰوَمُونَ

Sai sashinsu ya fuskanci sashi suna zargin juna