Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 1

إِذَا وَقَعَتِ ٱلۡوَاقِعَةُ

Idan mai afkowa ta afku (watau alqiyama)



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 2

لَيۡسَ لِوَقۡعَتِهَا كَاذِبَةٌ

Babu wani (rai) mai qaryata aukuwarta



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 3

خَافِضَةٞ رَّافِعَةٌ

Mai qasqantarwa ce mai xaukakawa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 4

إِذَا رُجَّتِ ٱلۡأَرۡضُ رَجّٗا

Idan aka girgiza qasa girgizawa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 5

وَبُسَّتِ ٱلۡجِبَالُ بَسّٗا

Aka kuma dandaqe duwatsu dandaqewa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 6

فَكَانَتۡ هَبَآءٗ مُّنۢبَثّٗا

Suka zama qura abar sheqewa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 7

وَكُنتُمۡ أَزۡوَٰجٗا ثَلَٰثَةٗ

Kuka kuma kasance dangogi guda uku



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 8

فَأَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ مَآ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ

To ma’abota dama fa, mamakin darajar ma’abota dama!



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 9

وَأَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ مَآ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ

Da kuma ma’abota hagu, mamakin wulaqantar ma’abota hagu!



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 10

وَٱلسَّـٰبِقُونَ ٱلسَّـٰبِقُونَ

Da kuma masu rige-rige (zuwa alheri)



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 11

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلۡمُقَرَّبُونَ

Waxannan su ne makusanta



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 12

فِي جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

A cikin gidajen Aljanna na ni’ima



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 13

ثُلَّةٞ مِّنَ ٱلۡأَوَّلِينَ

Su jama’a ne (masu yawa) daga (al’ummun) farko



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 14

وَقَلِيلٞ مِّنَ ٱلۡأٓخِرِينَ

Kuma kaxan ne daga (al’ummun) qarshe



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 15

عَلَىٰ سُرُرٖ مَّوۡضُونَةٖ

Suna kan gadaje masu adon zinari



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 16

مُّتَّكِـِٔينَ عَلَيۡهَا مُتَقَٰبِلِينَ

Suna kishingixe a kansu suna fuskantar juna



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 17

يَطُوفُ عَلَيۡهِمۡ وِلۡدَٰنٞ مُّخَلَّدُونَ

Yara samari dawwamammu (masu hidima) za su riqa zagaya su



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 18

بِأَكۡوَابٖ وَأَبَارِيقَ وَكَأۡسٖ مِّن مَّعِينٖ

Da kofuna (marasa mariqai) da butoci masu hannaye da kuma qoquna na giya



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 19

لَّا يُصَدَّعُونَ عَنۡهَا وَلَا يُنزِفُونَ

Ba sa ciwon kai saboda ita, kuma ba sa buguwa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 20

وَفَٰكِهَةٖ مِّمَّا يَتَخَيَّرُونَ

Da kuma ababan marmari na abin da suke so su zava



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 21

وَلَحۡمِ طَيۡرٖ مِّمَّا يَشۡتَهُونَ

Da kuma naman tsuntsaye na abin da suke sha’awa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 22

وَحُورٌ عِينٞ

Da kuma matan Hurul-Ini



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 23

كَأَمۡثَٰلِ ٱللُّؤۡلُوِٕ ٱلۡمَكۡنُونِ

Kamar misalin lu’ulu’u da yake cikin kwasfa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 24

جَزَآءَۢ بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Sakamako ne na abin da suka kasance suna aikatawa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 25

لَا يَسۡمَعُونَ فِيهَا لَغۡوٗا وَلَا تَأۡثِيمًا

Ba sa kuma jin wani zancen banza da mai sa zunubi a cikinta



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 26

إِلَّا قِيلٗا سَلَٰمٗا سَلَٰمٗا

Sai dai faxar salamun-salamun[1]


1- Watau sallamar mala’iku a gare su da wadda za su riqa yi wa junansu.


Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 27

وَأَصۡحَٰبُ ٱلۡيَمِينِ مَآ أَصۡحَٰبُ ٱلۡيَمِينِ

Ma’abota hannun dama kuwa, mamakin darajar ma’abota hannun dama!



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 28

فِي سِدۡرٖ مَّخۡضُودٖ

Suna cikin ‘ya’yan itacen magarya marasa qaya



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 29

وَطَلۡحٖ مَّنضُودٖ

Da kuma ayaba mai ‘ya’ya dava-dava



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 30

وَظِلّٖ مَّمۡدُودٖ

Da inuwa madawwamiya